Showing 57001 words to 60000 words out of 88219 words
fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
......D.c.o ya tura yaransa neman abokin mai napep, sai dai an samu wai baya nan yayi tafiya. Wannan dalilin yasa sukace zasu cigaba da riƙesa har sai an kamo abokin nasa. Hankalin ƴan uwansa ya tashi kamar yanda shima nashi ke a tashe. Amma dai d.c.o yaƙi saurarensu. Dan ya tabbatar musu da yana akan aikinsa ne. Babu yanda zasuyi dole suka haƙura suka tafi. A ɓangaren ƴan media suna nan suna cigaba da tattauna batun ɓatan Samraah. Yayinda hotunanta ke yawo lungu da saƙo kowa na faɗin abinda fahimtarsa ta bashi. Dan wasu har suna danganta komai da cewar ita ta jama kanta. Dama taya zata taɓa irinsu Maash tace zata zauna lafiya. Ai gashi nan ya mata lunbu-lunbu da ga ƙarshe ya ruftata dan mawuyacine ace bashine ya saka aka kwamusheta ba. Musamman in akai dubi da yanda ta samu damar tattaunawa da shi ta yanda manyan ƴan jarida suka daɗe suna fatan haka amma basu samu ba. Wasu ko na ganin wani ne ya saceta dan kawai a ƙullama Maash sharri. Wasu na ganin ko dai MD ɗin nasu ne musamman yanda zancen son da yake mata ya karaɗe ko'ina, ga shi kuma an saka mata ranar aure da ya rage saura sati uku kacal. Wasu dai kuma zarginsu na akan Maash ɗinne dai da tunanin son da yake mata ne ya sashi aikata hakan ganin an saka mata ranar aure da waninsa. Hakama wasu zarginsu bai bar kan Baby ba itama jin TAKUN SAƘAR dake tsakaninta da Samraah ɗin akan Mansoor ba, hakama mahaifiyarta da tun fil azal ba son su Samraah ɗin take ba. Ga kuma abinda tayi a randa aka kai lefe. Kai hatta da abokan huɗɗar Mansoor ɗin wasu a ciki sun shigo zargin jama'a. Tawani fannin kuma akance maƙiyane kawai ko kidnappers ne kawai saboda yanda sunan Samraah ɗin ya samu ɗaukaka cikin ƙanƙanin lokaci game da shirin da take akan matasa da yanda take nuna illar lalacewar matasa a cikin al'umma. Kaso marasa ƙarfi kuwa na ganin adai bunciki sauran samarin Samraah suma dan zasu iya aikata komai ganin Mansoor na shirin wuff da ita, ko kuma shi ƴammatan Mansoor ɗin. Kai zance ne dai gashi nan kala da iri harda wanda ma bashi da ma'ana. Kamar wasa a haka sati ɗaya ta shuɗe ana fakon abokin mai napep. Ba'a samu damar damƙosa ba kuwa sai a randa take cika kwanaki tara ciff.
★ “Kidnapping kuma? Ni wlhy yallaɓai bani bane. Mizai sa nai kidnapping mutum? Idan na ɗauketa ma ina zan kaita?”.
Cikin tsawa yaron d.c.o dake tuhumar tasa ya ce, “Kai karka raina mana hankali. In ba kai bane ba to waye bayan abokinka ya tabbatar da kai ya bama key ɗin napep ɗin tasa? Kuma da ita aka ɗauketa daga nan ba'a sake jin labarinta ba har yanzu”.
“Tabbas ni ya bamawa yallaɓai. Kuma ba ranar muka fara yin haka da shi ba. Saboda nima lokacin da nake da napep ɗin nakan bashi. Hasalima nine na koya masa tuƙinta, da taimakona kuma aka bashi napep ɗin ma a office ɗin mu. Amma wlhy ni banyi kidnapping kowa ba”.
“Ƙarya kake yi kai ne. Tunda har ka iya barin gari sai yau kake dawowa a tunaninka komai ya lafa ko”.
