Showing 45001 words to 48000 words out of 55849 words

Chapter 16 - Auren Shehu 2 Complete Hausa Novel

TAKORI   

01 Oct 2025

27

in dai aka zo fannin wayewa hali ya sha bambam.

In da Allah ya kawo abin da sauki, sai ya hada jinin Umar da Usman, yanda ado da wayewar Umar ke burge Usman, shi kuma Usman kamala da ilimin addinin Usman ke burge shi, musamman da ya ji ya na larabcewa da wasu daga cikin abokan sana'ar su da su ke Larabawa, sannan duk wani muhadara da majalisin malamai Usman na kokarin zuwa wani lokaci har gayyatan Umar din ya ke. Kullu yaumin Umar na kokarin jan Usman jiki kamar yanda mahaifin sa ya ba shi umarnin, duk dai Usman na dan janye jikin sa ba dan komai ba sai gudun kar ya kwafsawa Umar, duk wata harka da ya shafi shiga cikin mutane sai Usman ya nemi ya janye jiki, har sai Umar yayi da gaske kafin ya yarda ya bishi. Duk wanda kuwa ya kuskure ko kallan banza ne ya yiwa Usman lalle kuwa a ga fushin Umar.


***

Hutun Halitta wacce ita ce mai debewa Zainab kewa ya kare, Sudais ya ce lalle ta hado nata ya nata ta koma Saudi ba zai iya zuwa Nigeria ba kamar yanda ya mata alkawari ba saboda yanayin aiki da ya yi yawa.

Da yamma likis Halitta shirye tsaf, sanye cikin bakar doguwar riga, suna tafe suna hira Zainab ta raka ta har mota in da Ammy da Falmat ke zaune suna jiran ta su kai ta Airport. Har ta zauna ta dubi Zainab wacce ke tsaye ta na duban ta. Sanye da hijab ruwan dorawa da ya kai mata har kasa, gaba daya ta sauya ba walwala ba farin ciki, kullum cikin damuwa ta ke har ta kai ya fara nunawa a jikin ta.

"Dan Allah Yakura ki rage damuwa ko dan cikin da ki ke dauke da shi"

Cewar Halitta cike da damuwa. Ta kara da.

"Zan mi ki addua in Sha Allah......"

"Idan har irin adduar da kuka min ne har Allah ya sa na dawo gidan ba na so, da ba ku min ba da yanzu ina tare da miji na..."

Jin haka Ammy ta kauda kai gefe. Falmat cikin ran ta cewa ta yi 'aha dama zancen kenan Yakura ta zama sai ka ce mayya!"

"In Sha Allah zan mi ki adduar mafi alkhairi a rayuwar ki"

Cewar Halitta. Zainab ta kada baki ta ce

"Usman ne mafi alkhairi Halitta"

Halitta na mai murmushin yake ta furta

"In dai shi ne t??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????oh Allah zai warware komai Yakura, bi'izinllah"

"Allahumma amen, Allah ya tsare ya sauke ku lafiya"

"Ameen ameen, ma yi chatting, ko da yake ke fa ko wayar ma ba ki da shi bare na chat, ki taimake ni Yakura, kira daga Saudi tsadi, ki samu yar waya sai mu ke gaisuwa ta social network, ki taimaka"

Zainab na murmushi ta bata amsa da

"Yar ana ce zai yi tunani akai"

Da haka su ka yi sallama jikin kowa a sanyaye.

