Showing 42001 words to 45000 words out of 55849 words

Chapter 15 - Auren Shehu 2 Complete Hausa Novel

TAKORI   

01 Oct 2025

30

iya zama cikin su Halitta bare ta saki jiki da su.

Anty Sauda wacce ke zaune tare da Halitta da Ammy, ta girgiza kai bayan ta karewa Zainab kallo ta ce

"Wallahi wannan tsinannan almajirin ya cuce mu! Dan Allah ki ga yanda yayi breaking Zainab completely? Ji yanda Zainab ta koma, ji irin shigar da Zainab ta ke yi ta fita?"

Duka ukun kallan ta su ke yi, ita kuwa sam hankalin ta ba ya wajan su, tunanin sakamon gwajin da aka mata ta ke na game da juna biyu, duk da dai ita kan ta ba ta san wani irin sakamako ta ke fata ba, burin ta dai Allah ya tabbatar mata da abin da ya fi alkhairi.

Sanye ta ke cikin hijabi ruwan toka wanda ya sauka har kasa, sam babu wani alamar rawan kai da jin kai da aka san Zainab da shi. Hannu ta sa ta goge hawayen da ke gangarowa daga idanun ta, hakan ya sa Ammy dauke kai cike da jin zafin halin da diyar ta take ciki, ta na mai zargin kan ta da Malam da laifin sanya ta cikin duk wata masifa da ya afka mata.

Halitta da Anty Sauda ne su ka koma wajan ta, inda Halitta ta rungume ta cikin rarrashi, Anty Sauda kuwa fadi ta ke

"Ki dena kuka Yakura, wallahi sai an kwatar mi ki hakkin ki, na mi ki alkawarin kamo duk wanda ke da sa hunnu cikin wannan lamarin ko da kuwa wannan tsinannen almajirin ne! Ai ga irin ta nan! Na dage sai ya sake ki uwar ku ta ki goya mana baya, yanzu wa gari ya waya?"

Likita ce ta fito ta bukaci ganin Zainab ita kadai domin bata sakamakon gwaje gwajen da aka mata, Anty Sauda ta ki yarda lelle sai dai a fadi sakamakon a gaban su, ai su ne su ka kawo ta, da abin na sirrin Zainab ne da ba za su kawo ta ba sai su ce ta yi tafiyar ta ita kadai.

Sai da Zainab ta ba da izini sannan likitar ta yarda su ma din su ka bi Zainab zuwa ofishin likitan, Halitta ce kadai ta zauna waje.
Zainab da Anty Sauda zaune kujerar da ke fuskantar teburin likita, in da Ammy ta sami kujera can gefe ta zauna. Da Ammy har Anty Sauda likita su zubawa ido cikin jaran tsammani. Cike da nutsuwa likita ta musu bayanin cewa duka kwaje kwajen Zainab negative results aka samu ma'ana ba ta dauke da wani cuta da ake tsoro, likita ta kare jawabin ta ta hanyar fadin

" Sai dai kuma sakamakon gwajin juna biyun da aka mata ne mabambamci, dan kuwa ya nuna ta na dauke da juna biyu...."

Wani irin shauki ne ya ziyarci zuciyar Zainab ta tsinci kan ta tana mai runtse idanu, yayinda ta ke jiyo maganganun Anty Sauda tamkar ruwan zafi, fadi ta ke

"Ko juna dari ne zubar da shi za a yi wallahi! A yi polishing tsinannen......"

Ammy kuwa kuka ta saka ta salati, cewa ta ke

"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Innalillahi wainnailaihi rajiun!"

Anty Sauda ta kara da

"Sai yanzu ki ke da bakin salati? Ai dama aka ce wanda be ji bari ba ya ji hoho, mu ka yi mu ka yi ki dakile auren nan ki ka min kunne uwar shegu! Ai ga irin ta nan! Kai idan har ba a kama min yaran nan ba ban isa Sauda ba! Likita mu na so a cire cikin nan da gaggawa....!"