“Ranka ya daɗe ni ban bar gari dan komai ba wlhy. Ƙauyenmu naje da yake ina noma duk shekara. Shine na je nakai taki gonata. Can ɗin babu network shiyyasa wlhy bamma san mike faruwa ba. Sai yanzu da nake ji ma a bakinka. Amma na tuna wani abu, idan ban manta ba da safe abokinmu da shima mukanyi irin haka da shi yazo yace na ara masa key ɗin keken Salisu zai amso saƙo a tasha, tasa na gareji sai azhar zai amso.”
Da sauri ɗan sandan ya ce, “Ka tabbata?”.
“Tabbas anyi haka ranka ya daɗe. Dan ƙanina ma na ɗakin a gabansa akai komai. Yaje kusan awa biyu sai gashi ya dawo ya kawomin yay godiya. Har ma naji haushi saboda ya saɓa lokacin daya dace ace na maidawa Salisu kasancewar yana fitar sassafe shi”.
“Yanzu ina zamu samesa?”.
“Anguwarmu ɗaya da shi, sai dai ta bayan layinmu gidansu yake. Shima kuma yana harkar adaidaitan, nasan yanzu baza'a iya samunsa a gida ba sai irin takwas haka ko bayan magriba gaskiya”.
“Karka damu zamu samoshi”.
Ɗan sandan ya faɗa yana miƙewa. Kai tsaye office ɗin d.c.o ya nufa. Bayanin da yaron ya masa duk ya maimaita masa. Goyon baya d.c.o ya bashi akan su tabbatar sun samo wancan yaron kafin zuwa safiya. Ya tabbatar masa da in sha ALLAHU za'ai hakan kafin ya bashi damar fita. Cikin girmamawa yay salute ɗinsa sannan ya fice. Shiru kawai d.c.o yay yana mamakin wannan irin juya-juya. Dan case ɗin gaba ɗaya ya ɗauki zafi saboda yanda mutane keta ka-ce-na-ce akan batun yarinyar, shi kansa yanda yaga an ɗauki al'amarin nata da muhimmanci ya sashi bibiyar shirye-shiryenta na baya a daren jiya, tare da shafukanta na sada zumunta dake ɗauke da fallowers masu yawan gaske, sai yaji ta shiga ransa. Gata dai ƴar yarinya amma akwai kaifin basira da nuna kwazo akan aikinta. Ga mahaifin Mansoor da Mansoor ɗin sun addabama rayuwarsu. Kowane motsinsu yanzu yana a station ɗinsu ne. Azalzalar su kawai suke faman yi akan a gano musu inda Samraah ɗinsu take su dai. Hakama Yaya Musaddiq idan ka kallesa sai ya baka tausayi, rashin dauriya kawai Mansoor ya fisa. Shiko Hafizzullah sai dai kuka. Yayinda jikin Abba ya fara sanyi, sai dai yaƙi yarda ya nuna hakan ga mutane saboda shakkar Mom..
⭐❤️⭐❤️⭐❤️⭐❤️⭐
Faɗa muku yanayin da nake ciki a kwanaki tara ɗin nan da suka gabata sam bazai yiwu ba. Dan koda da kwatance nace zanyi hakan bai zama lallai ku iya fahimtata yanda ya kamata ba. Abinda kawai nake so ku fahimta al'amarin sam bashi da sauƙi. Nayi kuka matuƙa Bily. Irin wanda ni kaina sai da na tabbatar da nayi sa. Sai dai ku sani badan kaina nake yinsa ba. Domin ƴan uwana biyu ne da nasan zasu fi kowa shiga tashin hankali ne. Sai kuma masoyina da ya rage saura kwanaki goma sha uku kacal ya amsa sunan mijina. Dai-dai da daƙiƙa ɗaya ban gaza wajen miƙama UBANGIJI kukana akan ya kuɓutar dani daga wannan ƙangi, ya sa ina da rabon komawa ga dangina. Bani da wani ƙarfin nuna yunƙurina saboda halin rashin lafiya da nake ciki. Ciwon kai da zazzaɓi sun kasa barina. Na kuma gagara faɗama wanda ke zaryar ajiyemin abincina da har yanzu bai taɓa min magana ba, ban kuma taɓa ganin fuskarsa ba. Sai a yau da safe kusan goma da rabi sai gashi ya shigo. Nayi mamakin shigowar tasa saboda ba lokacin kawo min abinci bane, kuma baya shigowa dama sai zai kawo abincin. Amma ganin waya a kunnesa yasa na zuba masa manyan idanuna. Har gabana ya ƙaraso, batare da yamun magana ba ya tsaya ƙiƙam a kaina kamar wani mai gadin gidan kallon kwallo. Wayar dake a kunnensa ya sauke. Batare da yamun magana ba ya ajiyeta a ƙasa gabana. Na ɗago da nufin kallonsa maganar da akai cikin wayar ta katseni. Da sauri na maida kallona akan wayar, wata dattijuwar murya ce da nake ji kamar na taɓa saninta, cikin nuna ƙarfin iko da tabbatar da rashin wasa aka furta.
