Showing 1 words to 3000 words out of 30501 words

Chapter 1 - HAUWA KULU 3 BY TAKORI

TAKORI   

29 Jun 2024

4268

 ‘YAR CIKIN BADALA
(HAUWA-KULU)
3



PAID BOOK
SUMAYYAH ABDULKADIR
babbangoro2015@yahoo.com
07030137870
(whtsp only)

SADAUKARWA
SADAUKARWA NE GA DUK MAKARANTA LITTATAFAINA ‘YAN CIKIN BADALAR KANON DABO.











HAUWA-KULU -3
BAKO DAGA KUMASI (GHANA)
Y
ammacin ranar wata Alhamis, da misalin karfe hudu na yamma, iskar damuna na kadawa mai dadin gaske a tsakar gidan su Hauwa, hadari ya gangamo, gab ake da fara ruwan sama. Innar Hauwa na zaune akan kujera ‘yar tsugunne a madafinta tana kullin alalar leda wadda za suci da daddare.
Idan ta kulla ta saka a tukunya. Tana yi tana sauraron radiyo abunta cikin shirin jakar magori A daidai wannan lokacin ita kuma Hauwa tana daga cikin dakinta a kwance kamar wadda ruwa yayiwa duka sabida yadda ta kudundune a cikin bargo bisa dindimemiyar sabuwar katifarta (vitafoam), amma kuma zuciyarta babu dadi, a kwanakinnan ta rasa me ya sa ta ke jin babu dadi sosai a cikin ranta, amma data yi tsam da ranta ta yanzun kusan ta gano dalilin hakan; LIKITA SARHAM! Shine dalili ba komai ba.
Yau kusan kwanaki bakwai kenan da take fama da wannan damuwar a kasan ranta, don ganewa da ta yi Dr. Sarham ya daina kulata, ga shi dai yana zuwa gidan ba wai ya daina zuwa ba, amma yanzu sai dai kawai ta jiyo muryarsa daga waje shi da Inna in suna babatunsu, ko nemanta ya daina yi a cikin gidan in ya zo. Balle ya zo kofar dakinta ya takaleta da Magana yadda ya saba.
Hauwa ta yi duk iyaka tunaninta don gano laifin da tayi masa da har yasa Likita Sarham ya daina shiga sabgarta ta rasa. Kamar ma gaba yake da ita yanzu.
Hauwa ta muskuta ta gyara kwanciyar ta. Wata zuciyar ta ce da ita. "To ke Hauwa? Me ye abun damuwa don Sarham ya daina kula ki? Tunda dama ba don ke yake zuwa gidan nan ba, yau ina ganin ikon Allah don Innarsa ne yake zuwa fa shine har albarkacin ta yaga dama ya kula ki. Name zaki dorawa kanki damuwa a kansa don ya ga damar daina kula ki kuma??? Tayi wani tsaki irin na jin haushin kai. Ta ce wa ranta, daga yau ita ma za ta koyi fita sabgarsa, kome yake ji dashi ya tara ya samu, me yake takama da shi da ya wuce likitancin da bai iya ba? Ina dalili da za ta damu kanta akan fushinsa da ita, fushin ma na babu gaira babu dalili? Da dai ace ta san ta yi masa wani laifi ne sai ta damu, amma tunda ta san bata yi ba ina dalili?
Don ko ta jiyo muryarsa a falon Inna, ta jawo mayafi ta fito daga daki, ta tsaya daga bakin kofarta ta gaishe shi, ta lura tana kuma jin sai ya ga dama yake amsawa, yana wani basarwa kuma a shalake kamar an yi masa dole sai ya amsa. Daga amsawar kuma baya kara ce mata komai saidai ta gaji da tsayuwarta anan ta koma dakinta.
Ta yi kwafa data tuna jiya haka haka yayi mata, ta girgiza Kai tana fadin. "yayi da ‘yar halak. Ni na damu kaina da shi, mutumin nan fa babu wata alaka ta jini tsakaninmu, banda ta zumuncin Allah da taimakon da ya saka kansa yi mana. In haka ne me zai sa canzawarsa gareni ta dame ni? Tunda ita Inna ai bai canza mata din ba kaamr ma yafi zuwa akai-akia yanzu har fiye da da, koda ba zai jima ba.
Amma abin mamaki, duk yadda ta so ta daina damuwa din da sharetan da Dr. Sarham yake yi, ta kasa daina damuwar, abin ya dameta, saboda ko ta ki ko ta so, ta san cewa Sarham wani mutum ne mai matsayi a rayuwar su, wanda ya taka muhimmiyar rawar data fi ta dan uwan jini a rayuwar ta data Innarta, wanda ya fi gaban ta dauki gaba da shi, wai don kawai ya daina kula ta bisa ra'ayin kansa.
Muhimmancinsa a gare ta ya zarta haka. Aka ce ka yiwa dana dam uzuri sau saba’in kafin ka kama shi da yi maka laifi.
Ta saka a ranta me zai hana in yazo ta tambaye shi ko tayi masa laifi ne?
Tunanin da Hauwa ke ta yi kenan wuni guda yau ta kasa moruwa, ta jibge a katifa, ta kasa fitowa ta taya Inna aikin alale, tunda kullin alala ne zata iya don ta saba tayata, ta kasa jin dadin ranta ko kadan.
Ga yawan mafarkin Babanta Malam Bilyaminu data ke yi a kwanakinnan wai ta ganshi ya dawo amma bashida lafiya. Wannan ma ya kara dugunzuma damuwar Hauwa kuma ta kasa gayawa Inna don kada ta daga mata hankali in tace tana yawan ganin Malam ya dawo cikin halin rashin lafiya na shanyewar barin jiki.
Cikin wannan halin damuwar da Hauwa ke ciki, harda hawaye na diga ta gefen idon ta, daga bakin kofar shigowa tsakar gidansu aka rafka wata irin sallama cikin muryar girma da koshin lafiya.

