Showing 54001 words to 57000 words out of 114708 words

Chapter 19 - TUBALI book 2 complete hausa novel

18 Sep 2024

19365

ne, saboda basu tab’a tunanin wani
Daga cikin Doctors din zai k’ware da sauri akan abun har haka ba, musamman ma shi da yake d’an Nigeria, basu tab’a tunanin shi zaiyyi wining ba.

Domin faruwar hakan alamace dake, nuna musu babban nasararsa, shine kuma zai karb’i award na ban girma, tare kuma da certificate din da zai nunawa duniya, cewar shi babban likita ne, amintacce kuma yardajje akowacce k’asa.

Tabbas Rayyern yaji dadin hakan azuciyarsa, domin ko babu komai zai kankaro mutumcin k’asar sa.

Alhamdulillah Sauran
Patients dinma, da akayiwa operations din sun bud’e idanunsu, cikin sa’a kuwa kowanne da hayyacinsa ya dawo hakama nasu Dr Sadiq da sukayi gwajin su kan ƙananun dabbobi suma na Dr Sadiq ya tashi lfy bisa alamu gaba zai taka matakin da Rayyern ya taka a yau.

Sosai Doctors din sukayi kokari, harma way’anda suka gwada nasu akan mutum mutumi.


3:00 pm Dai-dai suka kammala, duk wani abunda zasuyi, Ganin garin nata k’ara gumewa da snow ne kuma, yasa duk suka watse, kaitsaye Rayyern ya nufo gida.

Saidai kuma kafun ya k’araso saida ya tsaya, amasallaci yayi Sallan La’asar, kana ya biya Halal restaurant yayi musu takeaway, na Arab dishes kafun ya nufo gidan kaitsaye.


Gaba d’aya yau din jin zuciyarsa yake wasai, badon komai ba kuwa saidan wannan nasarar daya samu.

Shigowa cikin falon yayi, tare da neman waje ya zauna, bayan ya zare jacket din dake jikinsa, kasancewar duk ta b’aci da dusan k’ank’ara dake dan sauka.

Kallon d’an table din dake cikin falon yayi, rashin Ganin ledodin daya bari awajen ne kuma, yasa shi gane cewar Jannart din ta fito, domin ta hakanne kawai yake gane fitowarta, ko rashin fitowarta, kasancewar Idan ta fito takan kwashe ledodin takai kitchine.

Ledan daya shigo dashi din, ya d’auko tare da d’aukan chicken kebab ya soma ci, bai wani ci sosai ba ya ajiye, sai kuma pizza da drinks din daya d’ansha.

Bayan ya kammala ne kuma kaitsaye ya wuce bedroom d’insa, saboda yana so ya d’an watsa ruwa.

Koda ya shiga bedroom din kayan jikinsa ya rage, tare da fad’awa bedroom ya sakarwa kansa ruwa.

Bayan ya fito awankanne kuma ya shirya, kansa cikin wasu Sabin riga da wando, tare da d’aura wata jibgegiyar rigar sanyi akai.

Still kuma car key d’insa ya d’auka, direct ya fice daga Cikin gidan.

Daga gidannasa kuwa kaitsaye wani babban shagon saida kaya ya nufa.
Mall Yevropeyskiy ya wuce kai tsaye dan yafi kusa da inda yake.
kayan sawa da kuma sweaters Chocolate's
masu yawan gaske ya saya.

Har ya juya zai tafi ne kuma, idanunsa suka sauk’a akan wasu, womenswears masu azabar kyau, wanda dukansu kaya ne da zasu tare sanyi.
Domin irin jibga jingan rigunan nanne da y’an k’asar suke sawa.

K’arasawa wajen clothes din yayi, tare kuma dasa hannunsa ya zaro wasu manyan jacket masu kyau, guda biyu ya ciro jacket din, sai kuma wasu wanduna masu kyau, way’anda ya ibosu sama da guda biyar haka nan yake kallonsu yana murmushin, a hankali ya lumshe idanunsa da alamun yana so tuno wani abune.

