Showing 1 words to 3000 words out of 29871 words
[2/6, 6:52 AM] +234 806 235 2006: ETERNAL LOVE
SOYYAYA TA HAR ABADA.
BY FAMS
DA Sunan Allah Mai Rahma Mai jinkai .
Ya rabbi ina rokonka da sunayanka tsarkaka ,yadda kabani iKon fara Rubuta littafin Nan lafiya cikin farinciki, kabani iKon kammalashi lafiya cikin farinciki.
wanan littafin sadaukarwa ne ga Yan uwana ,Allah yakara hade kawunan mu (Amin) ??
TSOKACi
nazo maku da labarin sabon littafina Mai suna ETERNAL LOVE wato SOYAYYA TA HAR ABADA Wanda ke kunshe da abubuwa daban daban Wanda zai Nishadantar da ku, kubiyoni Kusha labari.
??
1??
Pa pa pa pa.......karar saukar wani private jet kenan dayay landing a filin da jirgi ke sauka na mansion din Alhaji Yusuf A bulama , shahararran Mai kudin nan wato business tycon dayay fice a Nigeria.
Wani kyakkyawan matashine yafito daga jet din sanye cikin black t shirt Wanda ya dame masa jiki da wandon combat na kakin sojoji da p cap Wanda ya rufemai Rabin fuskar shi ,ga wani shegen eyeglasses daya Sanya ,hannunsa dauke da travelling back Wanda ke rataye a kafadanshi na Dama .daga kanshi yayi tane yashaki iska ,baya yayi da p cap dinshi , Masha Allah tubarkallah ,kallo daya take zakai masa kabawa kanka Amsa wanene shi wato jajirtattacen tsayyayen namijine Wanda haduwarsa ya zarce misali ,A shekaru Bazai wuce shekara 30 ba,Amma yanada shekarunsa. p cap din yasake janyowa ya rufe fuskarshi tareda Maida glasses dinshi at the same time Yana Sakin wani killer smile lokacin daya hango tawagar su Pappa dasuka zo taryashi .
without any thoughts ya duro daga jet din da scout ( bodyguard) dinshi ya budemai , gudu yafara kamar afilin daga jakarsa na rataye a kafadarsa.
Ammi ce tafito daga cikin wata black sonata 2022 itada papa ,sai Muneer fuskarka kowanan su dauke da murmurshi wane gonar auduga saboda murnan dawowar dansu Mafi soyuwa bayan shekaru biyar akasar France Yana karatu.
sai Mommy tareda Maya wacce keta tsallan murnan ganin Murad bakinta yaki rufuwa .
jakar dake hannun sa ya Saki Yana zuwa yay hugging Ammi so tight kamar zaa kwace masa ita ,sai Kuma ya saketa tareda dagata sama Yana spining.
Dariya suka hauyi gabadayan su Banda mommy dake yaken dole .
saukeni! saukeni! nacema Ammi tafada tana kokarin sauka .
sauketa yayi Tareda hugging dinta for the second time I missed you ,ay bansan lokacinda Alkalamina yafadi ba ,da Banga komai ba sai y¨¤nzu da yay murmurshi wasu irin fitinanun eyes ne dashi masu kyau ga wani saje daya Kara kawata face nashi ,Yana da dogon hanci da Kuma small lips masu dauke da kalan pink kyakkawane bana wasaba .
raba jikinsu Ammi tayi tareda rike chin dinsa taja a hankali .
Auuch it's hurt ! I know that's your purnisment for spinning me .sannan tace I missed you too.
Gyaran murya papa yayi wato mu bakayi missing dinmuba kenan ko ?
da sauri yajuya inda yaji muryan papa ya rumgume shi , don't say that papa I miss you as much .
Dariya A.yusuf yayi ya rumgume Murad tareda bubbuga bayanshi.Its ok son am kidding we are glad you are back here with us .
ya Murad aishikenan mun bata na daina kula ka cewar Maya tafada tana juyarda Kai alamun fushi.
Am so sorry my little pumpkin come give me a hug ,aikuwa da gudunta ta fada Mai Yaya...a taja sunan sa hugging dinta back yayi Yana dariya Nasan bazaki iya fishi da ya Murad dinki ba I know . Dariya tayi sanan tayi breaking hug din ,haka ma Muneer yay welcoming dinsa .ganin idon su Ammi yasashi karasawa wajen mommy ya gaida ta .
