Showing 27001 words to 30000 words out of 30501 words
irin wanda baki ba zai iya furtawa ba. Sannan babu kalaman da za su isa godewa. Ina rokon Ubangijiya fini godewa.
Idan har na yi fushi da kai a kan wani abu Yaya Sarham, to ya zama rashin adalci da butulci irinna an adam, domin ka yi min komai and beyond, da ya cancanci in gode maka ba inyi fushi da kai ba.
Kawai in na tuna cewa ni ba SO ne ya sa ka aure ni ba, tausayi ne da son kyautata rayuwata sai in ji komai na duniya ya daina yi min dadi…, burikana na shekara daa shekaru sai inji sun fita kaina”.
Sarham ya ce cikin daga murya, “Shi tausayin ba SO ne yake yin sanadinsa ba?
Ko kuwa in tausayi ne ashe duk masu lalurar ido na aibitin Murtala na Kano dana yiwa aikin ido sai in bisu in aure su, bana son ki zan kawo ki cikin gidanmu, in hada ki cikin iyalina Maijidda?
Bana sonki zan miki takwara da diyar cikina? Tun ma baki zama matata ba?”
Kawai sai Hauwa ta ji kukan dadi ya kwace mata, ta sa tafukanta ta rufe fuskarta tana yinsa riiiii-riiiii.
A hakan ba ta yi aune ba ta ji numfashin Sarham daf da fuskarta, ya ce, “kin yi kankanta in tsaya ina gaya miki abinda kike son ji daga gareni. Amma duk da haka ina so ki saka a ranki, ba wai furta kalmar so ne kadai yake sakawa a yi aure ba, sannan aure ba ya taba samun muhalli a inda babu so. Ko na ce, ko ban ce ba Maijiddah, ba zan aure ki alhalin ba ki da muhalli ko yaya a zuciyata ba.
Da wannan nake cewa. Maijiddah ki yi hakuri ki bani lokaci, ki taya ni mu taru ni dake mu raini wannan burbushin SOn, wanda dalilai da hujjoji suka fi shi karfi, daga ni har ke ba mu san me gobe za ta haifar ba, Allah daya halicce mu shi kadai ya san sirrin da ya boye a tsakaninmu.
Ina fatan ki taya ni rainon wannan burbushin son, har zuwa sanda zai girma ya zama mashahuri, abin buga misali beyond our expectations”.
Sarham ya yi shiru yana nazarinta hawaye sun ki tsayawa a idanunta, amma ta kare fuskarta da tafukanta. Ta sani cikin abubuwan da yake fada duka babu karya, gaskiyar zuciyarsa yake gaya mata,
“suyi nurturing dan burbushin son tare har ya girma ya zama mashahuri”.
Wanda ita kuma gaskiyar ce ta ke mata daci, ta cewa ita an aure ta ne ba don so ba, sai don wasu dalilai masu karfi.
Sarham ya fada ya maimaita a kunnenta, ya fada har a bayan idon ta, wanda shi a wurinsa ba komai ba ne face gaskiyar da ke zuciyarsa kasancewarsa frank person, kuma a wurinsa ya girma da yin karya, wai don ya farantawa mace.
Bai sani ba, ita wannan gaskiyar bakanta shi ta ke yi a zuciyarta, har gara ya barwa ransa ita, koda kuwa bai yi mata irin zancen da ta ke son ji din ba kamar na Jamilu mai nuna tsantsar tsagwaron soyayyah muraran.
Duk yadda Dr. Sarham ya so su yi kyakkyawar sallama abu ya faskara, shi kuma yana jin nauyi da pride din ya rungumo ta cikin jikinsa ya lallashe ta irin lallashin da yake yiwa Madina in ya bata mata rai, Madinah ai sa’arsa ce, ta kuma mallaki hankalinta, sannan soyayyar ce zallah ta hada su. A wautarsa Hauwa-Kulu ba ta san da irin wannan duniyar ba, ba kuma zai koyar da ita ba balle har a zo gejin da wani abu makamancin nasa da Madinah zai samu mabubbuga tsakaninsa da Hauwa.
Hauwa za ta ci gaba da cin matsayinta na tudu biyu, na kanwarsa kuma matarsa.
Yayin da Madina ke kan tudun muntsira na masoyiyar romansiyya.
Matsayin da ya bata na kanwa kuwa ai ya fi na masoyiyar soyayya, tunda matsayin kanwar jini ya ba ta, kuma dai Hausawa suka ce jini ya fi ruwa kauri, wato soyayyar jini da yake yi wa Hauwa-Kulu kaurin ta yafi na romantic soyayya tasiri, irin wadda ke tsakaninsa da Madinah.