Zuba su yayi acikin basket din dake hannunsa, kaitsaye kuma ya nufi wajen biyan kudi.

Koda akayi masa bill bai damu da yawan kudin ba, haka ya mik’a musu atm card d’insa suka cire.

Daga mall din kuwa, kaitsaye wajen sport ya nufa, saboda yana son dan motsa kafafunsa.

Acan gida kuwa Jannart tunda ta k’ule d’aki bata sake fitowa ba, ko da kwanciyar ma ya isheta bacci ne ya d’auketa, ba ita ta tashi ba kuwa sai dab Sallan Magriba, bayan tayi Sallah ne kuma, ta d’auko wani book dinta, ta soma karantawa.

Tana nan azaune har aka kira Sallah’n Isha, tana idar da Sallan kuwa ta haye kan gado, saboda sanyin garin ya sake yawaita.


Rayyern kuwa tunda ya fita bai dawo ba sai yanzun.

Ahankali ya bud’e murfin motar ya fito, tare da Kwaso manya manyan ledodin kayan daya saya, kaitsaye ya nufi cikin gidan.

Yana shiga cikin falon kuwa, idanunsa suka sauk’a akan, ledan abincin daya sayo d’azun, babu alaman an tab’asa.

Kauda kansa gefe yayi, for the first time kuma kenan daya d’aga, idanunsa ya kalli kofar dakin nata haka nan yaji kamar ba dadi.

Bakinsa ya d’an tab’e kana kaitsaye ya wuce dakinsa.

Yana shiga ya dire ledodin dake hannunsa, tare da wucewa toilet yayi wanka, bayan ya fito ne kuma ya shirya kansa, cikin wasu kayan bacci masu nauyi.

Hayewa saman gadonsa yayi, tare da kunna laptop d’insa, ya soma receiving sakonnin da ake turo masa, kaitsaye sakon maganer’n Companynsa ya fara dubawa, inda yake shaida masa yanda abubuwan companyn suke tafiya, da kuma yanda manyan y’an kasuwa, ke zuba hannun jari acikin companyn, komai dai yana tafiya normal.

Domin Koda ya duba details na companyn, ya ga abun na tafiya akan dai-dai.

Iya sakon da yasan suna da muhimmanci yayi replying, sauran sak’onnin kuwa ko duba su, baiyi ba ya kashe laptop din nasa.

Idanunsa ya d’an lumshe, dai-dai lokacin kuwa wayarsa dake gefe ta soma k’ara.

Ganin sunan Ramadan na yawo akan screen, din wayar ne kuma ya sashi d’agawa, tare da kara wayar akan kunnensa.

“Good Evening Hamma Rayyern, I hope you’re okay.”

Daga can b’angaren Ramadan din ya tambaya.

Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da gyara kwanciyarsa, Cikin kulawa yace.

“I’m Okay Ramadan, you? Ina Mamy da Abba?”

Murmushi Ramadan yayi tare da cewa.

“Same to you Hamma, Mamy da Abba kuma suna lafiya, Ina Aunty Jannart?”

Idanunsa ya d’an lumshe, kana cikin yin kasa da murya yace.

“Tayi bacci.”

Kai Ramadan ya jinjina, Jin kamar Hamman nasa agajiye yake ne kuma, yasa shi danne dariyarsa, domin shi wani tunani na daban zuciyarsa ta basa.

“Okay Hamma gud night, but please ka gaishemin da Aunty Jannart Idan ta tashi.”

“To.”
Rayyern din ya fad’a agajarce, domin bayason Ramadan ya sake yi masa wata tambayar, daga haka sukayi sallama.

Ahankali ya zare wayar daga kan kunnensa, tare da mik’ewa tsaye, ya k’arasa gaban fridge din dake cikin dakin.
Koda ya bud’e fridge din dan siririn tsaki yaja, saboda ganin da yayi babu ruwa aciki.
Gashi kuma yana buk’atar ruwa, saboda tunowa da yayi baisha maganinsa ba.

Kaitsaye ya nufi kofar fita daga cikin d’akin.

