Showing 21001 words to 24000 words out of 30501 words

Chapter 8 - HAUWA KULU 3 BY TAKORI

TAKORI   

29 Jun 2024

4273

daya gashin ya sauka kasa, tun daga lokacin ban kara gwadawa ba, don kaina tal kwabo ya koma Aunty Sumayyah".
Sumayyah ta dinga dariya, wait tal kwabo, ta ce, "Danjangwabo ai 'traditional relaxer' ne, wa ya aike ki?
Insha Allahu da mun sauka a Jiddah zan kai ki saloon din dana ke zuwa a yi miki na amarci wanda zai burge Bhaiyana".
Hauwa ta rufe ido tana jin kunya. Sumayyah tace "ah toh! Don in gaya miki gaskiya Bhaiya Dan kwalisa ne na gani kasheni, kuma yana so ‘yar kwalisar matar shi".
Sumayyah ta dauke mata damuwa da hirarrakinta masu ban dariya, duk na Sarham da irin gayunsa, nan da nan ta rage mata kewar Inna.
Sabuwar rigar barci fara kal, tsayinta iya kauri Sumayyah ta dauko ta bata ta saka, ta bata lotion mai kyau na neutrogena tana shafawa tana mata hira.
Sosai Hauwa ta sake da Sumayyah, ta jita (at home) don Summy ta maida kanta sa’ar Hauwa, duk da cewa ta girme ta da shekaru uku kwarara.
Mama da Abba na babban falo, Abba Prof. na cin abinci, Sarham na gefensa suna hira shi ya sa ya kasa tsallake su ya je don ya ga yaya Hauwa ta ke coping a gidansu, ya san dai zuwa yanzu ta fito daga wankan. Sumayyah kuma bazata barta ta nemi komai ta rasa ba.
Sarham duk da kasancewarsa dan bokon zamani hakan bai cire masa dattaku da halin kawaici akan mata irin na manya ba. Bokonsa bai cire masa wasu daga halayen kawaici irin na mazan da a gaban iyayensu ba, duk kuwa da kasancewar iyayen nasa yan zamani ne kuma 'yan boko suma. Banbancin tashin yaro a kasar musulunci irin Saudiyya da kasashen turawa kenan
Abba ke tambayarsa ko yaushe 'annual leave' din nasa zai kare? Kuma yaya ya tsara zaman iyalin nasa? Kafin Sarham ya shirya amsar bashi kuma yace.
In zaka bi shawarata, to Hauwa ka barta tare damu a nan, ta fara karatun degree a nan BUK tunda tana da WSSCE certificate, Jamb kawai zata zana a samar mata gurbi a duk tsangayar da take so”.
Abba Prof. ya kara da cewa, “bana so ta je Jeddah mata biyu su hada maka zafi, a matsayinka na likita mai bukatar nutsuwa wajen gudanar da ayyukan sa, Hauwa na bukatar (special care) in kun tafi kullum kana asibiti, matarka na jego, wa zai kula da ita? Tunda Sumayyah a makaranta ta ke zaune ba'a gidanku ba, don haka in har shawarata kake nema, to Hauwa'u ta zauna tare da mu a gidannan, Mamanku ta kula da ita, ni kuma in sa ta cikin jami'a zuwa gaba kadan mu ga me Allah zai tsara muku. For the mean time".
Sarham kansa na duke a kasa ya kasa dagowa balle Abba ya ga irin yanayinsa, da irin karbar da yayiwa shawarar sa. A da kam ya so ne ya tafi da Hauwa. Amma shawarar Abba Prof. ma abar dubawa ce, bai auri Hauwa don yayi rayuwa ta soyayya da ita ba, ko don biyan bukatar ransa, ko don ya yi auratayya da ita nan kusa, har gobe kallon kanwa yake yi wa Maijidda kanwar ma ta jini abar kulawa a gareshi, cikin dalilan da suka sa ya aureta harda dalilin zamowarsa sanadin nakasar idonta, da har gobe ya kasa yafewa kansa da kuma sauran dalilai masu tarin yawa, da bazau lissafu ba, ciki har da kaunar sa ta hakika ga Inna, da kuma alkawarin da yayiwa kansa na gina rayuwarta positively da tallafar ilminta koda idonta bai gyaru har abada ba.