Sallamar dai ta ki dadi tsakanin Sarham da Hauwa, ta ki kula shi, ta ki daina kuka. Ta ki yafe furucinsa. Har cewa tayi cikin subutar baki.
"Ita da ma ya barta tare da su Inna sun tafi Ghana, ya fi mata alkhairi a kan wanan kaddararren auren nasa, (wadannan kalaman da ya gama gaya mata yanzu sun mata da banzan ciwo), na cewa da yayi ta taya shi su yi nurturing ‘yar burbushin soyayyar da yake yi mata, su girmar da ita tare, har su samu ta zama mashahuriya, wanda in anbi salsala kalamansa na nufin ba ta da muhallin soyayya a zuciyarsa.
Wannan ya kara tunzura kuka da rikicin Hauwa. Abinda bata sani ba harda na kewar tafiyarsa.
Abin da ba ya son yi wato rungumar Hauwa ya lallasheta shi ya yi a bisa dole, jikinsa yana ’yar kyarma ya hade jikinsa da nata wuri guda suka dunkule cikin ‘tight hug’. Hauwa tana sakin kuka a hankali bata daina ba, wani abu tamkar 'electrical shocking' ya bakunci jiki da zuciyar Hauwa, dana Sarham as well, ta yi kokarin janye jikinta daga cikin nasa, amma yaki saki, ya tallafo fuskarta da hannu daya, kallon hawayen da ke bilbila daga kyawawan idanunta suna sauka akan kundukukinta sumul sumul dashi kawai Sarham ke yi, kafin ya kai dan yatsansa manuni yana kawar dasu one by one daga kan kuncinta, sai kuma yasa fuskarsa a cikin tafukan Hauwa, wato ya tallafi fuskar shi da hannuwanta biyu ya sanya fuskarsa a tsakiyar tafukanta, murya na dan rawa kamar yadda ilahirin jikinsa ke shaking and vibrating da ya hadu dana Hauwa, Sarham ya ce.
“Zan tafi Hauwa-Jiddah, sai nazo, ban san yaushe zan samu dawowa ba. Anyway ki kula da kanki, ki kula da ibada kin ji?”
Kai kawai ta gyada masa don dai ta samu freedom daga rikon kazar kukun da yayi mata, zai sumbaci tafukanta da ke kan sajensa, idanunsa a lumshe, Hauwa kamar ta san hakan zata faru ta yi maza ta janye hannayenta daga sajen fuskarsa, tsigar jikinta na tashi amma a wannan lokacin ji take bata bukatar irin wannan rarrashin yaje can yayiwa matar so.
Duk yadda Sarham yake so sallamar tayi dadi da armashi tsakaninsa da Hauwa, ta yadda bazai tafi tana ajje dashi da kalamansa a ranta ba, hakan bata samu ba, Hauwa ta dauki fushi mai ban mamaki wanda shi a iya saninsa bai da dalili. Meye laifi don ya gaya mata hakikanin gaskiyar da ke zuciyarsa cewa ba soyayya ce ta sa ya aure ta ba? Dalili ne, kuma har gobe zai kara maimaitawa dalili ne mai kwari da karfi ya yi mujazar auren nasu. Ta tayashi su raini wannan dalilin har ya koma ingantaccen SO, Shima zai so hakan. Ko don ya zamo mai adalci tsakanin ta da Madinah. Ya gama gane Hauwa so ta ke ya zauna yana mata karerayin samari ‘yan I love you? Ya karkace kai yana ce mata ‘I can’t do without you, bayan Madinah ce kawai ‘he can't do without’.
A ganinsa ya wuce wannan ‘stage’ din tun a can baya, kuma ba zai iya maimaita shi da kowacce mace a yanzu ba, bayan Madinah.
Ya tsura ma Hauwa ido daga tsaye, hannayensa biyu zube cikin aljihunsa, ya kasa fita daga dakin, kalma kuma ta kare masa don ta ki tsaida hawayen idanunta, kukan da bai ga dalilin yin sa ba, don ba za ta ce don kewarsa ta ke yin shi ba. Don yana da tabbacin Hauwa bata wani saka shi a ranta ba.
Lokaci na ta tafiya, Hauwa na sheshsheka, wadda ke saka Sarham tsuma daga tsaye, kukan nata na huda shi sosai, ya kasa fita daga dakin har sai da Sumayyah ta dawo, ba ta san cewa har lokacin yana dakin ba.
Ta yi niyyar komawa da baya ganin yanayin da suke ciki, ya ce murya na sarkewa “Summy, kina iya shigowa, wucewa zan yi in kwanta, kin san gobe asubanci za mu yi.
Ina fatan kin sayo ma Maijidda duk abin da za ta bukata din wanda zai yi mata akalla watanni uku?”