Gaban Innar Hauwa ya yi mugun yankewa ya fadi ras, jin muryar da ko cikin barci ta ke ba za ta kasa gane mai muryar ba. Muryar da ko mutuwa tayi ta dawo bazata manta sautin amonta ba, muryar data yi amanna da cewa mutum daya ne mai ita a duniya, muryar data yi kewa sama da shekaru bakwai.
Mai sallamar ya sake cewa, "Ikon Allah, Allah dai ya sa ban yi batan kai ba, anya?".
Sai idanunsu suka sarke shi da matarsa ta lalle (Safiya) Innar Hauwa, ya saki hamdala duk da ta kara girma da nauyin shekaru tana nan yadda ya barta da kyan jikinta, ya soma takowa zuwa gareta da hanzari, yana sakin hamdala ba kakkautawa.
Fatar bakin Inna na rawa da karkarwa har ya iso ya tsaya gabanta, ta ta mike tsaye ta kai hannu shima yana rawa ta taba gemun shi ta ce,
"MALAM!"
Ya rike hannun ta shikuma y ace “na’am Safiyatu. Na godewa Allah da ya hada fuskokinmu lafiya”.
Da dai ta tabbatar Malam Bilyaminu ne a gabanta ba mafarkai take yi ba. Sai ta tafi baya luu! Za ta fadi jikin bango, ya yi maza ya taro ta jikinsa yana fadin,
"Safiyatu, kada ki yi min haka, in ki ka fadi ki ka ji ciwo kafin mu gana fa? Ai godiya ya kamata ki yiwa Allah da ya hada mu a raye cikin koshin lafiya".
Ina! Inna Safiyya idanu sun bace, ta sume a jikin Malam Bilyaminu.
Shimfideta yayi a wurin wato ya kwantar da ita a dandanyar kicin din ya tafi ga famfo ya tari ruwa a buta da sauri ya dawo ya shiga shafa mata a fuska zuwa wuyanta. Ba jimawa Inna ta soma sauke ajiyar zuciya amma bata bude idanun ta ba.
Daga can daki Hauwa ta ke jin motsin su, ka san makaho da ji! Sai faman tambaya take,
"Waye a nan? Nace waye ne ya shigo? Inna kina ina, mene ne?"
Da taji ba'a amsa mata ba don a lokacin Inna ta samu bude ido suna kallon kallo itada Malam Bilyaminu, sai ta taso ta tako ta fito a hankali tana dafa bango, ta iso tsakar gidan tana faman juya idanunta harrr! Masu haske da girma.
“Wato an ga Inna ta fita shine aka shigo ayi mata sata ko?”
Malam Bilyaminu ya dago ido, yana duban diyarsa HAUWA-KULU da wani irin bege fal idanunsa, tana takowa tana ta tambaya alhalin idanunta a bude tangararas, "Wane ne ya zo wai? Nace waye anan?" Alhalin kuma ga idonsa ga nata tana kallonsa saidai ba cikin Ido ba.
Sanyin ruwan da ya shafa mata ya sa Inna farfadowa daga suman wucin gadin da ta samu ta saki ido kawai tana kallonsa, daga bisani data tabbatar bazata farka daga wannan gizagon da idanunta ke mata ba sai ta mike zaune, ta ja gefe ta zauna ta fashe da kuka tana rufe idanunta, ta ce.
"Hauwa Babanki ne yake yi min gizo, yau har a jikina na ji shi, naji hannunsa jiki na na kuma ji kamshinsa kusa da ni".
Malam Bilyaminu ya ce cikin wani irin yanayi na shauki, da cikowar hawaye fal a idanunsa.
"To tunda gizo nake yi bari kawai in koma kada in tsorata ku".
Ya mike zuwa kan tabarmar da ke shimfide a tsakar gidan ya z auna yana cewa, "Ku yarda ni ne ba gizo ba, ba kuma fatalwata ba, ba kuma gizo nake yi muku ba. Yau ne Ubangiji ya kaddari ganawar tamu. Babu tsimi babu dabara sai ga Sarki Allah. Alhamdu lillah da na same ku a raye, shine babban farin ciki na".
Hauwa ta kwalalo manyan idon waje, domin tabbas ta shaida muryar mahaifinta.
Ta taho inda ta ke jin sautin muryar tasa gadan-gadan gaba-gadi.