Dai-dai lokacin kuwa Jannart, da fitowarta daga, d’akinta kenan ta nufi kitchine, saboda Itama ruwan take da buk’ata.

Saidai kuma ganin duhu da tayi afalonne yasa ta, d’an tsayawa tare da soma laluben inda makunnin wutan falon yake.

Dai-dai lokacin kuwa Rayyern din ya fito, ko kad’an kuwa duhun bai tsorata shi ba, kasancewar yasan kan gidan shiyasa, baya wani buk’atar haske kaitsaye, ya nufi kitchine din.

Dai-dai ya kawo tsakiyar falon ne kuma, itama Jannart din ta iso wajen, wanda Jin motsin mutum da tayi, ya saka duk ta tsorita, juyowan da zatayi ne kuma sukayi karo, inda take kafad’ansa ya bugi hab’arta.

Wani irin k’ara ta saka tare da saurin, sanya hannayenta ta kama hab’ar nata.

Rayyern kuwa d’an ware idanunsa yayi, saboda bai tab’a kawowa aransa cewar tana cikin falon ba.
Jin yanda tayi k’ara ne kuma yasa shi, matsawa cikin sauri ya kunna, wani dan blue din hasken wuta dake cikin falon.

Idanunsa ya sauk’e akanta, wanda har yanzu tana rik’e da hab’ar nata, ta kuma rumtse Idanunta, da alama ya bugeta sosai.

Ahankali ya soma k’arewa shigar dake jikinta kallo, wata doguwar riga ce mai kauri, sai kuma hulan sanyin dake kanta, Yayinda dogon gashin kanta ya sauk’o kan kafad’unta.

Duk da cewar hasken daya kunna din, bayi da karfi sosai, amma hakan bai hanashi kallon yanda fuskarta, tayi fayau ba, ga kuma shatin nipples dinta da suka bayyana, kasancewar gaban rigar nata akwai tsagu ne, kuma yasa yake iya ganin tsakiyan kirjinta, ma’ana tsakiyan breast dinta.

Idanunsa ya mayar kan fuskarta, tare da soma takowa ahankali ya shiga matsowa inda take.

Dai-dai yazo kusa da ita ne kuma ya tsaya cak, kyawawan hannayenta ya kalla, akaron farko a iya tsawon rayuwarsu, ya sake matsowa kusa da ita sosai, har hakan ya bawa hucin nufashinsa dama sauk’a akan kirjinta.

“Meye?”

Ya fad’a da wata irin husky voice, din dake bayyana baccin da yakeji.

Jannart kuwa dake tsaye, Jin muryarsa da tayi akusa da ita ne, yasa ta saurin bud’e Idanunta da suka cika da k’walla, ta sauk’esu akansa.

Shek’in ruwan hawayen da idanun nata keyi ne, ya sashi jefa nasa idanun acikin nata, still cikin wata irin muryar daya kusan sata rud’ewa yace.

“Meye? Kinada damuwa ne? Me kikeso, uhummmm tell meeee.”
Yaja ƙarshen mgnar cikin kasalalliyar murya a tausashe
Hawayen dake cikin idanun nata ne suka gangaro, lokaci d’aya kuma tayi k’asa da kanta, tare da had’e yatsun hannunta waje d’aya.

Shi kuwa Rayyern a hankali ya m...!






By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:49 - 🥰🥰: “Naan please ka bud’e idanunka, Dan Allah kayi numfashi!!”

Ta kare maganan cikin matsanancin kukan, dake bayyana karyewar zuciyarta da rauninta.

Hakan da Dr. Sulaiman ya ganine kuma ya sashi, k’arasowa cikin falon da sauri, hankalinsa amatukar tashe yace.

“Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, please Jannart stop crying, kiyi min bayanin abunda yake damunshi.”

Jin muryar Dr. Sulaiman acikin kunnuwanta ne kuma, ya sata d’ago Kanta da sauri cikin shasshshek’an kuka, kana murya asark’e tace.

“Ka taimakamin Doctor, Dan Allah ina tsoron ya rasa rayuwarsa, numfashinsa tafiya yakeyi, tun d’azu cikinsa keyi masa ciwo, kuma bansamu maganin da zan basa ba.”