Sumayyah ta idasa shigowa dakin cikin sanyin jiki na yanayi mara dadin data gansu aciki, ta ce, “Ba abin da ban sayo mata ba, duk da cewa akwai komai a cikin akwatin lefenta, irin su pad, macleans da listerine na karo mata da sauran tarkacen da babu cikin akwatunan".
Sarham ya soma taku daya, biyu zai bar dakin har zuwa lokacin hannayensa biyu cikin aljihunsa ya ce, “Maijidda sai mun yi waya, take care”. Da wani irin karfin hali ya bar dakin ba tareda ya jira jin amsarta ba.
Hauwa ta ce, “Allah ya tsare, Allah ya sauke ku lafiya”.
Wani irin tausayi mai tsanani ya kama Sumayyah ganin cewa, ai Sarham ba irin sallamar da ya dace a ce ya yi da Hauwa ba kenan, za ta iya rantsewa in Madina zai tafi ya bari a wata kasa ba irin sallamar da za ta samu kenan ba.
A halittarsa ‘he's very romantic’ ga matar aurensa. Me yasa yake ja baya da Hauwa?
Ta hade rai sosai cikin taya Hauwa kishi, ta yi kwafa ta bi shi da harara yana ficewa.
Sumayyah ta zauna a gefen Hauwa wadda ke gyara filo don ta kwanta, ta ce, “Aunty Hauwa saboda Allah haka ake sallama da miji ana cin magani ana faman sharar hawaye da sharbe majina?
Da me zai tuna ki ya yi dokin sake zuwa gare ki?
Hauwa sai fa kin sake lale, in ba haka ba wallahi za su kai ki su baro a ‘yar jiran dakinsu.
Ki tashi ki kwato wa kanki ‘YANCIN SO, dana lura anaso a take miki da gangan, don ni ban ga soyayya a wannan auren naku ba, ya fi kama da zallar ‘yan uwantaka.
Ni ko yadda na ga ana magana da Madinah ana kashe murya da Ido ba haka na ga ana magana da ke ba.
Ke ni fa bana karbar ‘defeat’ na a so wata mace ‘yar uwata fiye da yadda za a so ni, don ban yarda ta fi ni da komai ba, dukkanmu mata ne a halitta, sai dai a ce kowacce da kalar tata fatar. Amma da irin kissar ta, na rantse mai mata irin Madinah, sai kin yi da gaske kafin ki samu gurbin da ya dace da ke a hannunsa, don wallahi Madina ta gama shan gaban Bhaiya daga sama har kasa, har kudu da arewa”.
Hauwa ta ce, “Aunty Sumayyah kenan, ta ya ya zan zo in same shi da matarsa in ce lallai sai na hada kafada da ita a zuciyarsa?
Nasan irin gwagwarmayar da sukayi tare kafin su kai ga wannan matakin? Kamar zan fi yarda da nasa ‘perception’ din fiyeda naki, da yace in taya shi mu raini nawa son har in samu ya girma a zuciyar sa.
Soyayyah ta Allah ce, ba’a mata dole, shi yake sanya ta a zuciyar da ya ga dama, ni ba wani ‘effort’ da zan yi don a so ni, ban da maida al’amurana ga Allah da yin abin da zai amfane ni duniya da lahira.
Ban shigo rayuwarsu don in hada kafada da ita a komai ba kamar yadda ban taba tsarawa kaina aure da mai mata ba. na shigo ne ta hanyar kaddarata.
To amma ya zanyi tunda Yayanki Allah ya rubuta min? Kuma shi iyayena suka zaba min? Na shigo gidansa ne da sunan shi ne mijin da Allah ya zabar min, kaddara kuma ta rubuta min, ba ruwana da irin mu’amalar da ke tsakaninsa da matarsa”.
A takaice Sumayyah ta gama gane Hauwa, sune irin matan da ake kira ‘naive and innocent’ a zamantakewar aure. Ba ta da wani ‘proper experience’ na zama da miji balle da kishiya, don haka duk yadda za ta kwatanta mata ta tashi tsaye ta kwaci soyayya a zuciyar Sarham ba za ta gane komai ba.
Ita kuma sai inda karfinta ya kare wajen kwato wa Hauwa ‘yancin so, sannu-sannu ba ta hana zuwa aka ce sai dai a dade ba a je ba. An yi mai wuyar ai tunda har Hauwa ta amshi sadakin Sarham, shi kuma ya amince ta amsa sunan matarsa, har ya bata dafin Mrs. Shanono.
Babban abin da ya taba zuciyar Sumayyah ko irin dokin nan na amarci babu a tare da shi, a tsayin zamansu da Hauwa za ta iya tuna ko sau nawa ya kira ta a waya daga sanda ya mallaka mata wayar hannu. Amma Madinah fa?