"Babu wanda zai cire min ciki!"
Cewar Zainab a fusace. Hakan ya sa su Anty Sauda sakin baki su na kallan ta. Ba ta gushe ba ta kara da

"Cikin shege ake zubarwa ba na halas ba, dana dan halas ne kada wanda ya kara aibata min ciki bare ya tsinantar min da shi! Idan har wahalar hanya be zubar min da ciki ba, ban ga dalilin da zai sa wani mahaluki ya taba min shi ba!"

Ta na gama fadin haka ta tashi fuuuu ta fice ta bar Anty Sauda da salati da sallallami ta na tafa hannu. Fadi ta ke

"La'ilahaillahu muhammada rasulillahi! Hajja Aleesha wannan yarinya ba cikin hayyacin ta take ba! An riga an juyar da kan ta sai mun dage da addua!"
Ammy kuwa rasa ta cewa ta yi, dama dai in tsiwa ne kadan daga aikin Zainab, mamaki daya shi ne ikirarin da ta ke akan cikin ta,
"Allah dai ya sa ba cikin hayyacin na ta take ba...."

Ammy ta fada a sanyaye.

"There is no two ways about it! Ki ma dena raba dayan biyu ba cikin hayyacin ta take ba, sai an yi rokan Allah!"

Cewar Anty Sauda. Da haka su ka yiwa Likita sallama su ka tafi. Cikin mota su ka tadda Zainab zaune ta hada girar sama da na kasa. Babu wanda ya tanka ta sai bayan da su ka isa gida sannan Anty Sauda ta saka ta a gaba da tambaya. Zaune su ke a falo, sun zagaye Zainab kamar suna gudun za a iya sake sace ta
"Za ki gane wanda ya dauke ki? Wannan tsinannan almajirin ne ko?"

Zainab ta mu su banza. Anty Sauda ta kara da

"Yakura mun san abin da ciwo, matukar ba ki budi baki kin yi magana ba ta yaya za mu iya kwato mi ki hakkin ki daga zalincin da aka aikata mi ki? Ki fada mana ya aka yi ya sace ki, Kuma ina ya kai ki, ya sunan garin...?"

Zainab ta ki amsa ta. Cikin nuna gajiyawa Anty Sauda ta furta

"Ina ga sai dai sojojin nan su tambaye ta kila su ta fada mu su, in ba haka ba Hajja Aleesha sai mun tsaya tsayin daka akan Yakura! Wannan almajirin ya asirce ta ya kuma breaking din ta...."

"Ba zan yi magana da kowa ba!"

Zainab ya katse ta a fusace. Ba ta gushe ba ta kara da

"Kada ki kara kiran miji na da tsinannen almajirin! Usman miji na ne! Eh shi ya dauke ni saboda shi aka daura min! Da zai kai ni ya gusar min da hankali, Amma da ya tashi sallama ta da hankali na ya sallame ni, na roke shi ya sake gusar min da hankali na ko zuciya ta za ta dena min radadin barin sa, ya ki! Yanzu ya sa na dawo gida amma zuciya ta na can tare da shi, Kuma ku bar tunanin addua, cikin hankali na na ke, kuma Anty Sauda zan so ki sarara min dan kuwa maganganun ki kan miji na suna neman yin tsauri dayawa!"

Shiru ne ya biyo baya tamkar wanda ruwa ya cinye, inda kunyar yanda Zainab ta watsawa Anty Sauda kasa a Ido ya rufe Ammy, Anty Sauda kuwa ji ta yi tamkar kasa ta tsage ta shiga. Tashi Zainab ta yi ta shige ciki, bayan tafiyar ta Ammy ta nisa ta ce

"Tabbas Yakura ba ta cikin hayyacin ta, ya asirce ta yayi..."

"Hmmmm kin ga Hajja Aleesha matukar ba Yakura ce da kan ta ta zo ta same ni ta ce min ba cikin hayyacin ta take ba na yi hakuri, wallahi na cire hannuna a kan maganar ta, ke hatta General ma zan fada masa babu ruwan sa....."

"A yi haka Hajja Sauda? Ai hannun ka ba ya rube ka yanke ba ko?"