***

Watannin Usman uku suna kasuwanci tare da Umar Balla. Hidimar da ke gaban sa be sa ya manta Zainab daidai da sakan daya ba, da ita ya ke tashi da ita ya ke kwanciya cikin ran sa. Wani sa'in sai yayi da gaske ya ke iya jure rashin ta. Har Umar ya kai ga ganewa akwai damuwar da ke tattare da shi, amma ko da ya tambaye shi dalili ce masa yayi babu komai kawai yakan dan yi tuntuntuni ne akan Rugar Shehu da kuma yanda zai bunkasa Rugar a sami cigaba.
Tafe su ke cikin motar Umar, kan hanyar dawowar su daga Mambila in da su ka je su ka yi cinikin shanu. Umar wanda ya ke baki, be da tsayi sosai amma kuma ba a kira shi gajere ba, haka kuma kyawun sa na ba yabo ba fallasa, sanye ya ke da kanana kaya, bakin wando da jar riga mai gajeran hannu. Usman da ke gefan sa sanye da wannan shigar ta sa da ya saba, riga yar shara, da rawanin sa da ya koma yi tun bayan tafiyar Zainab. Hankalin Umar kan kwalta ya furta

"Ni kuwa da za ka bi shawara ta Usman da fili za ka siya babba ko da kuwa a wajan, ka gina gidaje ciki in ya so ka kwaso duka jama'ar Rugar ta ka, ku yi zaman ku ciki "

Cikin kaguwa Usman ya furta

"Shin ka na ganin haka me yiwuwa ne? Kai mutane na fa ba kamar na ku ba ne, zaman bukka ya fiye mu su zaman binni da wahalar ta, Ni dai da ka ganni nan ni ke da kwadayin birni..."

Dariya Umar yayi jin furucin Usman, dan kuwa ya san har ga Allah ya sosa masa in da ya ke masa kyakayi. Kana ya ce

"Ina ce so kake ka bunkasa Rugar ta ku? Ka na tunanin wannan tsarin da Shugaban kasa ya ke so ya aiwatar mai yiyuwa ne? Ko ba ga yanda kudanci da wasu bangare na arewacin kasar nan ke sukar tsarin ba? Ka ga wannan Ruga settlement din ba abu ne mai faruwa nan kusa ba, Amma kai a karan kanka za ka iya kwatantawa ta ka Rugar, tun da babu laifi Allah ya ba ku arziki na dabbobi kwarai da gaske, da kuma taimakon yan kasuwa na nan Nigeria da kuma na kasashen waje wanda za su sa hannun jari a tada hanyar arziki mai girma, ina mai tabbatar maka za ka shahara kwarai"

"Kai wannan maganar ta ka ya sa ni tunani Umari, wa ya ga jama'ar Rugar Shehu kusa da birne!"

Umar na dariya ya furta

"Kai ba ma kusa da birni ba, idan ma cikin birni ka ke so ka kawo su ai ba abu ba ne mai wuya, dama naira ce wuyar, kuma Allah ya hore, ana nan ana nan sai ka aure matar birni, dama ana ta min maganar ka, ana ta kawo sakon gaisuwa fa"

Gaban Usman ne ya fadi, yayinda da Zainab ta fado zuciyar sa. Cikin kokarin waskewa da maganar aure ya furta

"Wace matar birni ce za ta so bagidaje dan kauye Irina? Ai mata sun fi son wayayyan mutum"

Umar na duban sa ta wutsiyar ido ya ce

"Wai kullum aka yi magana sai ka ke kawo wayewa wayewa wayewa! Wai kai wata irin wayewa ka ke magana?"
Zuciyar Usman daya ya furta

"Wayewa ai shi ne boko, ka ga kai da ka ke dan boko Umari hatta shigar ka daban ta ke, yanayin ka daban kai komai na ka ya fita daban ba kamar ni dan daji dan Ruga ba, wanda ko aji ban taba shiga ba bare a kai ga jami'a, ko zo a kashe ka da turanci ba ban sani ba...."

"Da larabci fa?"
Umar ya katse shi ya na mai take mota ganin ya sami sararin hanya.