K’arasowa wajen nasu Dr Sulaiman yayi, cikin kuma tsananin yanayin damuwa yace.

“Calm down Jannart, Insha Allah Rayyern zai samu lafiya, ki daina kuka kinji.”

Ya k’are maganar yana me lalub’o waya daga aljihunsa.

Rayyern dake rungume acikin k’irjinta kuwa, har yanzu da sauran numfashinsa, sannan kuma ahankali zuciyarsa ke bugawa, wanda kuma hakan na tafiya ne, da taimakon bugun zuciyar Jannart din da yake iya jiyowa acikin kirjinsa, kasancewar k’irjinsa da nata suna manne awaje d’aya.

K’warai yana so ya bud’e idanunsa da suke lumshe, amma kuma bashi da k’warin guiwar yin hakan, saboda zuwa yanzu komai na jikinsa yayi sanyi.

Jannart kuwa ahankali tasa hannayenta, ta sake matsetshi acikin jikinta, still kuma hawayen dake kwance akan fuskarta na d’iga ajikinsa.
Duk ta rud’e Yayinda Idanunta sukayi ja sosai.

Dr. Sulaiman kuwa Ganin yanda take arud’en ne yasa shi d’an rank’wafowa, kana cikin kulawa yace.

“Ya kamata mu kaisa asibiti mafi kusa, domin bashi taimakon gaggawa, amma firstly yanzu sakeshi bari na fara sakashi a mota.”
Ya ƙare mgnar yana matsowa kusa dasu,
Sunkuyowa yayi da niyar janye Rayyern dake jikinta.

Dai-dai lokacin kuma Rayyern ɗin ya fara wani irin numfarfashin masu nauyi.

Saurin girgiza kanta tasoma yi, cikin tsoro da kuma fargaban abunda ka iya zuwa tace.

“A’a Doctor Idan na sakeshi suma zaiyi fa.
Kalli yadda numfashinsa keyifa zai d’auke gaba d’aya, Ina jin tsoro ni dai bazan iya sakeshi awannan yanayin ba, Dan Allah kakira mana Dr yazo ya duba shi.”

Ta kai k’arshen maganan nata tana me, sake rungume Rayyern din acikin jikinta, Yayinda hawayen dake kwance akan fuskarta kuwa ke ci gaba da tsiyaya, tamkar ankunna famfo.

Baki Dr. Sulaiman din ya bud’e da niyar cewa wani abu, saidai kiran daya shigo cikin wayar tasa ne, yasa shi yin shiru tare da d’aukan wayan ya kara akan kunnensa.

Daga can b’angaren Ramadan jin Dr Sulaiman din ya d’aga wayan, cikin tsananin tashin hankali yace.

“Please Dr ya ake ciki, ya jikin Hamma Rayyern din? Kun kaishi asibitin Ina fatan babu abunda ya sameshi?”

Ramadan yayi tambayan duk agigice.

Kai Dr Sulaiman din ya girgiza, kana cikin yanayin damuwa yace.
“Ramadan ya zanyi Jannart ta rik’e sa gam, ta yanda babu yanda zan iya d’aukarsa, saboda tace wai Idan ta sakeshi suma zaiyi, na rasa makama Ramadan Domin ciwon nasa ya tashi sosai awannan karon.”

“Innalillahi wa’inna Ilaihirraju’un, Dr Sulaiman kayi wani abu mana, kayi wani abu kada Hamma na ya rasa ransa, Dan Allah ko Doctor ne kaje ka kira a waje.”

Ramadan ya fadi haka cikin tashin hankali.

Kai Dr Sulaiman ya jinjina, tare kuma da kad’a kansa cikin gamsuwa yace.

“Okay Ramadan amma inajin tsoron tafiya nabarsu awannan yanayin, Rayyern yana gab da suma, gashi Jannart kuma sai kuka take kamar zata shid’e, gaba d’aya na kasa iya control dinsu dukansu biyu.”

“Yah Allah help us.”