Amsawa tayi tana wani yake hakwara finally our sojan mu is back am so happy tafada ,ko kallo bata isheshi ba ya juya .Bai San Mai yasa ba but he dispise her so much .
Ok let's get going mutane na jiran mu agida .
Da sauri scout bodyguard dinshi ya budemai wata black rotan new model ,yashiga sukai zooming off to the mansion.
Convoy sukai saikace wani shugaban kasa .Tundaga wajen mansion din cike yake da tight security da motoci Nan manya manya na alfarma birjik ko ina yasha decoration ga wani cool music dake tashi a hankali ,mutane ko ina ana ciye ciye suna jiran isowarsu wajen.
" What the fuck!
Ya furta Yana zaro idanunshi waje ,yazaci iya family party ne ,Amma sai yaga mutane dayawa kamar wani biki.
Tsaki yaja am going to kill you Muneer yafada a hankali Dan yasan aikin Muneer ne .
Lumshe sexy eyes dinshi yayi Tareda Maida Kansa car seat .I hate noise pollution ya furta a hankali.
Motocinsu papa ne sukayi parking,yayin dana Murad yabi red carpet din da aka shimfida domin zuwan shi.
Jin an Bude kofar motar ne yasashi Bude Idanuwanshi dake rufe,
Muneer yagani face dinshi dauke da murmurshi alama yai masa daya fito.
Fuskarshi a hade kamar bashine yagama dariya yanzuba .
Zo kaji ihun Yan matan dake wajen ,da sauri ya Maida glasses dinshi tare da Jan hannun Muneer zuwa inda aka tanadar masa Dan zama, Yana zuwa ya karbi mic din dake hannun mc yafara magana wani slangs .
Papa dip wajen yayi don he's voice was killing Ammi he called out again ,juyowa Ammi tayi dake cikin friends dinta with a smile on her face ,
No amount of words will be enough to tell how grateful I am to you, having parents like you is the biggest of all blessings Muneer,Maya love you too yay masu blowing kiss tareda alamar heart da hannu.I need a rest yafada Yana barin wajen.
Bakajin komai sai tafi raf raf raf kakeji .Ammi da papa kuwa kowan nansu fuskarsa na dauke da murmurshi Dan sun San dalilin sa baicika son Taron mutane dayawa ba musamman wanan daya hada da outsiders,Maya kuwa sai blushing take kawayenta tai inviting sai kama kafa suke da ita wai tai masu hanya Dan dayawan su basuji dadin barin wajen da yayi ba ,dan saboda kawai su gansu sukazo.
Mommy kuwa tacika fam kamar ta fashe ,uhmm wanan Abu Yana ban mamaki taya Dan mijinki zai ambaci sunan kowa Amma banda ke ,duniya ta dauka bare abun magana baya kadan.
Banni da Dan kutumar uba ni zaisa a bakin duniya yayi kadan wallahi ,ina raga masa ne saboda wani dalili nawa Dana barwa Kaine ,Amma yaro baisan da wuta yake wasaba baisan wacece Azra ba hhhhh Amma da sannu zaa zo wajen ,tafada tana wani munafikin murmurshi.
Kai tsaye yanufi cikin gidan.
Hasbunallahu wa ni imal wakil, Allahuma Arzukuni wanan gida fadar haduwarshi ma bata lokacine , mutumin da shine number ta daya na kudi a kasa Saidai a hada gidansa Dana shugaban kasa a kyau.
Chandeliers tako ina, ga masu ayki Nan kowanensu sanye da uniform sai Miko gaisuwa suke Amma ko bi takan su baiba ,burinshi kawai yaganshi a bedroom dinshi .
Tun daga falon shi yafara wurgi da kayanshi yarage dagashi sai singlet da wandonshi,hannu yasa ya Kuna switch na dakin .
What ?! Grandma what the hell are you doing in my room?
Zuwa Nayi musamman don mu gaisa da Mai gidana don nasan ni da ganinka saika kusa shekara.