Anty Sauda na girgiza kai ta furta

"Ah ah Hajja, a dai yi mata addua, matukar ba ta canza ba toh tabbas ki cire rai akan ta kema, ki sa a ran ki babu Yakura. shikenan ya tsafe ta har abada"

"Innalillahi wainnailaihi rajiun!"

Cewar Ammy ta na mai sharar kwalla. Nan Anty Sauda ta barta, cike da bacin rai ta shige ciki tare da kiran mijin ta ta sheda masa halin da ake ciki.

*****

Bangaran Rugar Shehu kuwa, Muhamadu Bello ya tadda Usman tamkar mai makoki, cikin kankanin lokaci ya canza gaba daya. Zaune su ke karkashin bishiya in da Bello ya zo ya tadda shi bayan dawowar sa.

"Idan har ka na kaunar ta haka da ba ka bari ta tafi ba Shehu, domin kuwa Uwargida na kaunar ka ita ma, wallahi halin da ta ke ciki ya sanya na kasa barin ta har sai da na kai ta har Taraba, na bar ta a cikin wani hali"

Maimakon ya bashi amsa daidai da maganar sa, sai cewa yayi

"Ina nan a kan baka na na barin Rugar Shehu sati mai zuwa in Sha Allah, zan shiga uwa duniya kamar yanda na taba shiga a baya, Amma wannan karan hanyar neman cigaban Rugar nan ce zai fitar da ni"

Ya dan dakata kamar mai nazari. Muhamadu Bello ya nisa, kana ya ce

"Duk da ba haka aka so ba, Amma ka riga ka yanke hukunci ba tun yau ba. Ka ga Kado ba su da amana akan dukiya ko neman ta, akwai wani bafulatani dan uwan mu, Ibrahim Yerima Balla, dama mun saba cinikanyar shanu da shi, mutumin birne ne kwarai amma sai amana, ya kuma san darajar dan Adam. Nan Yola ya fiya zama duk da ya ce min ya na da gidaje a Kano da birnin tarayya, me zai hana idan ka tashi tafiya na hada ku?"

Bayan Usman yayi dan tuntuntuni ya furta
"Ka na gani zai iya saka ni hanya Bello? Ni fa yanzu tsoran bil'adama na ke"

" Mutum abin tsoro ne, Amma kada ka damu na shedi Ibrahim, ba ya cutarwa"

"Toh Alhamdulillah, zan shedawa su Kawu Iliya, sati mai zuwa sai mu tasarwa Yola, zan fara tafiya da shanu dari biyu mu gani, idan da bukata wasu nan gaba sai na yo aike"

Da wannan shawarar Usman ya bar Bello ya tinkari su Kawu Iliya. Dan kuwa shi ma ba zai iya jure zaman Rugar Shehu ba bayan tafiyar Zainab, komai na Rugar tuna masa da ita ya ke, sai ya zama tamkar zuciyar ta na ma zuciyar shi fatalwa. Ji ya ke kamar ya bi ta Kanon ko ya sami sauki, Amma taurin kai ya hana, shi ya sa ya yanke hukunci shiga duniya ko ya sami sauki.

******

Babu irin adduar da Ammy ba ta sa an yiwa Zainab ba, islamiyoyi da makarantur allo ta saka aka kai sadaka in da aka sa yara sauka da zikiri. Amma Zainab ko gizau, ta tsaya tsayin daka babu mai zubar mata da ciki.

Bayan sati guda da dawowar Zainab, da la'asar Zainab zaune bakin gadon ta dake tashin ta daga bacci kenan, kamar yanda ta saba ta yi mafarki da Usman, takaicin farkawar da ta yi ne ya sanya ta zaman bakin gado tare da doka uban tagumi.
A hankali aka kwankwasa mata kofa, sanin ba za ta amsa ba ya sa suka bude kofar su ka shigo, Ammy ce a gaba, biye da ita Anty Sauda ce da Halitta. Halitta ta zauna kusa da ita, in da Ammy da Anty Sauda ke tsaye suna duban ta. Cike da damuwa Ammy ta furta

"Yakura wannan tunanin da bakin cikin da ki ke ciki zai iya lahanta ki da dan cikin na ki, me zai hana ki bi Antyn ki ku koma Maiduguri, can zai fi mi ki kwanciyar hankali kafin ki samu ki koma makaranta....."

