Showing 15001 words to 18000 words out of 55849 words

Chapter 6 - Auren Shehu 2 Complete Hausa Novel

TAKORI   

01 Oct 2025

24

mamakin ta duk da dai ba ta ji kamshin turaren da ta saba ji daga jikin abokan ta irin su Mike ko Bobo duk sanda su ka rungumi juna ba, Sam ba ta ji warin datti ko na hammata da take kyautata zaton za ta ji daga jikin Usman ba. Jin hanyen sa na shafa gadon bayan ta sai da ta ji yar tun daka yatsun kafar ta har zuwa gashin kan ta, ba ta san sanda ta runtse idanun ta ba yayin da bugun zuciyar ta ya karu, bakin sa dab da kunnen ta na dama ta na jiyo numfashin sa, ya furta

"Ni mijin ki ne! Jikin ki nawa ne ina da ikon hada shi da nawa duk sanda na ga dama, ku ma na san zaki sakar min jikin na ki, ji yanda ki ka saki jiki kina mayar da numfashi, ko da yake ba abin mamaki ba ne, tamakar karya ki ke kin saba sakarwa ko wani kare da biri jikin ki......"

Kamar wacce aka watswa ruwan zafi haka Zainab ta farfado daga shaukin da ta shiga na kankanin lokaci sanadiyar rungumar da Usman ya mata, kukan kura ta yi ta na mai ture Usman hakan ya sa shi sakin ta ya na murmushin mugunta, dama abin da ya ke so kenan ya gasa mata bacin rai, ran ta ya soyu shi ne farin cikin sa. Cike da bacin rai yayinda idanun ta ke fitar da kwallar bakin ciki ta ke fadin

"Ni Zee? Ni ka yiwa wannan cin fuska ka na almajiri mai gadin gidan mu? Allah ya isa! Abin da ka ke min Allah ya ma ka! Mugu azzalumi! Allah ya isa! Kai ne kare! Azzalumin! You will pay for this wallahi you will pay for this!"

Usman na murmushin jindadi da gamsuwar halin da ya sa Zainab ya sa kai ya fita ya bar Zainab zube ta na kuka. Kukan na ta biyu ne, na tsanar Usman da kuma haushin kan ta da har ta bari kaskantacce kamar Usman ya rungume ta, sannan ya kara mata da zagi tare da bakar magana, har ya kira ta karya!

Ta na cikin wannan tunanin ta ji alamar an bude assabarin daki an shigo, ba tare da ta daga kai ta ga wanda ya shigo ba ta ce

"Na tsane ka! Kada ka sake kai hannun ka jiki na domin kai ba ma ka kai darajar kare da birin ba! Wallahi da na hada jiki da kai gwara na hada da dabba...."

Jin shiru ba a tanka mata ba ya sa ta daga Ido ta ga wanda ya shigo, Nan ta yi Ido biyu da kyakkywar budurwa fara sol, wacce dudu ba ta wuce shekara goma sha biyar ba, hannun ta dauke da kwaryar nono, kamar yanda Zainab ta bude baki ta na duban ta, haka ita ma ta ke kallan Zainab cike da mamaki musammam da Zainab ta tashi tsaye da kyar, yarinyar ta ga tsayi da dirin Zainab, cikin ran ta fadi ta ce 'Babu shakka dole Shehu yayi duk abin da aka ce yayi akan Kadon Nan, ciki kuwa har da daukan ta da yayi a bainar jama'a'

Ta ji labarin kyaun fata da ido da Allah ya yiwa Zainab, amma ba ta taba tunanin Zainab din haka ta ke ba. Kumatunta yayi jajur sanadiyar kalaman da Zainab ke fadi tsabagen nauyin maganar, Abu daya ya mata dadi shi ne , wato kenan akwai kiyayya ta gaske tsakanin masoyin na ta da Kadon sa, ko ba komai wannan zai kara ba ta damar zama matar shi.....

"Wacece ke? Ki taimake ni na tsira daga hannun wannan azzalumin almajirin...!"