Ramadan ya fad’a cikin muryarsa da tayi rauni sosai, cike kuma da tausayin d’an uwan nasa, ga kuma Jannart dake ta kuka, domin daga cikin wayar yana iya jiyo sautin kukan da takeyi.

Jannart dake rungume da Rayyern din kuwa, kwata kwata bama tasu Dr Sulaiman din takeyi ba, damuwarta shine taga Rayyern din ya bud’e idanunsa.

Ahankali ta dawo da kallonta garesa, tare dasa hannunta d’aya ta tallafo hab’arsa cikin kuka tace.

“Dan Allah Naan ka bud’e idanunka, kada ka daina numfashi, kada kuma ka cire rai da rayuwa in sha Allah, ai zaka samu sauki ko, nasan zaka warke zaka samu lafiya mu koma Nigeria lfy en Mamynka da Abbanka su ganka lfy, za kayi rayuwa kamar kowa muna bukatar ka a tsakiyar mu, dan Allah ka bud’e idanunka yanzu, ka dawo cikin hayyacinka Dan Allah...”

Ta k’are maganan cikin tsananin kuka da kuma raunin zuciya, ahankali kuma tasa hannunta akan kumatunsa tana d’an bubbugawa, cike dason taga ya bud’e idanunsa.

Idanu Dr Sulaiman ya zuba musu, lokaci daya kuma duk jikinsa yayi sanyi, musamman da yaga yanda Jannart din ke kuka sosai da sosai.

Maida wayar tasa cikin aljihu yayi, cikin sauri kuma ya d’auki key din motar Rayyern din, da ya gani akan table, tamkar wanda zai tashi sama saboda sauri, haka ya sa Kai ya fice daga cikin falon.

Kaitsaye wajen da motar Rayyern din yake ya nufa, yana shiga kuwa ya cilla motar kan titi, tare da nufar babban hospital din garin, wanda kuma shine mafi kusa dasu.

Jannart dake zaune kuwa duk da taji fitansa, amma bata d’ago Kanta ta kalleshi ba, Idanunta har yanzu suna kan fuskar Rayyern, still kuma ko wani d’igon hawayenta d’aya, da zai fita akan fuskarsa yake sauk’a.

Ahankali take yawo da hannunta dake kan hab’arsa, har ta k’araso zuwa kan kirjinsa.
Lallausan tafin hannunta ta kife akan kirjin nasa, dai-dai saitin zuciyarsa, Jin zuciyar tasa na d’an bugawa ahankali ne kuma ya sata, lumshe Idanunta tare da motsa labb’anta cikin sanyi tace.

“Ya Allah ka taimaki Naanu na Yah Allah ka bashi lafiya, kasanya juriya acikin rayuwarsa, Allah kagani bamu da kowa anan saikai, Kai ke kulawa damu akoda yaushe, Ya Allah yauma ka kula damu, ka saukaka mana tsanani izuwa sauki ya Allah ka rufa min asiri ka bawa Naanu na lfy.”

Takai karshen maganan hawaye yana me shatata akan fuskar nata.

Rayyern dake kwance ajikinta kuwa, duk wani abu da take fadi yana jinsu acikin kunnuwansa, saidai kuma yakanji kalaman nata da sautin amon muryar nata tamkar acikin mafarki, saboda gangar jikinsa ne kawai take wannan duniyar, hankalinsa kuwa ya tafi izuwa wata duniyar ta daban.

Suna ahakanne kuma k’iran Ramadan ya shigo cikin wayar Rayyern din dake gefe, Ganin sunan Ramadan ne kuma, yasa ta d’aga wayar da sauri tana k’arawa akan kunnenta, ta sake fashewa da kuka, still cikin muryar sheshshek’a tace.

“Ramadan har yanzu baidawo cikin hayyacinsa ba, na shiga uku Ramadan banason wani abu ya sameshi, duk jikinsa rawa yakeyi, gaba daya ya fita ahayyacinsa, Ramadan ya zanyi....”

Sautin kukan nata ne yasa Ramadan d’an rumtse idanunsa, zuciyarsa cike da damuwa, da kuma tashin hankali yace.