"Babu in da zani, ba kuma zan sake komawa makarantar ba, Nan zan zauna abu na har sai na haihu, idan kuma zaman nawa na damun ki Ammy sai na sami ko da gidan haya ne....."


"Ah ah Yakura"

Ammy ta yi saurin katse ta. Ta kara da

"Nan din ai gidan uban ku ne, ku ne magada dan ko da aka raba gadon Malam gidan a naku ya fado ina kuma batun neman haya? Kuma ina ki ka taba Jin zaman diya a gida ya dami uwar ta, dama farin cikin ki shi ne fatan mu...."

"Usman shi ne farin ciki na Ammy, rashin shi shi ne sanadin bakin ciki na, idan har kuna so ku sake ganin walwala ta a duniya ku barmin ciki na na haife shi, ban da makiyin da ya wuce wanda zai yi yunkurin raba ni da ciki na, wannan cikin shi ne rayuwa ta....."

Dan takaici Anty Sauda kasa magana ta yi ta juya ta fice fuuu tamkar za ta tashi sama. Ammy na mai dafa kafadar Zainab ta furta

"Na mi ki alkawari Yakura babu wanda zai sake cewa ki zubda cikin nan, Allah ya raba lafiya"

Ta fice jiki a sanyaye. Ya rage da Halitta sai Zainab cikin dakin. Shiru su ka yi kowannan su na sakar zuci, daga bisani Halitta ta furta

"Yakura?"

Halitta ta kira sunan ta a hankali. Zainab ta daga ido ta kalle ta. Karo na farko da su ka zauna tare cikin aminci ba tare da Zainab na neman ta da bakar magana ba. Halitta ta murmusa ta ce

"Kada ki damu, ina goyan bayan ki dari bisa dari"

"Na gode Halitta, Su Ammy sun kasa ganewa, ina son miji na, ina son Usman fiye da tunanin ku, akan wani dalili zan zubda cikin Usman?"

Duban ta Halitta ta ke cike da mamakin yanda te ke ikirarin kaunar da ta ke yiwa Usman wanda ada bubu wanda ta tsana kamar shi, lalle shi ya sa ba a so a fiya zurfafa kiyayya ko soyayya ga mutum. Halitta ta ruko hannun ta, cikin rarrashi ta furta

"Amma me zai sa ki dawo gida? Idan har ki na kaunar Usman me ya sa ki ka yarda ki taho ke kadai? Menene dalilin shi na barin ki ki taho?"

"Abubuwa sun faru dayawa Halitta, kin fi kowa sannin yanda na tsani Usman ada, ina zaman zama na Daddy ya daura min auren dole da shi, bayan rasuwar Daddy ni kuma na yi kuskuran sawa a kamo shi domin ya sake ni, shi ne aka kamo kanin sa......"

Nan takwashe komai ta fada ma Halitta, ta kare da

"Bayan ya warke shi ne ya gaba daya ya guje ni, dan Allah ina laifi na Halitta? Wallahi ban san kashe shi za su yi ba, I just wanted to go home then not knowing that Usman is the only home I've, yanzu gashi ya ba ni takarda, Allah kadai ya san saki nawa ya min...."
Ta kare maganar cikin kuka.

"Ina takardar ta ke?"

Kai ta girgiza mata ta ce

"Ah ah wallahi ba zan ba ki ba, ba za a bude ba, ba na so ma na san yawan sakin da ya min, ban shirya ba Halitta, haka ko da wasa kada ki bari su Ammy su san babu igiyar auren Usman a kai na"

"Kai amma be kyauta ba, Usman be ruke amanar Daddy ba....."