Maganar Zainab ya dawo da ita hayyacin ta, Har ta budi baki za ta bata amsa da ta san wanda ta ke magana akai kuwa? Sai ta tuna gargadin Shehu na kada su sake su nunawa matar shi suna jin hausa bare su mata magana da shi. Dan haka kawai sai ta aje kwaryar hannun ta ta juya ta fita ta na ji Zainab na ce mata dan Allah ta tsaya.

Jim kadan ta kara dawowa tare da wata kwaryar mai dauke da kwan zabi, Nan ma Zainab ta sake kokarin yi mata magana, yarinya ta nuna kamar ba ta gane abin da Zainab ke fadi ba, ta aje kwarya ta fita. Haka ta na kai kawo sai da ta aje kwarya har biyar, na naman zabi, sai ruwa, sai kuma 'yayan itatuwa.

Jin shiru ba ta sake shigowa ba ya sa Zainab tashi cikin dingishi, dan kuwa kamar yanda marar ta ta cika da fitsari haka hanjin ta ya cika da tutu, gashi gaba daya jikin ta ciwo ya ke mata ba ta daburin da ya wuce ta sami ruwan dumi ta yi wanka. Ta na tafiya da kyar ta fito waje yayinda ta ke ware idanu cikin fatan Allah ya sa Usman ba ya nan dan kuwa sam ba ta kaunar sake ganin shi. Ganin fitowar ta mata da yara kowa ya bar abin da ya ke ya na kallan ta. Cikin dauriya Zainab ta ce da su

"Ina ne toilet please?"

Kallan ta su ka tsaya suna yi babu mahalukin da ya san abin da ta ke nufi da "toilet" ganin haka Zainab ta kara da

"Mtswww na manta da jahilai na ke magana! Toh ina ne bandaki!"

Babu wanda ya tanka mata, hakan ya sa Zainab komawa bukkar Shehu, ta dauko butar da ta gani aje ciki ta ci sa'a akwai ruwa, da ta fito ta tarar suna nan dai tsaye kamar masu jiran tsammani, Zainab na mai musu alama da butar ta kara fadin

"Bandaki....wanka...ina zan yi?"
Duka su ka sa mata dariya, iya kulewa Zainab ta yi, ta na shirin juyawa ta koma daki sai ga Bello ya shigo da sallamar sa, ganin shi Zainab na mai yi masa alamar wanka da hannun ta ce

"Wanka, ina zan yi?"

Bello ya mata nuni da wani fili da ke zagaye da kara can gefe, ganin yanda Zainab ta zare idanu ta na kallan wajan shi kan shi Bello sai da dariya ta kusa subuce masa, ga tausayin ta da ya ke ji.

Ta na mai dawo da hankalin ta ga Bello ta sake fadin

"Oh my God! Yanzu fisabilillahi wancan zagayen shi ne toilet din ku? Ni Zee ni ce zan yi wanka cikin zagayen kara?"

Shi ma Bello tsayawa yayi ya na kallan ta kamar sauran yan gidan. Hakan ya sa Zainab juyawa ta nufi bandakin ta na fadin

"Na manta duka sokwaye ne a dajin nan! Ace rasa mai jin hausa sai wannan azzalumin! Kai wannan masifa da me ta yi takama! Bari dai na je na gani ko zan iya wanka, Duk Daddy da Ammy su su ka ja min wannan masifa! You will not get away with this! Wallahi you will not bari na tafi gida!"

Cikin tashin hankali da tsoran dattin da kazantar da za ta je ta tadda ciki ta yi adduar shiga bandaki ta kusa kai. Wayam ta gani, kasa ne shimfide a filin Allah, sai dan zarni da ke tashi sanadiyar rana da ya daki kasar, sam babu ko da masai ta tsugunno bare na tangaran da Zainab ta saba hawa, gashi a zahirin gaske a matse ta ke. Har za ta koma ta sake tambayar su ko dai sun yi kuskure ne ba su gane abin da ta ke nufi ba, idanun ta ya sauka kan wani dan roba mai dauke da sosan waya na wanka, ta tabbatar bandakin ne, kila sun bambamta shi da na ba haya ne.