Da kyakkyawan burinsa na ganin cewa ta zama wani abun amfani ga alumma, kuma abin alfahari ga iyayenta da duniyar masu nakasa. He wants to become HER PACESETTER in life! In haka ne kenan shawarar Abbansa tana kan hanya, kuma ita ta fi dacewa da Hauwa.
Bai auri Hauwa don sha'awa ko soyayyarbukatar gangar jiki ba irin wadda za’a kasa controlling ba, ya auri Hauwa ne don ya tallafi rayuwarta ya zame mata, ya ginata ta kowanne bangare ya kuma nema mata lafiya.
Da wannan tunanin Dr. Sarham ya amince da shawarar Abbansa na zai tafi Jiddah ya bar Hauwa tare dasu, ya dago a hankali ya ce, "Abba na amince da shawararka. Hauwa ta zauna karkashin kulawar ku, na tabbata sai tafi samu kulawa har fiye da a hannunmu".
Abba ya ce, “To masha Allah lelan Abba, haka nake so ka dinga fahimtata a komai, yanzu sai a samar mata karamar yarinya daga Shanono cikin yaran family dinmu, wadda za ta zama mai aikinta ita kadai ta kuma dinga raka ta cikin makaranta kullum, ko’ina ya zama suna tare, ko ni in zan fita in fita da su in kai su department dinsu.
In yaso sai su dinga dawowa da kansu in ta gama lectures su dawo gida tare da mai aikin nata. Zan yi wa Babanku na Shanono magana ya bamu aron 'yar sa Mardiya tunda ba su kai ga yi mata aure ba.
Yarinyar nan Mardiyya na lura tana da hankali sosai ga nutsuwa.
Har suka gama hira shi da Abba Sarham bai tsallake su ya je dakin Sumayyah gun Hauwa ba. Har sai da Abba ya tashi ya shiga turakar barcinsa, bayan ya gaya masa sati mai zuwa zai koma Jeddah, hutun nasa next week zai kare, kuma zai sayo mata (JAMB form) ya cike mata komai kafin ya koma in sha Allahu, don a lokacin Mama ta ke gaya musu an fara sayar da jamb form na wannan shekarar.
Bayan wucewar Abba bedroom dinsa ya rage daga shi sai Mama suka ci gaba da hira. Mama ta ce,
"Yanzu da gaske iyayen nata jibi za su koma Ghana? Su kuwa me yayi zafi hana da bazasuyi hakuri su zauna a mahaifar su ba?"
Ya ce, "Eh Mama, ni ma abun yana tayar min da hankali sosai don wallahi na saba da Innar Hauwa yadda ba kya zato. Saidai ko ke kika ji cikakken labarin Malam Bilyaminu da dan uwansa Zakari, zaki bi bayan hukuncinsa na yin nisa dashi shine mafi alkhairi gareshi da iyalinsa, ga dukkan alamu arzikin sa yana can".
Ya ba ta labarin irin yadda Inna ke sonshi da kula da cikinsa da abincinta mai dadi da tsafta, da yadda ta ke yawan yi musu addu'a su iyayensa ba dare ba rana. Da halin da Zakari ya janyo musu na shan wahala da sayar da abinci a tasha, sakamakon rushe gidansu da yayi, ya ce, “Mama, in na tuna hakan sai in ga hukuncin da Malam Bilyaminu ya yanke na barin Kano ya fi masa alkhairi fiye da ci gaba da zama da irin wadannan ‘yan uwan, kuma a haka dan sa na cikinsa ya dage ya kafa kahon zuka sai sun aura masa Hauwa.