“Nasan zuwa yanzu kin fahimci inda kike ba wajen wasan yara bane ba. Ba kuma filin ɗaukar rahoto bane ko dandalin sada zumunta. Baƙya buƙatar wani bayani kam dogo yanzu ƴammata. Sanin wanene ni? Miye dalili? Mi kika aikata duk bana buƙatar ji. Video recording ɗin hannunki kawai nake buƙata, mi zanyi da shi, ko minene alaƙata da shi ba damuwarki bane. Na duba a duk wayoyinki babu kin ciresa a ciki, ya rage naki faɗar inda yake ko wajen wanda yake a bani ke kuma ki kama gabanki. Idan kuma kikace zaki zama mai taurin kai tabbas zaki dawwama a wannan ɗakin tamkar kabarinki, dan ko mutuwa kikai a ciki zamu gina miki kabari mu bizne ki batare da wani mahaluki ya taɓa sanin hakan ba har abada. Kuma zan mallaki video ɗin sannan na ɓatar da duk wani ahalinki daga doron ƙasa. Zaɓi ya rage naki lokaci na tafiya miki dan nasan kina shirin zama amarya”.
Ni kaina ban san sanda murmushi ya suɓuce min ba. A karan farko na wani ja numfashi mai nauyi tare da sakin wata siririyar dariyar ƙarfin hali. Kaina tsaye na nima na furta,........✍️
_Shin wa kuke tunani ne? Gashi dai Sam-G tace muryar Dattijo, kai nafa ruɗe nima. Amma mu haɗu a comment section ko wani zai canko mana🤔😞_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒐𝒖𝒓_
........“Oh oh wannan irin dogon zance haka Baba, bakinka ko gajiya bayayi. Kayi haƙuri ina jin girman tsufarka a cikin raina duk da ba ganinka nake ba. Sai dai ga saƙo zan baka. Ka faɗama shi wanda ta aikokan shin tsoron Samraah Abdul-wahab Gwarzo yake ne? Ko kuwa shi bai cika namiji bane daya laɓe a bayan tsufarka a yimin barazana? To idan yana kusa da kai ya buɗe kunnuwansa da ƙyau ya saurareni, idan kuma baya kusa ka masa recording. Ni Samraah Abdul-wahab Gwarzo ban yi video ɗin dan aimun barazana na bada ba. Idan buƙatarsa yake mu haɗu gaban hukuma. Idan kuma yana da ƙarfi yazo muyi gaba-da-gabq kwanta. Sai dai ya sani ko dungurin wani da ga cikin ahalina yayi bazai sauke hannunsa ba video ɗin zai baza duniya. Dan haka zaɓi ya rage nashi, ku farka daga wannan nannauyan barcin na barku lafiya”. Da ga haka na yanke wayar tun kafin shi ya yanke. A fusace wanda ya kawo min wayar yake hararata. Amma nai biris da shi na ɗauke kaina. Kiran wayar aka sake yi, da sauri ya ɗauka ya kai kunne. Ban san mi aka faɗa masa ba na ga dai ya sake hararata ya juya ya fita. Nima da harar na raka nasa bayan ina taɓe baki. Da ga haka na zame na kwanta zuciyata na wata irin tafasa. Sai dai a wani gefen ina jin daɗi dan koba komai na samu bakin zaren wanda yasa aka kawoni nan. Zargin mutane da yawa ya fitamun a dai zuwa yanzun, musamman ma jama'ar gidanmu.