Ok I see you are missing as much yafada Yana kashe mata ido tareda zuwa don ya bata hug .nifa dadina dakai idonka a tsakar ka yake da wanan shekarun nawa zaka rumgume don lalace tafada tana daukan pillow ganin ya taho gadan gadan Dan ya rumgumeta.
Yana zuwa tashiga Maka Mai pillow Yana tarewa suna zagaye dakin ,fakon idonta yayi ya hugging dinta tareda bata peck a chicks dinta yay maza ya fada toilet tareda sa key ,hannu tashiga tafawa tana sallallami zaka fito kasame jairin yaro laifin iyayenkane dasuka barka a kasar nasara har kake koyan dabiunsu tafada tana ficewa daga dakin .Yana duk abunda take fada yay smiling old woman.
Alhaji Yusuf A bulama shahararran Mai kudine Wanda yay fice , mutumin borno ne dane ga marigayi malam Ado bulama ,malamine Mai karantar da yara karatun addini anan jahar ta borno Wanda Shima saboda iliminta na addinin islama yay fice ,matan sa hudu na aure Kuma Yana da tarin yara ,acikin matan nasa akwai mairama wato grandma yar garin gombe ,wacce suka hadu lokacin da aka gayyace su wani Musabaka a garin na gombe wacce itace tazo ta daya gasar ,Tunda malam Ado ya daura idonshi akan mairama yaji kamar Bai taba soyyaya ba nutsuwar ta da kammalarta ne yajashi ga fadawa cikin kaunar ta ,bayan gama gasar ya tura daya daga cikin dalibinsa na hannun Damanshi bin sawun su har Saida yagane masa gidansu ,
Aikuwa Bai kasa a guwwa ba yaje Gidanasu yasa Akai masa sallama da mahaifinta Wanda Yana ganinsa ya shedashi gaisawa sukayi ,anan Yagaya masa abunda yake tafe dashi ,murna sosai Alhaji Musa Dan fillo yayi yakuma amince da bukatarshi na neman auran mairama .
Baa dau lokaci Mai tsayi ba malam Ado ya auri mairama bayan karamin yakin da matan sa sukayi ,ta tare a Maiduguri babban gida wato family house tunsu .
Mairama macace Mai tsananin hakuri shiyasa Malam yake ji da ita Wanda hakan ke Kara janyo mata bakin jini gurin matansa ,suka dauki Karan tsana suka daura mata .
Sau shida tana sai datai haihuwa shida suna mutuwa , ana bakwanne ta haifi Alhaji Yusuf Shima bata wani sarai dashiba Amma cikin hukuncin ubangiji sai ya rayu.
Haka ya taso cikin ukubar Yan uba ,ba Mai Yi dashi shida maihaifiyarshi sai mahaifinsa .
Haka rayuwa taita tafiya har ciwon ajali yakama malam Ado Wanda kafin rasuwarsa Saida ya rabama yayasa gadonsa ,Sanin irin tsanar da suke nuna ma Yusuf da mahaifiyarsa ,Amma mah ,saboda Rashin tsoran Allah Yana rasuwa suka tada Rigima sai an sake raba gado Wanda karshe sukayi rabonsu na son zuciya suka wawashe komai .
Hakan dasukayi bakaramin bata ma Mairama Rai yayba kunsan bafulate da zuciya ,Nan tasaida Dan abunda suka bar masu suka bar garin suka koma gombe .
Kwanci tashi haka Yusuf yake zuwa kasuwa da kakanshi inda ya hadashi da amininsa yake koya masa kasuwanci.a hankali ahankali saigashi Shima yafara kafa nashi rumfar ,dayake Allah yasamasa albarka a harkar sai gashi Yana tasamun budi .
Bayan shekara uku Musa Dan fillo yarasu wato kakanshi yaji mutuwar sosai saboda sunshaku dashi .
Haka rayuwa yaci gaba da tafiya har lokacin daya hadu da mommy wato Azra inda tazo sayyaya shagon da mahaifiyarta wacca takasance mace Mai shegen son kudi ,ita kuwa Azra Daman nutsuwar ta sai a hankali tunda taga Yusuf gashi Kuma kyakkyawa she kenan taketa masa kwarkwasa ,shi Kuma haka Nan yaji ta burgeshi yakuma yaba da ita .
