Showing 183001 words to 186000 words out of 334042 words
Ummi tace "Toh wai ita kuma wannan karamar yarinyar da kake sa wa a baki kake comparing da matarka meye hadinka da ita ne, why don't u face ur life ka daina mentioning dinta a lamarin ka, did she have anything to do with u again xaka sa ta a bakin duniya" Ya kalli Ummi amma bai ce komai ba, Ummi tace "Ni ka tashi kaje ka same matarka ka bata hakuri ka dauketa ku tafi gida, Allah ya ci gaba da daidaita ku, ba ruwana da matsalar cikin gidanku, it's something u should have known before marrying her" Abuturrab yace "But how mum, kullum fa fes fes xaka ganta a titi, waye xai san xata yi haka?" Ummi tace "Allah ya kyauta" Ya kwanta saman gadonta yace "Ni sai na ci abinci Ummi, kuma ba yanxu xan tafi ba sai after isha, kullum fa sai nayi takeaway din abinci bata girki" Sharesa Ummi tayi ta mike ta nufi kofa ta fita, Aisha ce ta kawo masa abinci dakin, tana ajiyewa ta juya ta fita, shi kam ko kallonta bai yi ba, can ya mike ya sauka kasa ya dau plate ya fara dibar abincin. Aunty ce tsaye bedroom dinta tare da Aneesah dake xaune gefen gado tana kallonta, bata dade da dawowa gidan ba tun fitar da tayi bayan Hajja ta tarwatsa meeting din daxu, Aunty ta xuge jakarta bayan ta dau abinda xata dauka a ciki sannan ta dawo kusa da Aneesah ta xauna ta ajiye mata kwalaban turarruka uku a gabanta tace "kinga wannan, sai bayan mun koma asibiti ko xuwa gobe sun kara tabbatar maki babu wata matsala sannan bayan kin koma gida sai kiyi amfani da su" Aneesah tace "Aa kawai gwara ayi sabon dinkin Aunty, ni ina ji a jikina ba dai dai nake ba" Da mamaki Aunty tace "Kamar yaya?" Aneesah tace "Ni dai kawai ayi hakan, ko nawa ne xan biya ai" Aunty ta tabe baki tace "Toh shkkn, amma wllh Aliyu yayi mugun raina maki wayo, sannan ni banga laifinsa ba kece babbar wawuyar da kika yarda wai yana da matsala, a gidan ubanwa yake da matsalar mutumin da har gidansa kin sha xuwa ki kwana? Ko ke duk xuwan da kike gidansa a Abuja kin ga alamar yana da matsala?" Aneesah ta tabe baki tace "Ban ta6a ganin haka ba wllh, kawai shi dai baxai yi intercourse ba sbda gudun sa6on Allah amma ba don bashi da lafiya ba ko wani abu, amma babu abinda baya min ai, ce min yayi of recent ya samu matsalar" Aunty tace "Wllh ni ban yarda da kanwar uwar nan tasa ba don ita ma waye bai san tana shige shige ba kilan taje ta hango aikinmu ne tasa aka lalata, shine yake ta maki hanya hanya..." Aneesah tace "Toh ai da kin tambaya inda kika je daxu" Aunty tace "Wllh na manta shaff ban tambayi mutumin ba, amma akwai wani da xan kira anjima a benue, xai sanar da ni komai, yanxu kuma sai ki kirgo dubu talatin na turaren nan ki bada" Aneesah tace "Ina na gansu Aunty, har yau fa nace maki kudin nan da kika ce in tambayesa sai min yawo da hankali yake, yace yau yace gobe" Aunty tace "Rabu da shi don ubansa, xa muyi maganinsa nan ba da dadewa ba, muna nan dake sai account dinsa ya dawo hannunki gaba daya" Kwankwasa kofar dakin aka yi, Aunty ta jawo pillow ta ture kananun kwalaban turaren a karkashi da sauri, Aka bude kofar Abuturrab ya shigo da sallama kansa a kasa, Hade rai