Barcina na sha yau da rana sosai, dan yanzu bani da wani aiki sai inci in kwanta ɗin, sai idan naji na gaji ne da zaman waje ɗayan sosai nakan ta zagaye ɗakin wani lokacin ma na ɗan motsa jikina dai, saboda na fahimci na fara ƴar ƙiba ba kamar sanda aka kawoni da bana cin abinci ba sai yawan kuka. Ganin zan halaka kaina a banza nama masoyana asara yasa na fara cin abincin tunda nasan ban isa canja abinda yazo a littafin ƘADDARA ba ai. A yanayin ɗan ƙarfin jiki dana tashi da shi ya sani jin zan iya tunkaresa koda zai ƙarar da numfashi na, sai dai zan fara da wannan mai kawo min abincin a yau ɗin nan. Amma sai zuciyata ke gargaɗina da hakan kai tsaye, dan haka na shiryama raina wata sabuwar dabara ina kuma addu'ar cin nasarar hakan amma sai na gwada plan ɗin farko baiyi ba tukunna dai.
Kamar ko yaushe cikin ƙarfin hali na tashi nai wanka da ruwan ɗumi. Kaya na saka na sake dawowa na kwanta a katifar dan jiri nake ji na neman ɗibata. Ina nan kwance tamkar mai barci naji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar. Luff na sake kwantawa har aka shigo aka sake maida ƙofar aka kulle. Sai da ya shigo tsakkiyar ɗakin sannan ya tsaya cak. Idanu na ɗan ƙara buɗewa ta can ƙasa yanda zan gansa da ƙyau. Ƙofar bayi yake kallo, nasan kuma dalilin yin hakan, dan kan shower ɗin na ɓalle nabar ruwa nata zuba. Ka ɗan naga ya duƙa yana kai yatsansa biyu ƙasa ya dangwala, sai kuma naga yay saurin ajiye ledar abincin hannunsa ya nufi toilet ɗin da alama ruwan ne ya fara fitowa.
“Lafiya miya faru?”.
Na faɗa a hankali. Bai tanka min ba, bai kuma tsaya ba. Na saki murmushi ina tashi zaune. Bayansa na bi. Duƙe na samesa yana ƙoƙarin buɗe hanyar da ruwa ke fita gaba ɗaya da ɗayan hannunsa. Ɗayan kuma ya danne pipe ɗin shower ɗin ya cusa babban yatsarsa a ciki ya tsayar da ruwan. Sai dai duk da haka yana ɗan fita sii. Da wannan damar nai amfani nima na shigo ina faɗin, “Tun ɗazu nake kiranka dan ka duba amma baka amsamin ba.”
Kaɗan ya juyo ya kalleni sai kuma ya sake maida kansa ga abinda yake yi. Ni ko na duƙa kamar zan janye masa boket dana jiƙa kaya ciki na samu nasarar zare wayarsa. Da sauri na tusata cikin rigata. Na janye bokatin na fita abina. Sake komawa nai cikin katifar nai kwanciyata. Sai dai zuciyata sai faman gudu take a ƙirjina. ALLAH ALLAH nake ya zo ya fita kafin ya farga babu wayar tasa. Amma bai fiton ba sai kusan bayan minti goma. Batare daya kallan ba ya nufi hanyar fita. Cikin rawar jiki ina jin ya kulleni ta baya alamar ya tafi kenan. Na ciro wayar. Naji daɗin ganin babu password jiki, cikin rawar jiki data hannau na saka number Yaya Musaddiq na danna masa kira. Harta katse bai ɗauka ba. Hankalina ya sake tashi jikina har kakkarwa yake. Sake ƙoƙarin kira nake ina kallon ƙofar. Nan ma ta shiga amma har tana neman yankewa babu alamar za'a ɗauka. Nama gama sadaƙarwa dan idanuna har sun cika da hawaye sai ya ɗaga. A yanda yay sallama cikin wani yanayi na mutum mai damuwa yasa idanuna sun ciko da ƙwalla. Cikin rawar muryar alamar son sakin kuka na ce, “Yaya Musaddiq nice. Nice kandalarka. Dan ALLAH kuzo ku fiddani anan karna mutu. Yaya banda lafiya ciwo zai kasheni. Sun kawoni nan sun ɓoye kullum sai dai suyita bani abinci kawa.....”