Baibar taba harsaida tamai kwatancen gidan su yakuma mata alkawarin zuwa .
Tana fitowa mahaifiyarta ladi ta tareta Mai yace maki ? Ya Baki wani abune ?
Kai ladi tafada kanta tsaye cikin Rashi kunya Dama sun Raina ta basa wani kallonta da gashi itada yanuwanta , mahaifinsu kuwa dashi da hoto duk daya don ladi ta gama dashi ta mallake don macace Mai biya biyan bokaye ga son kudi kamar Mai.
Wasa wasa sai ga Yusuf da Azra sun fara soyyaya haka suke ta tsarsa kudi kamar haka Amma baya gani ,saboda soyyata rufe masa Ido .
Nan labari yajema mairama mutane suka tsegunta mata halayan ladi dakuma yayanta ,Nan fa hankalinta yatashi tai kokarin rabasu Amma abun yaci tura .
Hankalin Yusuf Saida yatashi ganin mahaifiyarsa da gaske take Bazai auri Azra ba har Saida yaje ya sanar ma baffannin ta da Kyar suka shawo kanta ta amince Akai auren Amarya Azra ta tare gidanta da angonta Yusuf anzuba soyyaya kam ,kudi kuwa haka ta rika tasarsa dayake Mai kyautane har Saida tasaima iyayanta gida ,tabasu jari ,aka aurar da yayyanta Biyu duk Yusuf shi yay masu komai .ladi kuwa kamar zuba ruwa akasa Tasha yah tana auran Mai kudi sai wulakanci .zuwa gidan Yan tsubo kuwa bakama hannun yaro ,duk ta koyama yayanta binbokaye .waiyazubillah.
Haka rayuwa taci gaba da tafiya Azra shiru ba haihu ga Yusuf da masifar son yara ko fita suka Yi yaga yara sai yadauke su ko yasai masu allawa abun bakaramin bata mata Rai yakeba gashi ita har y¨¤nzu shiru ba labari .
A haka Allah ya hadashi da wani amini suka kulla kasuwanci Wanda har yakasu ga fara fita waje suyo kayyayaki arziki sai bunkasa yaka yakai mahaifiyarsa makka bayan ita ,yabiya masu shida Azra shekara na zagayowa ya biyama iyayanta baba mahaifinta harda kukansa tsabar murna .
Kwanci tashi ba wuya su Azra an doshi shekara 15 ko barin wata ,Nan fa abokanai suka fara zugashi harda masu bashi kannansu Amma duk yaki amincewa,kwasam mairama ta tada Rigima itafa a dole sai Yusuf ya Kara aure don hakurinta yakai karshe Dama can bata kaunar Azra ,Nan fa hankalin Azra ya tashi sai gida gun mahaifiyarta tazaiyane mata koma ,suka dau hanya sai gidan Dan Aljan Amma ba nasara don yasanar masu cewar mairama ta tashi a tsaye akan danta saboda haka duk ayki da zasu Yi a y¨¤nzu bazaiyiba inkuma suka zafafa daya daga cikinsu zai rasa ransa ,haka suka koma gida ransu a bace ganin ba nasara don yasanar masu cewar da rabon Yaya.
Kwasam Allah ya hadashi da Ammi yar kasar Ethiopia lokacinda suka je Saro kaya .farat daya yakamu da Santa Itama haka .Yana dawowa yasanar ma Mairama ,ay kamar zata zuba ruwa akasa don murna ,takuma kwabeshi karya sanar ma Azra .haka kuwa akayi Azra tasaki Baki Jin zancen aure ya lafa hankalinta a kwance har wani kiba tayi fresh da ita .yabata kyauta kudade yace tasai duk abunda take so ta dauka aykinsu ne yaci don an hadasu da sabon boka.
Kwasam wata ranan asabar da yamma taga ana shigowa da kaya can Kuma sai guda .matane ke shigowa gidan da kaya suna zuwa dayan part din Wanda aka gyara ,don lokacin da ake gyara ta tambayeshi yace mata saboda arinka sauke Baki zai gyara.
Jikinta na rawa tayi hanyar part dinshi ko dankwali .