"Ah wannan Alhamdulillah ai har labari sai na baka da shi"

Kai Umari ya gyada, be gushe ba ya kara da

"Wannan larabcin da ka iya ya fi turancin da ka ke ihun ba ka iya ba, ilimin da ke da shi na addini ya fi wannan bokon da ka ke tunanin shi ne wayewa, da ilimin boko shi ne wayewa da tun lokacin manzo (SAW) za a fara boko, addinin islama shi ne wayewa, ba ka taba yin bokon ba ne, da ka yi da za ka gane cewa komai da ake koyarwa a bokon musammam na bangaran kimiyya akwai su cikin alqur'ani da hadisin Manzo (SAW)"

Usman na mai gyada kai ya furta
"Allahu akbar"
Umar ya kara da

"Wannan rudun da ka ke gani na duniya, ba wayewa ba ne, wannan ba komai ba ne illa zamananci, ka ga wannan shiga tawa da ka ke gani ya ke burge ka, nan da shekaru masu zuwa sai ka ga ana kiran sa da old fashion, ma'ana an bar yayin sa, zamanin sa ya wuce, Allah shi ne zamani Usmanu! Haka kuma mutane nawa ne ga su yan birnin kuma yan boko amma hakan be sa sun kasa shirme ko rashin azanci a rayuwar su ba? Soboda sun yiwa wayewa fahimta daban har ya kai su ga halaka. Haka kuma ita jami'a da ka ke gani, waje ne koyan rayuwa, waje ne in da mutane iri iri daga sassa daban daban ke taruwa domin koyan ilimin boko, toh amma daga karshe ba ilimin kadai ake koya ba, har da dabi'u na dan Adam, mai kyau da mara kyau sai dai wanda yayi dace, da kuwa ilimin addini shi ma ya na da gurbi irin yanda boko ya samu a zukatar bil adama da kuwa boko ya zama ba koman komai ba"

Umar ya fadi ya na mai kallan Usman. Ya kara da

"Ai kai ma wayayye na Usmanu, in kuma ka na so ne ka zama dan zamani zan maisheka dan zamani na koya maka shigar yar birni, Amma fa idan matan birni su ka sako ka gaba ba ruwa na"

Ya karasa maganar ya na dariya. Shi ma Usman din dariyar ya ke, nan kuwa be san Umar har zuciyar sa ya ke magana ba, dan kuwa daga lokacin ya sha alwashin wanke Usman tas ya mayar da shi dan zamani kuma dan birni.

*****
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, in da Zainab ke renon cikin Usman, tare da fama da son shi da tsananin kewar sa, har ta kai in ta yi sujjada ta kan roki Allah ya cire mata soyayyar Usman daga zuciyar ta, amma sai ya zama tamakar abin ma dada karuwa ya ke, dan haka sai ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido. Halitta ce ta dage sai da Zainab ta sami waya, amma iyakar ta WhatsApp, bayan shi ba ta wani social network. Zainab the slay Mama ta zama salihar Dady a zahiri da badini, haka kuma ta na kokarin yiwa Malam addua sosai,

Bangaran Usman kuwa yanda Umar ya dage akan mayar da shi dan zamani ya sanya shi mika wuya wajan daukan darasi, ta suturun Usman ya fara, sai da ya tabbatar Usman ya ba da dukkanin kayan sa na ruga sannan tasa shi gaba ya masa ordering shaddu getzner na gani na fada daga SAFFAD Fabrics and more na Hajiya Safiyyah Ummu abdoul, . Rabin shaddu farare ne guda ishirin, sai kuma shudi, ruwan kwai, da kalar toka guda goma. Haka kuma ga material na maza da su boyel. Kanana kaya da takalma ne ya sa ka abokin sa mai shigo da kaya da Uk ya kawo masa. Tun Usman na kokawa akan kudin da Umar ya ke sa shi kashewa, sai gashi shi ma ya zo ya na alfahari da su bayan isowar kayan ya ga kyan su.

Dinki irin na zamani wanda yawanci irin na Umar din ne ya sa aka yiwa Usman, kai hatta roll on sai da Umar ya koyawa Usman yanda ake amfani da shi. A hankali ya ke kokarin fito da Usman gari duk da ba karamin fama ya ke sha da shi ba wajan saka kananan kaya, sai Usman ya ce masa shi wallahi ya na jin kan sa tamkar tsirara musammam idan rigar mai karamin hannu ce. Ran da kayan sa na Uk su ka iso ranar Umar ya zo har gidan gona ta tasa Usman a gaba lalle ya saka daya daga cikin su ya fito ya same shi ya na jiran sa cikin mota.