Sanda aka kawo ta gidan bata manta ba Sarham baya awanni biyu bai kira ta a waya ba, ga wani munafikin ‘midnight’ call da suke yi kullum dana yammaci da yake tafiya bakin layinsu yayi duk don tana cikin gidansu ba tare dashi ba, har sai da suka bar gidan zuwa inda suka fito, sannan suka samu lafiyar su.
Duk wannan ba ya gaban Hauwa, ba don komai ba sai don cewa Sarham bai koya wa Hauwa soyayya ba, bai bi matakan da suka dace wajen aurenta ba, don ko tadi bai taba zuwa officially ba, kalmar so ba ta taba giftawa tsakaninsu kamin su yi aure ba, haka ba ya jin wai a gaba za ta gifta. Duk abin da yake nema a diya mace yana da shi a Madina, don haka aurensa da Hauwa ba zai daina kiransa da auren dalilai da sanadi masu yawa ba.
A daren Sumayyah ta koya wa Hauwa amfani da abubuwa na tsaftace jiki kamar su mouth wash da mouth freshner, wanka da bath gel maimakon sabulu. Turarukan lefenta ta jere mata su a kan madubinta, ta nuna mata yadda za ta dinga amfani da komai har abubuwan toiletries din duk ta koya mata amfani da su.
Tun a daren suka yi sallama da Sumayya cike da kewar juna, haka Hauwa ta kwana cikin sake-saken yadda rayuwa za ta kasance mata a gidan iyayen mijinta babu mijin, babu Sumayya mai debe mata kewar Inna.
Sarham da kanwarsa Sumayyah, sun tashi zuwa Jiddah a washegari. Gida ya rage daga Mama sai surukarta Hauwa da yarinyar da aka dauko mata daga Shanono.
Hauwa na jin dadin zama da Mardiyya, nan kasan kafafun gadonta Mardiyya ke saka katifarta ta kwanta. Duk wani motsi da Hauwa ta yi za ka ga Mardiyya ta mike tana tambaya, “Aunty Hauwa kina son wani abu ne? ko bandaki za ki shiga in taimaka miki?”
In bandaki za ta shiga sai ta ce, “Ai ba sai kin raka ni ba Mardiyya, ko ma barcinki zan iya kai kaina”.
Mama koyaushe in ta dawo aiki sai ta fara shigowa dakin da Hauwa ta ke, ta zauna su yi hira, tun Hauwa ba ta sakewa har ta gane Mama fa ba ta surukuta da ita. In Abba Prof ya dawo kullum Mama cewa ta ke, Mardiyya ta fito da Antinta falo ta ji labaran tara, su daina kulewa a daki su kadai.
Surayyah tuni ta bar musu gidan, ta koma gidan Hajiyar Gadon Kaya.
A kullum abincin Hauwa na musamman Mama ke sa wa a shirya mata, kuma sai ta zabi abin da za a dafa mata. Mama ba ta dawowa gida ba tare da ta kawo wa Hauwa tsaraba ba, musamman da ta gane tana da son cin gugguru (popcorn) kullum sai ta sawo mata shi.
Kafin ka ce me ye wannan, wata irin shakuwa irin ta Uwa da Da mai ban mamaki da ban sha'awa ta samu muhalli tsakanin Mama Mai Shari'a da surukarta Hauwa.
A wasu lokutan Barr. Haj. Maimuna Shanono in tana hira da kawayenta na jiki su Barr. Hannatu a chamber dinsu, za ka ji Mama tana fadin musu, “ita kam yanzu ne ta san Sarham ya yi aure daidai da shi. Inda zai fada aji, inda ba'a raina arzikin shi ba. Yanzu ne ta san ta yi surukar da in ta ce ta yi kaza za ta yi ba girman kai ba dagun kai, ita yanzu ta san ta yi suruka da take da ‘high influence’ a kanta".
Kuma in za ka tsire ta ka ce meye aibun Madinah Sorondinki, kome tayi mata da har gobe bata bata yardarta da amincewarta 100% ba, kamar yadda ta bai wa Hauwa-Kulu farad daya, zaka tarar Mama ba ta da amsar ba ka.
Bata da wata hujja kwakkwara ta son Hauwa fiyeda Madina. Daidai gwargwado Madina ba ta gaza da su ba, ko bata musu biyayya ko tana da wani nakasu da za'a iya bugun gaba a soketa da shi ba, illa hakan halin Dan Adam yake musamman a inda soyayyar miji ta kasa boyuwa akan mace, wasu iyayen mijin nada halin dan Adamtaka in ‘ya’yansu na mutuwar son matansu, to su kuma za ka samu ko me matar za ta yi ba zai burge su ba. Kuma a kasan ransu suna jin zafinta, babu