Wallahi Mama ban yi niyyar auren Hauwa ba Allah ya sani, wadannan dalilan da wasu masu yawa suka sa na yanke shawarar auren nata kawai, don Jamilu da gaske yake auren Hauwa zai yi ko ta halin kaka, ya manta da ko waye ubansa garesu".
Mama ta jinjina kai, abun ya tsuma ta, a karshe kuma ta yi ‘yar dariya ta ce,
"kenan Jamilu ya tado tsohuwar boyayyar soyayya daga barci, kishi ya sa an yi gaggawar yin abin da ya dace".
Sarham ya yi wani basakkwacen murmushi, ya yamutsa fuska ya ce,
"Mama ni fa, ni fa in zan gaya miki ki yarda ba son Hauwa nake ba, I mean so na soyayyah, Mama ni Hauwa kanwa nake kallonta har gobe, kwatankwacin yadda nake kallon Sumayyah cikin idona".
Mama ta tsuke fuska sannan ta mike tsaye don tatsuniyar tasa ta fara isar ta, ita bazata taba yarda wai namiji zai iya kashe kudinsa da lokacinsa ya auri macen da baya so ba, ta ce,
"ka je ka gayawa wani maho din wannan tatsuniyar kanzon kuregen naka, ba ni mai shari’ah Maimunatu ba".
"Mama ki yarda da ni, ban taba yi ma wata mace kallon so bayan Madinah ba, ba don so kadai maza irina ke aure ba Mama. Dalilai da yawa sun fi komai saka maza kashi 90% yin aure ba soyayya ba, wallahi Mama dalilai ne suka rinjayi zuciyata na yi wannan auren amma ba so ba".
Mama ta ji wani irin babu dadi a ranta, kamar ita ce ta haifi Hauwa, mijin da ya auri Hauwan ya tareta yana gaya mata haka, ta kuma ji matsanancin tausayin Hauwa ya kama ta kan abinda Sarham ke fada a kanta.
Tun daga wannan lokacin Mama Mai Shari'a ta kudiri aniyar zata taimaki Hauwa-Kulu, za ta zame mata UWA kamar Inna, amma ba uwar miji ba, zata zame mata Uwa, kamar yadda Innarta ta zamewa Sarham ba tareda su sun sani bama. Ko albarkacin abincin da ta dinga bashi. An ce mai Da wawa…inda ake son dan sa anan yake.
Mama tace a ranta. Insha Allahu watarana sai Sarham ya furta SON nan da yake ta musawa da bakinsa. Sai ya so ta kamar, ko ma fiye da yadda yake son Madinah dinnan.
Mama ta mike ta ce masa, "Ma'assalam Sarham zan shiga daga ciki, don na ga tatsuniyar taka ta yau ba mai karewa ba ce, mu kwana lafiya.
In kun yi waya da “MATAR SO” din ka ce ina gaida Waheedah, tun safe nake gwada layinta (tana nufin Madinah) na kasa samu, in ya shiga sai ya katse, ban san me ya samu wayar tata ba, kwatakwata an daina samun ta. Naso ne dama in rarrashe ta akan maganar auren ka da Hauwa.
Ina fatan ka lallashe ta da kyau Sarham, ka san mu mata a irin wannan lokacin lallashinku da hakurinku da juriyar ku kan canjin halinmu da dabi’unmu kowanne iri ne kadai muke bukata, ka yi hakuri da dukkansu, ka kuma zamo mai adalci a tsakaninsu.
Kada ka kara fada min wai dalili ne yasa ka auri Hauwa, raina baci yake yi".
Mama ta dade tana yi masa nasiha mai ratsa jiki da bargo, akan zama da mata biyu, sannan suka yi sallama ta bi bayan Abba. Shi kuma har zai wuce dakinsa sai kuma ya taka zuwa dakin Sumayyah don ya yi wa Hauwa sai da safe, ya kuma ga halin da ta ke ciki, ya san har yanzu tana nan cikin kukan nata na shagwabar an rabo ta da Inna.