Umar na zaune cikin mota har ya fara tunanin sake komawa ciki ya taso kyeyar abokin na sa, sai gashi ya fito cikin kananan kaya, shudin riga mai haske, da shudin wando mai duhu, shi kan sa Umar be san sanda ya saka ihu ba ganin yanda kayan ya karbi Usman kwarai, fadi ya ke

"Yo mutumina! Lalle yau za mu dau magana!"

Cike da kunya Usman ya karasa gaban sa, sai a sannan Umar ya lura da silifas ruwan dorawa da ke kafar Usman. Ya na dariya har da kwarewa ya furta

"Toh Malam Shehu! Wannan silifas da ka sha haka ina zuwa?"

Usman na mai kallan kafar sa, da iya gaskiyar sa ya furta

"Yo menene toh? Silifa din ma ba ni sawa?"

"Ka ga wannan magana ta ka sai ka canza Alhaji, kar a ga gaye iya gaye amma in ya bude baki sai aji maganar yar Rugar Shehu"
Usman ya kai masa duka, Umar ya kauce ya na dariya, ya kara da

"Haka kuma tsakanin ka da silifas dan Usumanu sai dai a bandaki, wallahi babu in da zan kara zuwa da kai da silafas kafar ka!"

"Sai na yi zamana! Kai ni fa da na san haka za ka uzzara min da ban ce ina san wayewar nan ba!"

Umar na dariya ya wuce ciki ya na mai furta

"Zamananci dai ko, na fada ma ilimin addanin musulunci shi ne wayewa, wannan da ka ke koya zamananci ne, gishirin zaman duniya"

Usman na duban shi har ya shige ciki, cikin ran sa ya na mamakin yanda ya saba da Umar sosai, dan tun da ya ke be taba yin aminci da abota da kowa ba kamar Umar, cikin kankanin lokaci su ka saba da juna sosai kullum su na tare, haka kuma Alhamdulillah harkar gidan gona ta karbe shi, haka kuma shawarar Umar da ya bi shi ma da alama za ta bulle masa. Ya siyar da shanu fiye da dari biyu da hamsin daga cikin shanun sa, da kudin su ka yi cinikin wani katan fili duk da dai yayi wajan gari kadan amma babu laifi wajan da kwanciyar hakanli da kuma tsaro kasancewar yayi kusa da daya daga cikin check point na sojoji, in da dama nan su ka yada zango kusan na dundundin.

Umar ya fito dauke da daya daga cikin sau cikin da aka turowa Usman. Da kyar Usman ya yarda ya saka. Haka su ka fita ya na masa mitar ya takura masa, shi fa takalmin nan ya matsa masa. Asibitin hakurin da ya ke zuwa ya kai Usman, ga mamakin sa sai gashi dentist din da su ka gani ta ce Usman ba ya bukatar wanke hakori, hakoran sa are so perfect, sai dai Umar ne ke bukata. Ko da Umar ya koka sai Usman ya murmusa kana ya ce

"Kai ne fa Umar ka fadakar da ni cewa addinin mu shi ne wayewa, Manzo (SAW) ya ce ba dan kar ya takurawa al'umar sa ba da ya ce su dinga asuwaki kafin kowacce alwala. Ka ga ban san brush da wannan abun da ku ke shafawa kai ba, Amma na san aswaki da Manzo ya koyarda da mu, shi ya sa baki na ke da tsafta da haske"

Umar na gyada kai ya furta

"Hakkun ka yi gaskiya, Amma kuma wannan karan za ka kara da zamani, idan mu ka gama da asibitin nan za mu biya shopping mall mu siyo su brush da abin goge bakin ka ga sai ka kara wasai ko?"