Samunshi tayi Yana waya sai murmurshi yake saki shikadai daga gani yanajin dadin hirar dayake .
Yusuf ! Yusuf da sauri yakashe waya ya gyara zamansa lafiya Mai ya faru kike kwalamin kira ,kasa bashi Amsa tayi sai window data je ta yaye curtains din ta nunamai dayan part mata nata shiga da kaya.
Hannunta zaje juwa kan kujerar daya tashi suka zauna ,sai lokacin tasamu bakin magana ,wai ya haka Yusuf ina nuna Maka mata nata shigomin gida kaikuma ......guda taji tunkan yafara magana .
Wani ashar ta lailayo kan bura uba Yusuf nikama kishiya ?
Tsayaki ji Azra karki min mummunan fahimta wallahi auran Nan danayi Badan in muzantaki bane nayishine da...kaga dakatamin malam karka kalallamaini da dadin Baki ,ni zaka wulakanta kayi aure Bada saninaba tafada yayin da take dukan kirjinta .
Wato Saida munafukar tsohuwarka tasaka ka Kara aure....
AZ..ZZ..RA yafada Yana daga hannu almamu zai bugeta ,fisge hannunta tayi ta hankada shi yayi baya kamar zaifada tafice da gudu kamar mahaukaciya, Wallahi sai anyi mutuwar kasko agidan Nan Saidai kowa ya rasa ya juyota tana fada .
Aybaisan lokacin da yayi sufa dareta mikewa yabi bayanta Dan yasan zata aykata abunda tace.
Kitchen tashiga ta dauko ashana tafita da gudu ,dakin dasuke ajiye gen tayi Nan ma tadauko galan na petir bata tsaya ko inaba sai side din Amarya ta dura ashariya .
Nanfa hankalin Yan uwan Ammi yatashi don su atunaninsu mahaukaciyace don basajin hausa.
Ganinta dauke da galan ga Kuma alamun kamar fada take suka dau haske habawa kafa Mai naci ban bakiba Nan fa kowa ya fara kokarin tsira da ranshi daidai lokacin Yusuf ya karaso baiyi wata wata ba ya wanke fuskarta da Mari bashiri ta Saki galandin.
Zaune suke gabadayansu ladi da yayyan Azra za hakuri suke badawa kamar sayi sujjada yayinda Azra ke zaune a kasa Yana Rusa kuka.kanwar maihaifiyar Ammi ce tace Sam yarsu bazata zauna da Azra karta jeta kashe masu ita a banza .A Nan ne mairama takada Baki tace aykuwa bata Isa ba inhar baza ta iya zama da kishiya ba to saidai Yusuf ya sauwake mata .Nan ne fa su ladi sukaita banbaki harsuka hakura aka tsaya a zai raba masu gida .Hakan baima Azra Dadi ba don ta daukan ma kanta saitayi ajalin matar Yusuf komin dadewa .
Bayan meeting ladi tasa Azra a gaba ta zageta Tas kin bani kunya in Banda ke shashashace mahaukaciya Taya zakice Zaki kashe kishiyar ki a bainar jamaa ,kina ganin inkinyi haka ke Zaki tsira ? Ta karkashin kasa yakamata mubi .
To ke ladi da har kike cewa takarkashin kasa zamubi mucimma burinmu ba agabanki Dan Aljan yaje in mun matsa daya daga cikinmu zai rasa ransa ba ? So kike ni bakinciki yakasheni nikenan .cewar Azra
Mts wani lokacin kan ladi baya dauka Dan de bake Akai ma kishiya bane zakice haka cewar bashira .
Shegiya tsinana zugata to.mara mutunci ay gashinan ke saboda Rashin hakurinku kin sake kaso aurenki shi Kuma kamalu gashi can sai aukin shaye shaye wannan jaraba har ina .
Uhmm nace y¨¤nzu kuka fara gani .
Da kyar ladi ta shawo kan Azra ta kwantar da hankalinta hartasata bawa Yusuf hakuri har da kukan munafunci,har gida taje tabama mairama hakuri.
Lokaci yay ta tafiya kwasam saiga ciki ajikin Ammi ,murna awajen masoyan Yusuf baa magana ,Nan hankalin Azra ya