Malam Bilyaminu ya tare ta, ganin zata taka shi ta wuce ta kansa, kuma nan da nan ya fahimci cewa Hauwa-Kulu ba ta gani, wato (ta rasa idanunta).
Ji ya yi zuciyarsa ta wani irin tsinke, mummunan tsinkewa. Da ya haifar masa da faduwar gaba. Ya kama hannunta ya zaunar da ita a gefen jikinsa, ya ce, "Nana Hauwa'u! haka Allah ya yi da ke???"
Duk dauriyarsa da farin cikinsa na sake saduwa da iyalinsa Malam Bilyaminu sai ga shi yaja gefe shima kamar yadda Inna tayi, ya sa habar babbar rigarsa yana shatatar hawaye yana kuka harda sharbe. Ba abinda zai ce banda Allah yayi masa sakayya.
Sai mu ce farin ciki mai yawa ne cakude da alhinin halin nakasar da ya samu Hauwa a ciki ya gudana a wannan ranar a gidan Malam Bilyaminu.
Kuka-kuka, farin ciki- farin ciki, haka suka kasance a yammacin ranar. Har aka kira mangariba. Kafin Inna ta share ido, tace da Baban Hauwa ya dau kaddara kamar yadda suka dade da dauka suma, ya karfafe su a cikin halin raunin da ya same su. Sun riga sun yi amanna da kaddarar Hauwa-Kulu.
Sun yi sallar magriba da isha tare kenan cikin jam'I, Malam din ya limance su kamar yadda suka saba acan baya, bayan sun idar, Malam Bilyaminu sai bin gidan yake da kallo na mamaki da tu'ajjibi. Entirely modern! Babu bishiyun su na baya kuma. Ya ce, "Safiya, ki fidda ni duhu, kaina ya daure, a kan yadda aka yi gidan nan ya koma haka, da inda Hauwa’u na ta samo lalurar makanta??? Ya Subhanallah".
Inna tasa habar zaninta ta share Ido, taji wani irin karfi da kuruciya sun sake shigarta yau, kai har ma da koshin lafiya, tace,
"wallahi daga annobar 'Apolo'.
Daga nan ta shiga fedewa Baban Hauwa abubuwan da suka faru a bayansa, daga biri har bindi.
Har abin da Zakari ya yi musu, na rushe gidan, da yadda rayuwarsu ta kasance cikin walagigi bayan nan. Baban Hauwa kuka kawai yake yi kamar ba namiji ba da sharbe yana sharewa da habar babbar rigarsa. Yana fadin “tsakanina da ZAKARI sai hisabin Allah”.
Ya ce, "Yanzu shi LIKITA SARHAMU din ina yake?" zan so kwarai na ga wannan jarumin, kuma BARDE! Ga rayuwar iyalina”
Inna ta ce, "Za ka ganshi ba da jimawa ba, duk da dai ya gaya min nan da sati biyu shi da iyalinsa za su koma garin Jeddah inda yake aikinsa na likita".
Malam Bilyaminu ya ce, "don Allah bani lambar wayarsa in kira shi. Ya zama lallai in yi masa godiya, in iyayensa na raye su ma in yi tattaki har inda suke in yi musu godiya kafin mu bar Kano".
Inna ta kai shi sabon dakin da yake a kulle, wanda shine nasa tuntuni, dama a gyare dakin yake har da gado da katifa Sarham ya saka a dakin, sai ta dauko wankakken zanin gado ta shimfida, ta hada masa ruwan wanka a bandakinsa, wanda ke like da dakin.
Sai da ya shiga wanka ta je ta zubo masa alalen wanda ta karasa a gurguje, tana aikin tana tazbihi na mamakin kyakkyawar kamar da ta ga maigidanta Malam Bilyaminu a ciki, babu alamun wahala ko kadan a tare da shi, maimakon ta ga ya kara tsufa furfura ta baibaye shi sai ta ga ya kara gyagijewa wato ya kara kuruciyama a idanunta fiyeda kafin tafiyarsa, ya yi 'yar kiba kib-kib irin ta hutu kuma cikin kyakkyawar suttura ta farar shaddar yayi ta lokacin (mirror), yar ciki da babbar riga wadanda suka sha aiki.