Darawa Usman yayi, kafin ya kara magana Umar ya kara da

"Ka bari fa Usmanu, yanda ka zama gaye din nan sai fa mun yi da gaske, dan wallahi ba ka bina bashin rantsuwa matan da za su fara binka sai Allah, musammam ga ka da dukiya, fata na dai kada ka yi zaben tumun dare, na kuma san kai mai sani ne, ka ji tsoran Allah ka kuma roki Allah ya kare ka daga kaidin shedanun mata, ya kuma ba ka mace ta gari....."

"Amen summa amen"

Cewar Usman, cikin ran sa kuwa Zainab ya ke hangowa. Tunanin ko ta cigaba da rayuwar ta yanda ta ke a da ya ratsa zuciyar sa, be san sanda ya furta

"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Allahumma ajirni fi masibati haza wakallifni khairan minha!"
A tsorace Umar ke kallan sa ya na tambayar lafiya? Me ya faru. Shi kuwa Usman bakin kishi ne da ya taso ma sa ya turnuke kirjin sa ya sanya shi salati. Amsawa Umar yayi da babu komai, kawai ya tuna wani abu ne. Yayi saurin barin wajen gudun kar Umar ya gane halin da ya ke ciki, dan kuwa sirri irin na Usman ya sa har yanzu be taba bawa Umar labarin Zainab ba.

*****
Sanda cikin Zainab ya cika wata tara chif, ya rage saura sati biyu EDD din ta ya cika Halitta ta dawo Nigeria. Ganin yanda Zainab ta bude ta zama katuwa zama da kyar ta shi da kyar Halitta ta sako ta a gaba da tsokana, duk dai ita ma din dauke ta ke da na ta yaron cikin wata uku cif.

Wata ranar lahadi da yamma likis, Zainab da Halitta sun dawo daga strolling, Halitta ke raka ta kusan kullum safe da yamma. Su ka tadda Anty Sauda zaune gaban Ammy ta hada kai da gwiwa ta na ta sharbar kuka. Hankalin su ba karamin tashi yayi ba dan kuwa a tunanin su ko General ne ya mutu. Muryar Halitta na rawa ta furta

"Anty Sauda lafiya? Ammy lafiya? Wani abu ya sami Genaral ne?"

"Ba gwara wani abu ya same shi ba da cin fuskar da ya min! Ni General zai ci Amana?"

Jin haka Zainab ta samu waje ta zauna cike da mamaki, shin dama akwai ranar da Anty Sauda za ta kuka da General? Mutumin da ta ke ikirarin ta gama da shi ko tsinke ta aje be isa ya tsallake ba sai da izinin ta. Zainab ba ta yi mutuwar zaune ba sai da ta ji Anty Sauda ta furta

"Wai Genaral ya rasa wacce zai auro min sai yar aiki! Da ilimi na! Da wayewa ta! Da arziki na amma ya auri yar aiki na? Wata jaka yar kauyen kayayau! Har ya na ikirarin matukar ba zan iya zama ba toh kofa bude ta ke!"

Jikin Halitta yayi sanyi kwarai, haka ma Falmat wacce shigowar ta kenan ita ma ta tsinci maganar. Ammy kuwa ta dade da kasa magana tsabagen al'ajabi. Zainab ce kadai ta furta

"Tooooh yar kauye fa Anty Sauda? Ki na nufin yar kauye dai kamar miji na Shehu?"
Ta yi maganar da manufa biyu wanda in aka dauki Anty Sauda babu wanda be fahimci in da Zainab ta dosa ba, Anty Sauda ta furta

"Irin su fa tsinannun tsintattun mage! Kuma ita ma din bafulatana ce waya sani ma ko Rugar su daya shi ne ya min shune tsinannun! Sai na yi maganin su! Wallahi bokan ta ya mata karya yanda na sha wahalar mallakar Malam sai ba ta isa ta zo da ruguje min ba! Yarinya ce fa kankanuwa! Ga ta bagidajiya! Kin san mazan nan daga na barta ta na masa girki saboda business ya dan fara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login