Showing 15001 words to 18000 words out of 19751 words

Chapter 6 - BINTU DIYAR BAYI Book 1

13 Aug 2024

1770

murmushi gami da shafa gashin baki ya dubi bayin sa tare da tambayar
‘’ gide wagga bayin wani Masarauta ne? me ya kawo su Masarautar mu?’’
Zu6ewa k’asa su ka yi, sa’annan d’aya daga cikin bayin ya amsa masa da

‘’bayin Masarautar Sa’ayrasa ne ran Yarima ya dad’e, hallo ina da labarin su su ka rako Gimbiya Fatima d’iyar Sarki Inuwa na S’ayrasa a matsayin bayi na ta....’’
Cike da gamsuwa Yarima Sadauki ya ke gyad’a kai, kafin daga bisani ya ce
‘’doguwar mai tafiya uwa d’iyar Saraki, ita na ke da muradin gani, hallo a duk in da ta ke a mata iso zuwa ga turaka ta’’

‘’an gama ran Yarima Sadauki ya dad’e, yo to ko Gimbiya Fatima ka ke da muradin ganin ai dole ta taho gare ka bare kuma baiwar ta, babba gare ka Saudakin Sadaukai, ba hau da wani ba sauke wani, Sadauki maida garin wani kango’’
Ya na mai hura hanci cike da sarauta da tak’ama ya wuce gaba, yayinda bayi su ka tashi su na mai rufa masa baya ba kuma su fasa fasa masa kirari ba.





������������
[16:08, 11/09/2017] hm: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣4⃣


Sidiya ce...✍��



Barde kuwa a nasa 6angaran komawar sa turakar sa har da amai. Hankanlin sa be kwanta ba sai da ya amayar da dukkanin abun da ke cikin sa. Abun da ya ke bashi mamaki be wuce yanda yaji dan adam ya na wari kamar na mushe ko kuwa ja6a ba, daga ganin shigar ta ya san baiwa ce sai dai ba irin kalar shigar bayin Fabarusa ba ne, ko koma baiwar wata masarauta ce dole ya sa a nemo masa ita a sallame ta daga cikin fada ta je ta nemi magani gyambon da ke jikin ta idan dai ba so ake kar shi har lahira ba. Da wannan ya sami mafakar rashin zuwa ya ga amaryar sa, yayi kwanciyar sa abun sa.



Washagari da sassafe Jakadiya ta je masa da karin kumallo na musammam bisa ga umarnin Sarki Abdulrahman. Wanda Yarima Barde ya san ba komai ba ne illa tambayar
‘’shin ka je wa matar ka?’’
Saboda haka ko da Jakadiya ta tashi tafiya sai Yarima Barde ya bata sak’o zuwa ga Gimbiya Fatima, ya na mai fad’in
‘’a shedawa Gimbiya Fatima, bayan gaisuwa da fatan ta na lafiya, ta saurari zuwan mu bayan fad’uwar rana, kada ta tsawaita buri ba ma buk’atar komai daga gare ta’’

Kalaman da Barde ya k’arasa da su be hana Jakadiya rangwad’a gud’a ba, dan kuwa ta san tabbas idan aka juri kai zuga gabas wata ran ta zo da ruwa. Ai kuwa ko da sak’on ziyarar Barde ya riski su Bintu, nan fa Bintu ta ga ta kan ta dan kuwa tun da safiyar Manman Cangwai ta shiga gyara ta da su turarukan wuta, tsimi ne da cukwid’i kai har da wanda ma ba a sa ta ba, domin fa Maman Cangwai ita ta na da nata manufar na musammam cikin ran ta na game da Bintu, sai dai sa6anin sauran ita kad’ai ke san Bintu da alkhairi.

In dan ban da fad’uwar gaba babu abin da Bintu ta ke, bini bini ta ke duba lokaci ta na mai fargabar fad’uwar rana da abun da za ta zo mata da shi na daga ziyarar Yariman Fabarusa. Haka kuma kaman nin wannan da ta gani cikin lambu be dena mata gizo ba, da za ta sami dama ko shakka babu ta na komawa cikin lambu ko Allah ya sa ya k’ara bayyana a gare ta.
Yarima Barde ma cikin zulumin had'u da k’anwar Gimbiya K’amariyya a matsayin matar shi ya wuni. Rana na fad’uwa ya shirya cikin shigar sa na saraki, biye da shi amintaccan bawan sa ne wanda ake kira Bakar namba, su ka nufi 6angaran su Bintu.

Lifaya fara kyal Bintu ta d’aura bayan ta sha turaruka na hayaki da humra. Ta na daga zaune bisa gado gaban ta na fad’uwa tsabagen fargaba ji ta ke kamar ta zura a guje. Maman Cangwai ce ta sa ta a gaba ta na ta jera mata bayanai tare da kashedi, fad’i ta ke

‘’kin san dai ke d’iyar Sarki ce ba d'iyar bayi ba, ki kasance mai rowar muryar ki a gare shi, ban da yawan surutu in dai ba ya zama dole ba, ki kasance gwanar iya kalamai duk san da zaki bud’i baki ki yi furuci, ki tabbatar kin tauna kin juya kan ta hito daga leban ki.........’’