Cike da kyamkayami ta sami gefe ta yi fitsarin cikin dabara ba tare da ta tsugunna ba, hakan ya ba ta damar ruke tutun da matse ta, Da niyar neman wajan yin tutun da wanka bayan ta idar da sallah. Da ta gama ta dauraye kafafun ta da ruwa sannan ta fito daga bandakin tana kakkabe kakkabe yayinda ta ke jin wani iri a jikin ta tsabagen kyamkayami da tashin hankali.

Har ta yi alwala ba su dena kallan ta ba, ta na idarwa ta yi sauri ta shiga ciki hannun ta dauke da butar ta ke fadin

"Mayu kurwa ta kul sai dai ku ci kan ku!"

Dankwalin ta ta shimfida kan ledar dakin, ba tare da ta tambayi ina ne gabas ba dan ta san ma babu mai amsa mata matukar ba Usman ba ta tayar da Sallah daga zaune, ta rama Asuba sannan ta gabatar da azahar. Ta idar ta na tunanin wanda za ta tambaya ina ne bayan gidan da za ta kasayar da tutun da ke cikin ta, ji ta ke tamkar zawo ne ke shirin kama ta, gashi Rugar kaf babu wanda ke amsa mata in ban da Usman.

*****
Can birnin Kano kuwa tun washagarin tafiyar su Usman labari ya iski Ammy bayan ta bayar da abinci a kai masa. Ta yi mamakin dalilin tafiyar na sa ba sallama, amma ba ta kawo komai cikin ran ta ba. Hankalin ta be fara tashi ba har bayan da ta kira Zainab ba ta dauka ba, sai ma sakon txt da ta tura mata, ta yi tunanin rashin da'ar Zainab ne ya tashi kila Falmat ta sanar mata da zuwa Usman. Kiran ta da aka yi daga makaranta aka tabbatar mata da rashin ganin Zainab a dakin jarabawa ne ya tada hankalin Ammy, musammam da ta lissafa tafiyar Usman da kuma ranar karshe da aka ce an ga Zainab a makaranta, sai ga Ammy ta na kuka wiwi, haka ma Falmat wacce ita ce ta kira Anty Sauda ta fada mata halin da ake ciki. Sai da ta tabbatar mijin ta ya raba hotunan Zainab bariki bariki, check point na kowani hanya, haka kuma aka fara kokarin bincike ta hanyar kididdigar wayar salulun Zainab, sannan ta hawo jirgi ta tawo garin Kano.

Fada sosai ta rufe Ammy da shi fadi ta ke
"Kukan me ki ke Aleesha? Ba abinda ki ke so ba kenan? Kun cuci yarinya kun lalata mata rayuwa! Ga irin ta nan ai! Gashi na dai za ki yi biyu babu cifar gafiyar baidu! Shi mijin na ki dama babu shi, diyar ta ki ma Allah kadai ya san halin da ta ke ciki a raye ko a mace!"

"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Dan Allah Hajja Sauda ki dena fadin haka, ke ma kin san uwa ba za ta cutar da diyar ta da gangan ba! Oh ni Aleesha Yakura ko a ina ki ke? Ya Allah ka kare min Yakura! Kai amma yaran nan be yi halacci ba! Be Kuma yiwa Malam adalci ba! Be min adalci ba!"

Cewar Ammy cikin kuka. Anty Sauda wacce ta dau zafi matuka ta kara da cewa

"Ku Kuma fa? Kun mata adalci ne? Gashi kun jawo ya dakile mata karatun ta dan wallahi ko yanzu aka ga Yakura kun gama cutar da ita, she missed two exams, talk more of halin da ta ke ciki, kai Aleesha ba ku yiwa yarinyar nan adalci ba!"

"Innalillahi wainnailaihi rajiun!"