Aunty tayi ta mike ta dau Hijab dinta ta saka ta shimfida darduma ta hau sallahn isha, Aneesah dai sai wani cika take tana batsewa tana danna waya, ya ja stool ya xauna ya fiddo nasa wayar yana dannawa, yana ta xaune har Aunty ta idar da sallah, sannan ya kalleta yace "Ina yini Aunty" a takaice Aunty tace "Lafiya lau, sai yanxu ka ga damar shigowa bayan ina ganin sanda ka shigo gidan tun kafin magrib?" Yana kallonta yace "Dakin Ummi nake ai" Aunty tace "Toh yayi kyau, ai da baka fito ba ka dauwama a can din" Shi dai bai ce mata komai ba, ta dau carbinta tana ja, bayan few seconds yace "Dama xuwa nayi in baku hakuri Aunty a kan abinda ya faru, ni bana nan lkcn da Aneesah suka samu matsala da Hajja, ban ma san me ya faru ba har yanxu, na kuma bata hakuri tun a daren jiyan amma taki saurarata tayi wucewarta" Aneesah ta katse sa a fusace tace "Wllh karya ne Aunty, da bakinsa ya umarce ni da in tafi" Kallonta Abuturrab ya dinga yi yace "Ni nake maki karya?" Tace "Toh tunda baka ji kunyar yin karyan ba nice xan ji kunyar karyata ka Aliyu" Aunty na kallon Abuturrab tace "Ni tambayar da xan fara yi maka a nan shine me wancan dabbar taje yi gidan ka tare da Hajja?" Da mamaki yace "Dabba kuma, ai Allah ma bai ce a siffanta mutum da dabba ba Aunty, dabba fa kika ce" Aunty tace "Ohh ni xaka ma wa'axi? To nace mata dabbar sai kayi yanda xaka yi yanxu, kanwar uwarka ce ita din ko ta ubanka?? Ko uban meye hadinka da ita xaka ce kar in kirata da dabba? Ka bani amsar tambayata uban me ya kaita gidanka Aliyu?" Cikin tsawa ta kare maganar, Ya sauke idonsa kasa yace "Nima ganinta kawai nayi tare da Hajja i don't know how" Aunty ta mike tana tafe hannu tace "Toh tayi xuwan farko tayi na karshe, duk ranan da kauyancinta da gidadancinta ya sake kadata ta bi wani ma ba Hajja ba xuwa gidanka dama nace tana shigowa Aneesah ta kirani, xan kuma dau makullin mota in fita inje gidan sai kuma nayi mata abinda har ta koma ga Allah baxata manta ba don ubanta, duk ranan da ta sake gigin xuwa gidan Aneesah wllh wllh sai na lahira ya fi ta jin dadi, sai na walakantata walakanci mafi muni, sai na mata toxarcin da har jikokinta sai ta ba labari wllh" Abuturrab kallon Aunty kawai yake ko kiftawa babu, can dai ya dauke kansa, Cikin bacin rai Aunty ta ci gaba tana cewa "Idan ba kwadayi da jakanci ba uban me xai sa tayi sha'awar komawa gidan da aka saketa ta fito, me xai kai ta?? To wllh ta kiyayeni bani da kyau, idan ta ci gaba da shiga gonata sai na sa ta bi duniya ni ba imani ne dani ba al-qur'an, su Ramlah yan iyayi da suka ga xa su iya riketa su ci gaba da riketa din, amma duk ranan da gidadancinta ya fada mata karya ya kaita gidanka to kuwa ranan xata yi da ta sanin haifota da matsiyatan iyayenta suka yi" mikewa Abuturrab yyi ya nufi kofa Aunty tace "Gidan ubanwa xaka ina magana Aliyu?? Aliyu ba da kai nake ba??" bude kofar yayi ya fice ya bar masu a bude ko kullewa bai yi ba, Aunty ta bi sa da kallo baki bude har ya fita kofar parlor gaba daya. Abuturrab na fita bangaren Ummi ya koma, Ummi na kallonsa tace "Kaje ka bata hakurin?" Kasa ce mata komai yayi saboda yanda xuciyarsa ke tafarfasa, Ummi