Malam yana fitowa wanka, Inna ta gabatar masa da abinci, bayan alalen kafin yayi wanka har tayi maza ta tuka masa tuwon masara da miyar kuka, ta zauna gefensa tana firfita masa sai cewa ta ke, "da dai a ce na san yau Malam zai dawo, da na yi masa girkin tarba na musamman". Shi kuma ya murmusa cike da kewarta da kewar kulawarta irin wannan, yana kara hada Zakari da Allah cikin zuciyarsa, a fili kuwa cewa yake,
"Ai kema kinsan na yi kewar tuwonki Safiyya, kin san tukin tuwonki da dandanon miyarki daban yake da na kowa.
Kwarai na yi kewar abincinki, kulawar ki, tattalinki da addu'ar ki gareni kullum zan fita, addu’ar nan taki ta Allah ya sa in kawo muku halal, in ciyar daku daga halal.
Umh, ya nisa, “kada Allah ya maimaita mana rabuwa da juna kona kwana daya ne Safiyya, ina addu'ar daga nan mu wuce har gidan aljannah tare. Duk kuma abinda zai sake samunmu, ina rokon Allah ya same mu muna tare da juna.
Yadda na same ki ba ki yi aure ba har zuwa wannan lokacin ya kara min yarda da kaunarki gare ni Safiyya, zan kuma saka miki da abishir din cewa har abada ni naki ne ke kadai. Allah ya yi miki albarka”.
Haka sukayi kwanan matsanancin farin ciki a yau. Malam Bilyaminu da matarsa Inna Safiyya. Hauwa kuwa ko na minti daya ba ta runtsa ba a nata dakin don farin ciki da godiyar Ubangiji, kwana ta yi sallah tana godewa Ubangiji da ya dawo da Babanta, a lokacin da duk suka fidda rai da rayuwarsa. Ta rasa inda zata tsoma ranta don farin cikin yafi gaban kuka ko dariya, tuni ta manta da damuwar wani Sarham da take ciki.
Washegari Inna ta fito madafi don dora abin kari sai ta tadda Hauwa a kicin ta hada kai da gwiwa a kan kujera 'yar tsugunno. Ta saka kai a tsakanin kafafunta kamar wata marainiya, ita ba kukan fili ba, ita ba kukan zuci ba.
Inna ta karasa gabanta a hakali tace, "o'oh! Kayyasa Kulun Majadun, Kulu mai tuwon ‘yan birni! Lafiya da sassafen nan ki ka zo madafi kikayi wannan irin zama na kaka-nikayi haka?”
Ta dafa kanta tana tambaya cike da kulawa irin ta Uwa. Uwar ma irin Inna, da ba duk UWA ba! Uwar Hauwa wadda babu irinta.
Hauwa kamar jira take Inna ta tankata sai ta fashe da kuka mai tsuma rai, cikin kukan ta ce,
"Inna.... !".
Kukan ya kara kwace mata da karfinsa na gaske.
Inna ta kyaleta har tayi mai isarta, don ta san in Hauwa na kuka bataso ma a rarrasheta sai ta kai intaha, kafin da kanta ta gaji da kukan, ta share ido, tace, "Inna shikenan ni yanzu banida amfani? Ba zan iya amfanawa kaina da ku iyayena komai ba? sai dai in zame muku liability?
Inna na tashi da dokin na yi wa Babana girkin barka da zuwa, girkin da bait aba cin mai dadinsa ba, tun ban kai haka ba ina yi masa girki yana shi min albarka, idan baki manta ba.
Sai da na shigo madafin yau na tuna ashe fa ba zan iya aikin wuta ba, kada in tsumbula hannnuna a mai ko garwashi, tunda ba ni da ido, komai ma bazan iya ba Inna na taimakon ki, na zama banida amfani?".
Zuciyar Inna ta karye, wani irin karyewa, cike da 'maternal love' wanda ya motsa mata, ta ce,
"Idan Allah ya nufa, da albarkacin tsarkin Al’qur’ani, da tsarkin mulkin Allah sai ganinki ya dawo kamar na kowa tun a duniya HAUWA-KULU, sai kin ga idon ‘ya’yan ki, sai kun hada ido a lokacin da kike shayar dasu, ina ji a jikina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login