Cewar Ammy yayin da maganar Anty Sauda ke dada rura zuciyar ta. Wayar Anty Sauda ne yayi kara, ta yi saurin dagawa ta kara a kunnan ta ganin mijin ta ne mai kiran wayar. Nan ya sheda mata cewar sojojin da ke check point sun tabbatar da wucewar Yakura ranar da ta baro Yola zuwa Kano, haka kuma ta sake biyo hanyar a washagarin ranar a karo na biyu, Amma kada su damu in Sha Allah su na kan yin bincike.

Bayan ta aje wayar ne Anty Sauda ke fada ma Ammy halin da ake ciki. Ammy na mai daga hannu sama ta ce

"Ya Allah ba dan halin mu, Allah ka bayyana mana Yakura! Ba a ce an gan ta tare da Usman din ba?"

"Cikin motar haya wai zai san ko tare da wani ta ke tafe? Dama dai kuna da hotan almajirin ne da da sauki...."


Anty Sauda ta amsa mata ta na mai tabe baki cikin jimami.

"Yanayin shigar shi fa? Ai shigar sa daban ta ke da na mutane? Kai ta ya ma aka yi Yakura ta yarda ta bishi? Anya kuwa ba asiri ya mata ba kuwa?"

Cewar Ammy ta na sharar hawaye.

Anty Sauda ta amsa da

"Amen Ashe dai kuna kaunar ta kuka cuce ta"
Auren Shehu 2

5




Ko da ya isa gidan Hansai ba ta dena kuka ba, Iyalle ce ta masa bayanin rashin darajar da Zainab ta aikata musu, da kuma kwashe ruwan shan gidan da ta yi ta ja zuwa bukkar Shehun, Allah kadai ya san abin da ta yiwa Hansai sa'ad da ta leka dakin dan kuwa har lokacin Hansai ba ta dawo hayyacin ta ba. A fusace ya wuce bukkar ba tare da ya tambayi Hansai baasi ba, ya na sa kai cikin bukkar kafar sa ta sauka kan sauran ruwan wankan Zainab mai jirwaye da be gama shanyewa ba, haka kuma idanun sa ya sauka kan dan fantarin ta da ta wulgar gefe.

"Me ya faru a dakin nan?"
Cewar Usman a fusace.

"Au dama wannan bukkar daki ne? Caf ai ina na gane? Bayan hada jiki da irin ka ai sai an yi saukar dauda, wanka na yi......"

Wani irin mugun kallo da ya jefe ta da shi ne ya sanya ta dada gyara zama tana mayar masa da martani da irin kallan da yake mata. Tsiwar da ta ke masa be sa ya kasa ganin kyawun ta ba, duguwar rigar jikin ta ya mata kyau sosai musammam yanda ya bi jikin ta ya zauna daram. Haka kuma da niya ta yiwa bakin ta ado da jan janbaki duk dan ta boyewa Shehu halin kunci da ya saka ta ciki, dan ta lura ya gan ta cikin bakin ciki shi ne babban burin sa.

"Wanka ki ka yi cikin dakin nan? Yanzu fisabilillahi dakin nan ya miki kama da wurin kwana?"

Ta na mai daga gira ta ce

"Wallahi kuwa wanka na yi, ka fa san tsatona, ko bandakin masu gadin gidan mu ya fi bukkar nan daraja, bare na Zee, ka manta daga in da ka sato ni ne?"

Ya na jinjina kai ya kara da

"Da ruwan shan gidan nan gaba daya ki ka kashe ki ka yi wanka?"

Ta jinjina masa kai alamar
"Eh wallahi"

Usman yayi shiru kamar mai nazari, sannan ya furta

"Abin da aka yi bayan gida...."

"Kashi? Eh shi ma ni na yi wallahi!"

Yanda ta yi saurin katse shi duk bacin ran sa sai da dariya ta kusa kwace masa, wato lalle ya gane so ta ke ta tunzura shi ya yanke hukunci a kan ta, lalle 'yaro yaro ne' cewar Usman cikin ran sa, ya na mai murmushi ya furta

"In dai kashi ne ai mu muna maraba da shi, gwamnati ba ta ba mu takin zamani, dama da kashin mu ke taki, daga na dabbobin har na mu na mutane, Nan gaba in za ki yi sai ki min magana ni zan raka ki har daji yankin shukar mijin ki, kin ga sai ki saki jikin ki ki kasayar da hujja, yanda shuka za ta fito mu sami amfanin gona, yanzun ma ba ta baci ba na sa yara su kai daji....."