“Zai dawo Hayyacinsa Aunty Jannart, Insha Allah nan bada jimawa ba Hamma Rayyern zai dawo hayyacinsa, ki daina kuka dan Allah, ki kula dashi kafun Dr. Sulaiman ya dawo.”

Cikin kukan ta jinjina kai, saidai ta kasa cewa komai sai sheshshekanta da yake tashi.

Acan Nigeria din kuwa Mamy dake gefen Ramadan, itama hawaye takeyi gaba daya ta shiga cikin damuwa.

Haka ma Abba wanda ya zauna yayi ta gumi, abubuwa da yawa yake sak’awa acikin zuciyarsa, kallo daya kuma zakayi masa kafahimci cewa yana cikin matsananciyar damuwa.

Kasancewar kuma Ramadan din a hands free ya saka wayar ne, yasa dukansu suke iya jiyo kukan Jannart din, harma da nishin Rayyern dake tashi k’asa k’asa.

Ahankali Abban ya d’ago ya kalli Ramadan, da hannu Yayi masa alama akan ya bashi wayar.

Ganin hakanne kuma yasa Ramadan mik’a masa, kara wayar Abban yayi akan kunnensa, cikin son b’oye damuwa da kuma tausasa murya yace.

“Jannart.”

Jannart dake zaune kuwa jin muryar Abban acikin wayanne yasa ta d’an zabura, cikin rawar murya tace.

“Abba Hamma! Hamma!! Abba jikinsa yana ta b’ari, ga numfashinsa ya kusa d’aukewa, ciwo yakeji sosai, Dan Allah Abba ka taimakeshi.”

Idanu Abban ya d’an lumshe saboda tsananin tausayin yarinyar da yaji, domin ayanzu kukan ta yafi komai d’aga musu hankali sabida yanaga tashin hankali da take ciki zai hanata yin abinda ya dace.

“Jannart, Jannart!!”

Abban ya kira sunanta ahankali.

Yanda taji sautin muryar Abban ne kuma yasa ta, d’an tsagaita kukan nata tare da amsawa.

“Kiyi shiru kinji ki kwantar da hankalinki, ki daina wannan kukan In sha Allah Rayyern zai samu lafiya, ki daina kuka ki zama mai juriya akan ciwon sa kinji ko Jannart, yanzu addu’a ya kamata ki masa, ki daina kuka domin yawan kuka zai iya jawo miki wata matsalar kema, saboda haka ki share hawayenki Allah nanan kuma zai Iyar muku.”

Abban ya fad’i haka cikin son bata k’arfin guiwa.

Jin hakanne kuma yasa ta sanya hannu ta share hawayenta, cikin nuna biyayyarta agaresa tace.

“To Abba.”

Kai Abban ya jinjina cike da yabawa halin yarinyar, kana Ahankali ya zare wayar akunnensa ya kashe, saboda shi d’inma dazai samu dama, kukan zaiyi Domin har abada bazai tab’a son ace wani abu ya samu Rayyern din ba, haka kuma bazai so ace Rayyern yabar duniya batare da ya sauk’e wani k’aton nauyin dake wuyansa ba, Lallai zaiso ace Rayyern ya rayu, har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta.
Baya ga haka kuma Rayyern din shine komai nasu, shine AHALI’nsu kuma k’ashin bayansu.


Ahankali ta zare wayar daga kan kunnenta, tare da lumshe Idanunta tana mejin yanda Rayyern din ke sake shigewa cikin jikinta, Yayinda ya saka duka hannayensa biyu ya rungume cikinta gam.

Wanda hakan da yayi din kuma alamace dake, nuna cewar yanajin ciwo sosai.

Acan b’angaren Dr Sulaiman kuwa.
Koda yaje EUROUPEAN Medical senter mascow (E.M.S) din emergency Doctor ya nema, bayan ya shaidawa Doctorn matsalan Rayyern din ne kuma, suka nufo gidan kaitsaye.

Suna isowa kuwa ko gama dai-dai-ta parking ba suyi ba, direct suka nufi cikin gidan Dan bawa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login