Fittt naji an ƙwace wayar daga hannuna. Hannu ya ɗaga zai ɗauke fuskata da mari sai kuma miya tuna oho masa ya tsaya cak. Niko tsoron da naji na kar ya kai ƙaton hannunsa kaina ya sani dunƙilewa waje ɗaya na rumtse ido. Jin shiru banji saukar marin ba na buɗe idona. Dai-dai nan yake ƙoƙarin fita a ɗakin. Na taso kuwa da uban gudu na nufi ƙofar nima, ina gab da ƙarasawa ya datse da sauri. Zubewa nai a wajen na saki wani kalar kuka mai ban tausayi da cin zuciyar mai sauraro.. Ina a wajen ko cikakken minti biyu baiyi da fita ba sai gashi ya dawo cikin sassarfa. Jin saukar handkerchief kawai nai a saman face ɗina. Kamar waccan ranar nayi niyyar yunƙurin tashi amma abinda suka shaƙa min yaci ƙarfina. Kamar ƙyaftawar ido na sulale ƙasa, daga haka ban sake sanin abinda ke faruwa ba kuma..
✨●●)(●●)(●●)(●●✨
Gaba ɗaya yanda Yaya Musaddiq da Mansoor suka rikice bama su fahimci wayar ya yanke ba. Dan suna tare ne a mota sanda Samraah ta kira wayar. Da farko hankalin Mansoor ba'a kan Musaddiq yake ba. Sai da yaga yayi wata shegiyar zabura yana ƙwala kiran sunan Samraah jikinsa har wani gab-gab yake na rawa sannan. Wayar shima ya fisga jikinsa na rawa yake faman kiran ta. Sake ƙarɓewa shima Yaya Musaddiq ɗin yayi. Duk sun rikice sun ruɗe, jin dai ɗif ɗin yayi yawa suka ɗan fara dawowa hankalinsu. Sai sannan suka fahimci wayarma ta yanke. Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga rige-rigen sakkoma Yaya Musaddiq. Dan harga ALLAH yana matuƙar ƙaunar ƙanwarsa. Mansoor ma dai idonsa cike yake da ƙwalla, cikin ƙarfin hali ya buɗe motar ya fita. A ɗan zabure Musaddiq ya figi wayarsa dai-dai sanda Mansoor ke fita a motar, dan tunawa da ya dace ma su kira d.c.o fa. Kiran nasa kuwa yayi, sai dai ba'a ɗagaba. Cikin tashi hankali ya cigaba da kira. Har 3 miscall, fita yay da sauri a mota. A jikin motar ya samu Mansoor jingine idonsa a lumshe. Cikin sauri-sauri yake faɗin, “Na kira d.c.o amma bai ɗagaba. Inaga ya kamata mu ƙarasa police station ɗin mu sanar masa”. Shima ɗan zaburar Mansoor yay, cikin alamar gamsuwa da zaburowa ya nufi motar yana faɗin, “Hakane yaya, wlhy ni kaina ma ya tushe na rasa mizan yi, amma bara na kira Yaya Attahir ya nemesa tunda abokinsa ne”.
Musaddiq ya gamsu da hakan, cikin ƙanƙanin lokaci Mansoor ya sanarma yayansa halin da ake ciki, kafin suma su ɗauki hanyar zuwa police station ɗin. Sosai Mansoor ke gudu, hakan yasa cikin ƙanƙanin lokaci suka iso station ɗin. Sun samu d.c.o baya nan ya fita sai dai Yaya Attahir ya kira Mansoor ya sanar