Yanda Zainab ta yi da fuska kamar mai shirin yin amai ne ya kara kawata nishadin Usman, be dena murmushi ba ya kara da

"Hansai kuma fa? Me ki ka mata?"

Zuciyar ta na tashi tsabagen tashin hankalin da furucin da Usaman ya saka ta, Ganin yanda idanun sa ke rawa jikin ta ya bata murmushi ya ke, cikin rashin fahimtar dalilin annushuwan sa duk wannan aika aikan da ta masa ta ce

"Ka tambaye ta mana! God you sting!"

"Abu duk lalacewar ki sai na tankwasa ki, idan ba haka ba ban Isa Shehu Usman ba, kin ci darajar amanar da mahaifin ki ya bani da kuwa sai kin kwashe kashin ki da hannun ki, haka kuma zan tambayi Hansai, matukar wani abu ki ka mata mai muni wallahi sai na aika kwatankwacin shi kan ki sai dai ita din ce ta ce ta yafe...."

"Allah ya sa kar ta yafe! Na tsane ka! Na tsane ku! Wallahi da ni ke da kai na da tuni na kashe kai na da wannan rayuwar azaba da ka saka ni....."

Shiru ya mata ya juya zai fita, har ya daga assabarin ya sauke, kana ya juyo ya na murmushin mugunta yayinda ya ke duban Zainab da idanun ta su ka cika da kwalla, ya ce

"Alhamdulillah, Alhamdulillah wannan shi ne kwatankwacin bakin cikin da na ke so na dasa zuciyar ki, ki sani wannan sumin tabi kenan domin kuwa nan gaba ba ni kadai za ki tsana ba Abu, na mi ki alkwarin kamar yanda ki ka tsani rayuwar wannan Ruga har kina tunanin kashe kan ki, sai kin tsani kan ki fiye da yanda ki ka tsane ni, wannan shi ne buri na, dan haka duk wannan abubuwan da ki ke aikatawa sun yi kadan su sa na karaya, ki sake sabon shiri..."

"Allah ya sa! Allah ya sa! Macuci! Allah ya isa"

Cewar Zainab cikin gunjin kuka. Yana dariyar jin dadi ya fita ya bar ta tana kukan takaici. Zuciyar sa fara sakamakon halin da ya bar Zainab ciki ya koma wajan Hansai. Wanda sai a sannan ta masa bayanin ganin Zainab da ta yi ba kaya ta na wanka tsakar daki, fadi ta ke

"Wallahi Kado batta mutunci, haka tibi tibi na gan ta..."

Cikin rarrashi Usaman ya mu su jawabi da

"Ku yi hakurin zama da Abu matukar kuna so na zauna da ku, idan kuma hakan zai zama da takura ku yi hakuri ku bari na hada nawa ya nawa na dau iyali na mu koma can birni....."

"Ah ah za mu zauna da ita Shehu, me yayi zafi da mu ka samu ma Allah ya dawo da kai, ai hakuri ya zama dole!"

Iyalle ce ta yi saurin katse shi. Cikin goyan baya sauran ma su ka yi alkawarin hakurin zama da Zainab, ita kuwa yar budurwa wacce ake kira Raqeeba zuciyar ta ce ta dada cushewa, lalle auren Shehu matukar yana tare da Kadon nan tasa ba karamin abu ba ne, ta yanke hukuncin lallba gyatumar ta Hansai cikin azanci ta bijirowa Usman da maganar auren.

Kamar yanda ya shedawa Zainab, yara ya sa suka kwashe kashin su ka kai daji, wanda da su ka dawo ko wanke hannu ba su yi ba su ka cigaba da hidimar gaban su.

Bayan da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login