ta lura da yanayinsa ta ci gaba da aikinta da take yi kawai, bayan kusan minti uku yace "Ummi ki kira Aneesah kice ta sameni a mota, idan kuwa bata fito ba xan yi wucewata" Ummi tace "Ka kira uwar dakin taka ka gaya mata mana, ba ita tafi kusa da Aneesar ba, sannan ina ce ma a bangarenta take" Abuturrab ya mike yace "Next weekend idan na dawo xan xo in dauketa in sha Allah, sai da safe" daga haka ya nufi kofa Ummi tace "Aliyu" tsayawa yayi, sai kuma ya juyo tace "Tell me what happened" Yace "Ummi kawai ni bana son abinda Aunty take yi ina raga mata ne kawai saboda Abba but idan ta ci gaba da shiga gonata i can go to d extent i am not suppose to, she is getting me pissed off" Ummi ta rike ha6a tana kallonsa da mamaki a ranta kuwa cewa tayi yau kuma?? Can ta d'an yi murmushi tace "Toh me ya hadaka da uwar dakin taka, dama ana jin kanku ashe" Abuturrab yace "She should just stay away from my personal life nd issues, that's all, xan jira a mota ki kira ki gaya masu idan kuma bata fito ba wucewata xanyi, sai da safe" Daga haka ya fice daga dakin Ummi ta bi sa da kallo, daukar wayarta tayi ta shiga kiran Aunty, Aunty na dagawa tace "Hafsah ki turo min Aneesah" Aunty ta wani kyabe baki tace "Aneesah kuma?" Ummi tayi shiru bata ce komai ba, Can Aunty tace "Toh dama sallah take bari ta idar" Ummi ta katse wayarta, sai bayan minti shidda Aneesah ta shigo parlon Ummi ta xauna saman kujera ta gaida Ummi, Ummi ta amsa tace "Ki je ki saka hijab dinki ki dau jakarki mijinki na jiranki a mota, sai kuma ayi ta hakuri, shi dama xaman aure d'an hakuri ne, kowa hakuri yake, ke kuma sai ki gyara duk abinda baya so, shima xai gyara in sha Allah, Hajja kuma ba lallai xaki sake ganinta a gidan ba ma, kiyi hakuri ki bi mijinki ku tafi kin ji" Aneesah tayi kasa da kanta, bayan wani d'an lokaci tace "Toh" sannan ta mike ta nufi kofa, Ummi ta bi ta da kallo har ta fita, tana komawa ta sanar ma Aunty yanda suka yi da Ummi tana tabe baki, Aunty ta ja wani dogon tsaki tace "Toh baxa ki je ba wllh, ita a wa xata tsomo baki cikin lamarin nan? Ina ruwanta! A cikin kayan miya wacece ita a lamarin Aliyu??" Aneesah dai sai ta6e baki take, can tace "Kinsan me Aunty tunda har kirana tayi ta min magana ki bari kawai inje kar ta saka ni a baki" Aunty tace "Ta saka 'ya yanta a baki dai ba ke ba wlh, kamar tana wani tabuka abun kirki a kan lamarin Aliyun da xata wani tsomo baki a wannan case din, ta ma ji da mugun abinda ke cinta kullum a xuciya mana da shiru shirun da take na algungumanci" Aneesah ta mike tace "Ko kayana ma baxan dauka ba Aunty xan dai tafi da turarrukan cikin hand bag" Aunty tace "Toh ya xancen xuwa asibitin gobe, ni fa dalilin da yasa nace baxa ki tafi yau din ba kenan" Aneesah tace "Sai in taho idan ya koma aiki gobe da safe, nasan da sassafe xai wuce kano ai, yawanci yanxu haka yake yi, ni bana son wancan matar tace nayi disrespecting dinta ne amma da sai in tsaya" Aunty ta ja tsaki ta xauna gefen gado tace "Dama goben ki xo da wuri, Kinga dai dai kenan kafin ya dawo wani weekend din anyi duk abinda xa ayi an wuce wajen" Aneesah ta saka hijab dinta ta xuba duk turarrukan a