Amma ga mamakinsa a kan stool din madubi ya same ta cikin farar rigar barci mai kyan gaske wadda Sumayyah ta bata ta saka, ta dau wanka tayi wani irin fresh da ita, bai taba ganin ta zahirin irin yau ba da tsabar kuruciyarta ta ‘teenager’ data fito fili, sannan bai tsammaci wannan yanayin a tare da ita ba, dakin sai kamshin amarci mai dadi da sanyi yakeyi, kanta da ya sha ‘weeving’ yiri-yiri babu kallabi, ta gama shafa lotion wanda ya sa fatarta yin taushi sosai. Tana daga kan stool Sumayyah na daga gefen gado suna ta hira suna dariya, fararen hakoranta a warwaje kamar mai tallan sensodyne.
Bai taba ganin Hauwa-Kulu cikin kyakkyawan yanayi da kyakkyawar shiga irin wanda ya ganta ciki a yanzu ba.
Ita Sumayyah ta ga shigowarshi, da yake kofa take fuskanta, amma ba ta fada wa Hauwa ba. A lokacin Hauwa na tambayar Sumayyah, "Karatun likitanci nada wahala?”
Sumayyah ta dubeshi tayi murmushi mai sauti ya kasha mata ido, ta ce mata, "Aah babu, ba wani wahala".
Sai ta ce, "Kin ga da idanuna ba su rufe ba, da a bude suke kamar na kowa har yanzu, nima da irin karatun Yayanki zan yi, Ina sha'awar inga ana aikin fidar ido, kasancewar sa wani kwayar halitta mafi hatsari da muhimmanci ga jikin dan adam, ba ki san yadda likitoci suke burge ni ba, shi ya sa har wasu lokutan nake DAKACEN ina ma… in ga Yaya Sarham! Inama in ganshi cikin kwayar idona, in ga yadda kamanninsa na zahiri suke? Ko daidai suke da yadda nake kintata shi ina fasalta shi a raina?
Anti Sumayyah wallahi haka kawai kyawawan kalamansa SUNA BURGENI!!!”.
Sarham sai kawai ya juya da baya cikin mutuwar jiki, tare da yi wa Sumayyah alamar kar ta ce ya shigo.
Yana shirin kwanciya kamar yadda ya saba ya samu kansa da yin addu'ar Allah ya cika wa Hauwa burinta watarana ta sanya idanunta cikin nasa, ya gaya matai do da ido shima tana burge shi”.
Yana addu’ar Allah ya bashi ikon yi mata adalci ta kowanne bangare, ya kuma ba shi tsawon ran da zai sauke duk alkawururruka da kudirin da ya dauka a kan rayuwarta na zame mata PACESETTER.
Sai washegari ya shiga dakin Sumayyah suka gaisa, ya baiwa Sumayyah kwalin waya, ya ce, ta hada wa Hauwa.
Sumayyah har ta fi Hauwan murnar mallakar tsaleliyar wayar nan. Nan da nan ta hada ta, ta saka layin da ya hado da shi na mtn, ta saka a caji tana gaya wa Hauwa sunan wayar da Bhaiya ta saya mata.
Hauwa wadda kanta ke sunkuye tun shigowarsa dakin, tana iya jin idanunsa all over her, da kyar ta iya furta masa kalmar godiyarta gajeriya.
A lokacin bata dade da yin wanka ba. Mama ta kawo shadda dinkakkiya dakakkiya 'yar Mali ta bata ta sanya, shaddar orange colour, tasa ta yi sharr da ita, amarya sosai mai jini a jika. Sumayyah ta fice daga dakin don dai ta ba su wuri su gaisa, ganin cewa tun jiya basu gaisa ba.