"Ya yi iyakar kokarin sa Halitta, Ni na hada baki da ma su neman ran sa, kada ki ga laifin sa Halitta"

"Haka ke ma ba ki da laifi Zainab, kin yi komai dan neman mafita ne, kin yi ne domin ke samu ki tsira, kuma duk wanda yayi judging din ki base on that ba adali ba ne, you did what you thought was right for you"

Shiru su ka yi na wasu mintina kafin Halitta ta nisa, kana ta ce

"Nan da sati biyu zan koma Saudia Yakura, Amma kafin na tafi zan so a ce kin yarda an je makarantar ku a san ya makomar karatun ki ya ke, mate din ki fa sun yi graduating"

Murmushi Zainab ta yi, yayinda ta ja filo yanda za ta dan kishingida, sannan ta furta

"Shin ki na tunanin zan iya komawa makaranta a wannan hali da na ke ciki? Ku yi hakuri ba zan iya ba Halitta, waccar Yakurar da ku ka sani is gone...har abada.."

Tausayin Zainab ya dada rufe Yakura, gashi hawaye ya na son zubo mata, Amma sai kokarin ruke shi ta ke dan kar Zainab ta gani ta kara karaya. Tashi ta yi da sauri za ta fita, har ta kai kofa ta tsaya, ta dan juyo kadan yanda Zainab ba za ta lura da hawayen da ke zuba daga idanun ta ba ta ce
"Falmat ta ce wayar ki ba za ta gyaru ba, wacce iri ki ke so a siyo mi ki?"

"Waya? I don't need it for now, ku bar ta kawai....."
"Yakura! Wani irin rayuwa ce wannan? Hatta waya ma ba za ki ruke ba?"

Zainab na murmushi ta ba ta amsa da

"Sanda ina slaying kun ce na fiya fitina, yanzu kuma I'm managing myself kuna ta kokawa! Dan Adam kenan, ba na bukata dole ne?"

"Ah ah ba dole fa"
Cewar Halitta yayinda ta fice abin ta tana zubda hawaye.
AUREN SHEHU 2


Kamar yanda Ammy ta mata alkawari babu wanda ya kara tunkarar Zainab da maganar zubda ciki, hakan ya sa ta dan sami kwanciyar hankali, musamman da Anty Sauda ta hada na ta ya nata ta koma Maiduguri.

Cikin sati daya Usman ya hade kayan sa, bayan ya shawo kan su kawu Iliya da kyar sun yarda ya sake barin Rugar Shehu. Ana saura kwana uku ya tafi aka daura auren Muhamad Bello da Raqeba. Iyalle ce ta karbi rukon Cangwai duk da a zahirin gaskiya sun gano ba diyar Usman ba ce, rashin Rahila da Tanko ya sanya dole su hakura su zauna da ita.
Muhamad Bello ne da kan sa ya raka Usman har Yola gidan Alhaji Ibrahim Balla kamar yanda ya yi alkawari. Ya karbi bakwancin Usman hannu bibbiyu musammam da ya ga harkar cigaban da ya zo da shi. Cikin gidan gonar sa ya bawa Usman masauki na musammam, cewar shi zai iya zama kafin ya bude ido shi ma ya sami na shi.

Alhaji Ibrahim Balla magidanci ne mai kimanin shekaru hamsin da biyar a duniya, matar shi daya haka kuma dan sa daya tilo kamar tsoka daya a miya, amma hakan be sa ya sangantar da dan na shi ba wanda ake kira Umar. Ya tashi da tarbiya, dattako dadin dadawa kuma ga gata, ilimi wayews da ado tamkar dawisu. Umar saurayi ne mai shekara talatin da biyar a duniya, kasancewar ya karanta health economics a Fannin digiri ya koma yayi development studies a masters ya sa ya zama shi ne jagaba wajan habbaka sana'ar mahaifin na sa, wato sana'ar gidan gona.

Cikin kankanin lokaci Alhaji Ibrahim ya lura da halayyar Usman, da kuma amanar sa, hakan ya sa zuciyar sa kwadaita masa hada shi da dan sa Umar wanda kusan duk abin da ya shafi gidan gonar shi ke tafiyar da shi. Ga kuma ilimin Isalama da ya tabbata Usman na da shi wanda ya ke da yakinin lalle Umar zai amfana sosai, da wannan ya yi kokarin kulla abotan Usman da Umar, duk da kuwa ya san

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login