jaka sannan tayi ma Aunty sai da safe ta fita. Har suka isa gida Abuturrab bai ce ma Aneesah komai ba ita ma haka, banda danna wayarta babu abinda take, ta sauka motar ta bi bayansa xuwa cikin gidan, xaunawa parlor yyi yana kara regretting furnitures da aka xuba ma Aneesah a bangarensa, ko kallonsa bata yi ba ta haye sama ta wuce bangaren nasa, kwafa yyi ya mike ya haura sama ya bude dakin da su Hajja suka sauka ya shiga ciki, tsaf Hajja ta gyara dakin kafin su fita neman jiddah daxu da safe, don cewa tayi babu inda xata tafi bata gyara dakin ba haka kawai ta shiga hakkin tsafta, har bandaki sai da ta wanke, banda kamshi kuma babu abinda dakin yake, cire kayansa yayi ya shiga bandaki dake cikin dakin, bayan yayi wanka ya jima xaune dakin kafin ya sauka downstairs ya shiga kitchen, har sannan kitchen din fess tun gyaran da Jiddah tayi masa, ya dinga bin kitchen din da kallo kafin ya dau mug ya tafasa ruwan xafi ya hada shayi ya fito, a parlor ya sha shayin, yana ta xaune har kusan sha daya kafin ya mike ya wuce sama, babu yanda ya iya ya nufi bangarensa don daukar jallabiyarsa, Aneesah ce durkushe dakin hannunta rike da karamin towel tana goge turarrukan da suka fashe da sauri, har wani rawa hannunta yake, jakarta ta dauka xata ciro charger bata san a bude yake ba duk kayan ciki suka jirkice ciki har da turarrukan da aunty ta bata daxu wanda nan take biyu suka fashe wani kamshi ya gauraye dakin, tana ganinsa ta mike da sauri ta wuce bandaki da towel din, ya bi ta da kallo....
Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via
3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you
Makulli Aneesah ta sa a kofar bandakin bayan ta shiga gabanta na faduwa, ta ajiye towel din a karamin bucket ta tara ruwa ta dau sabulu ta fara wanke hannunta ba ji ba gani... Karasawa Abuturrab yyi yana jan kafa ya xauna gefen gado, har bayan minti sha biyar Aneesah bata fito daga toilet din ba, mikewa yyi ya dau jallabiyarsa ya fita dakin, sai da Aneesah ta tabbatar hannunta baya kamshin turaren sannan ta bude kofar bayin a hankali tana leko dakin, ganin baya nan ta sauke wani ajiyar xuciya ta fito, dama kayan bacci ne jikinta ta dau wayarta tayi plugging sannan ta kashe wutan dakin tayi kwanciyarta.... Har karfe daya saura Abuturrab bai yi bacci ba yana dai kwance da abinda ya damesa, idan ya juya ta daya side din gadon sae ya sake komawa daya side din, lkci daya ya mike xaune ya dafe kansa, sae kuma ya sauka saman gadon ya bude kofa ya fita ya sauka downstairs ya wuce kitchen ya jona ruwa a kettle, yana ta tsaye yana kallon kettle din sae kawai ya kashe socket din ya wuce sama, bangarensa ya nufa bayan ya shiga parlon ya karasa ya bude bedroom dinsa, hannu ya kai jikin bango ya kunna switch din dakin, bacci take hankali kwance ya kashe switch din ya karasa gun gadon ya hau, cikin bacci Aneesah taji kamar hannu a jikinta ta bude ido a hankali, lkci daya ta mike tace "Meye haka Captain?" Xaro ido tayi tana kokarin turasa ganin abinda yake shirin yi tace "Wai meye ne Captain, what is this u are doing" Rungumeta yayi jikinsa underneath his breathe yace "I need you today...." Sosai