Sarham ya tako ya zauna a gefen Hauwa. Dab da kafadunta. Hauwa na iya jin sanda ya zauna din, da kamshin balaraben turarensa 'sandalia' daya nasheta, ta lumshe ido ba shiri, inama zata gan shi a lokacin, hakika da ta kara godewa Allah a bisa ni'imar da yayi mata na bata Dr. Sarham Abbas a matsayin mijinta kuma abokin rayuwar ta na har karshen rayuwa. Wani sassaukan yadi ya sanya mai matukar tsada ruwan Madara shara-shara da shi har kana iya hango sabuwar farar singlet dinsa dake ciki. Sannan yadin baida nauyi ko kadan sai tsada. Hannun Dr. Sarham Hauwa ta ji ya ratsa a cikin hannunta na dama for the first time a rayuwarsu, wanda hakan yasa ta dan firgita, tsigogin jikinsu gaba daya suka tashi a lokaci guda. Sarham ya yi crossing fingers nashi da na Hauwa tareda rufesu da daya hannun nasa yana murmushi ya ce,
“Maijidda matar likita ina kwana? Yaya kuma kwanan bakunta? Ina fatan kinyi barci mai ni'ima kin warware gajiya”.
Hauwa, wadda yau ta ji duk duniya ba wanda ta ke jin kunya sai Dr. Sarham, kasa amsawa ta yi, gashi yana kara karfin matsar da yayiwa hannunta da nasa hannun mai tsananin taushi, ya ce, "Ina gaishe ki Maiji....”.
Ta dan motsa baki cikin dabarar son janye hannunta daga nasa, sabida kasalar da taushin hannun nasa ke saukar mata, da kyar ta iya ta ce,
"Ni ya kamata in gaishe ka ai Yaya Sarham, ina kwana?"
Bai yarda ya saki hannun nata ba duk da yadda ta ke son zameshi cikin dabara, ya ce,
"Na kwana ina tunanin cikin halin da ki ka kwana yau ba tare da Inna ba.
Na fi ki damuwa da rabuwa da Inna, amma wannan ita ce 'reality' din kowacce diya mace, cewa ita din yar gidan wasu ce kin ji, mai lafiya ko mara lafiya in dai ta isa aure to Allah ya yi umarnin iyayenta su yi mata, ko a birnin Sin ne, so ko ba ni ba ki sa a ranki wai don rashin ido ba za ki dauwama a gaban Inna ba matukar Allah ya kawo miki mijin da ya dace dake yake kuma son ki tsakani da Allah, amma banda Jamilu, ba don komai ba sai don kwanciyar hankalin ki da zaman lafiyan iyayen ki da hakan zai wargaza. Ki yi hakuri kin ji???
Ni na san na saka gaggawa a cikin aurenmu, amma dai ai ba yau muka san juna ba ko Maijidda, kuma in har na kara jan lokaci bayan wanda Ubangiji ya ara min, Jamilu ba zai rabu da ke ba, da gaske yake.
Ni kuma ba zan taba barin wani abu ya kara taba zuciyar Inna ba da izinin Allah, balle aurenki da Jamilu wanda shi ne babban tashin hankalinta”.
Hauwa bata san sanda ta katse Sarham ba, cikin rishin kukan da ya taso mata.
"....... Yaya Sarham, kana kokarin gaya min ne cewa saboda Inna ka aure ni kai, saboda kwanciyar hankalinta daga Baba Zakari, don ka raba ni da Yaya Jamilu, amma ba don kai a karan_kanka kana sona ba ko?"
Maganar Hauwa ta firgita Sarham yadda bai yi zato ba, don a tunaninsa Hauwa ba ta ma san wani abu wai shi SO ba. kuma bata da tsinkaye mai zurfin haka.
Shirun da ya yi ne ya ba ta damar zare hannunta daga cikin nasa a hankali, tareda matsawa gefe daga jikin sa, ta ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login