gabanta ya fadi ta fara turasa da duk karfinta tana cewa "You need me when i am on my period Captain?" Gani tayi kamar yana son confirming din abinda ta fada, bata san lkcn da ta fashe masa da kuka ba tana turjewa tace "Don Allah ka bari captain, meye xaka wani taho min kamar wata akuya bayan ni ban...." Bai bata privilege din ci gaba da magana ba, da farko gani take kamar xata iya kwatar kanta gunsa amma ya gwada mata ba karfinsu daya ba, hakan yasa ta fara masa magiya tana basa hakuri hankali tashe tana ce masa she is not in d mood amma kamar bai ma jin abinda take cewa, Aneesah bata ta6a shiga tashin hankali da firgicin da ta shiga a lkcn ba, banda rawa babu abinda jikinta yake tana hadasa da Allah ya bari, cikin not less than 10 mins komai ya faru... Tunda ya koma gefenta take satan kallonsa tana shessheka tana kukan tsoro, ga xuciyarta da take ji kamar xai fado don bugawa, gashi ita ba ganin fuskarsa take ba balle taga expression dinsa, Ita dai har ta gaji da satan kallonsa tana kuka ganin kamar ma bacci yake don ko motsawa bai yi ba balle ya kalli inda take, ta lallaba ta matsa kusa da shi xata ta6asa, sauka taga yayi daga saman gadon tun kan ta ta6asa ya nufi kofa, ta bi sa da kallo gabanta na ci gaba da bugawa sai da ya fita ta fashe da kukan gaske na tashin hankali... Abuturrab na komawa dakin da ya fito ya sa makulli ya shiga bandaki da sauri jin cikinsa ya hautsine.... Har kusan asuba Abuturrab bai yi bacci ba duk da sallah da ya dau lkci yana yi, after subhi prayer yana xaune parlor deeply in thought, sai kuma ya dau wayarsa yayi dialing number Ahmad, Ahmad ya shigo daki kenan dawowarsa daga masallaci ya nufi wayarsa da mamakin wanda ke kiransa by this time, ganin Abuturrab ne ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren Abuturrab yace "Good morning" Ahmad yace "Morning..." Abuturrab ya d'an shafa kansa yace "Dama ina son maka tambaya ne" Ahmad yace "Alright i am all ears" Abuturrab yace "I want to know more about Virginity, what it is, and how it is" Buda ido Ahmad yayi sosai yace "Tohhh" sai kuma ya kalli Ramlah dake xaune saman darduma, kofa ya nufa yace "Ban gane tambayar ka ba" Abuturrab yace "Meye baka gane ba a ciki?" Ahmad na fitowa parlor ya nemi kujera ya xauna, Abuturrab yace "I'm serious Ahmad, ka bani amsar tambayata don Allah" Ahmad yace "No ina mamakin hadin Pilot da tambayar ne... But anyway virginity da Hausa shi ake ce ma budurci, kuma idan aka ce Virgin ana nufin wanda bai ta6a intercourse ba, weather a male or a female..." Abuturrab yace "To ya ake gane someone that is a virgin?" Ahmad yace "Mace ko namiji?" Abuturrab yace "Both" Murmushi Ahmad yyi yace "Ita mace akwai wani thin membrane lining da ake kira da hymen a jikinta, and it will seem a bit difficult to penetrate in her, don dole sai anyi breaking hymen din, and in some cases they will be shedding of a little blood, mind u in some cases nace, wasu matan kuma ba sai ta hanyar intercourse kadai hymen dinsu ke breaking ba, d'aga abu me karfi, tsalle tsalle, hawan bishiya ko keke, and many stuffs like that, yana sa suyi loosing hymen dinsu, but duk da