Daga waje tun isowar Yarima 6angaran na Bintu warin nan da ya ji a lambu ya fara bakuntar hancin sa, hankalin sa ne ya fara tashi yayinda ya ji bugun zuciyar sa na dad’a k'aruwa. Cikin wannan hali ya yi tsaye bakin k’ofar falon Bintu, yayinda bak’ar namba ya shiga kwad'a sallama.
Ladiyo na mai amsa sallamar ta fito, ganin wanda ke gaban ta tsaye ta yi ta na duban sa. Sanye ya ke cikin fara Jabba wanda aka mata ado da koran zare, bisa babban rigar sa ce na dokakkiyar shadda fara kyal sai d'aukan ido ya ke. Haka rawanin da ke bisa kan sa irin na buzaye zuwa huffin da ke sanye cikin k’afafun sa farare ne kyal kai ka ce shirya shi aka yi.
Ganin ta saki la66a da su ga66a ta na duban Barde, ba ta da niyar motsawa bare ta kai gaisuwar ta gare shi, ya sanya Bakar numba fad'in
‘’hattara d’iyar talakawa! Yarima Barden Mahadi shi an gaban ki’’

Tuni Ladiyo ta zu6e k’asa jin buzun nan dai ba kowa ba ne illa mijin Bintu, fad’i ta ke
‘’tuba na ke Yarima, Allah ya huci ran Yarima, babban Barde babban bako’’

Shi kuwa Barde ganin tufar jikin ta ne ya dad’a d’aga masa hankali ba wai yanda ta masa ba, dan kuwa tabbasa wannan baiwar mai wari da yayi arba da ita cikin lambu a daran jiya irin shigar ta kenan. Idan kuwa haka ne to lalle d’aya daga cikin bayin matar da aka aura masa ne ke wannan mugun warin da ke neman halaka shi.
Bakar numba ne ya amsa da
‘’an gaishe ki d’iyar talakawa, ki shedawa Gimbiya Fatima Yarima Barde na neman iso gare ta’’

Da sauri Ladiyo ta tashi har tana hard’ewa, yayinda ta ke fad’in
‘’an gama ran Yarima ya dad’e’’
Ciki ta shige jiki na rawa, ta tadda bayin da ke hidima cikin falo wanda k'atuwar muryar Bakar numba ya sanar mu su da isowar Barde, kowannan su ya nutsu jere cikin sahu, musammam bayin Fabarusa wanda dama sun fi na Sa’ayrsa sanin darajar Barde. Kai tsaye cikin d’akin Bintu Ladiyo ta shige ta na mai zubewa k’asa gaban Bintu dan kuwa ganin Barde ya sa ta tsorata da sa’a tare da nasarar da ke tattare da d’iyar bayi
‘’ran Gimbiya ya dad’e, Yarima Barde ya iso ya na mai neman iso gare ki Gimbiya’’

������������
[16:08, 11/09/2017] hm: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣5⃣


Sidiya ce...✍��



Jin haka hankalin Bintu ya tashi, cike da fargaba ta kai duban ta ga Maman Cangwai, wacce ta gane halin da Bintu ta ke ciki kana ta ce

‘’ki nuna masa hanya ya iso gare ta, ni da sauran bayi za mu tsaya daga wancan d’aki, ke kuma Ladiyo da ke ku tsaya daga wajen kofa kafin Gimbiya ta sallame ki’’

Cikin rawan jiki Ladiyo ta tashi ta na mai fad’in
‘’an gama ran gimbiya shi dad’e’’
Ko da ta koma gun su Yarima Barde, Maman Cangwai ce ta fito da kan ta ta sallami sauran bayi zuwa ga d'ayan d’akin, duk da kuwa bayin Sa'ayrasa ba haka su ka so ba, su ma dai so suke su ga Yarima Barden nan da jama’a ke yawan ambaton sa wajan kyawu. Ladiyo a gaba, biye da Ita Yarima Barde ne in da shi kuma Bakar numb ya tsaya daga waje, su ka shigo falon Bintu.
Warin nan da ke d’aga masa hankali shi ya ke bunk’asa ya na dad’a bakuntar hancin shi duk sanda ya d'aga k’afa ya sauke a falon. Isar su tsakiyar falon Yarima Barde ya tsaya cak, ga mamakin Ladiyo ji ta ya furta

‘’gide bayi masu shiga irin ta ki nawa ne cikin wanga turaka?’’
Ladiyo na mai susa k’yeya yayinda ta shiga kame kame ta cikin fargabar kar dai ya gane ita ce mai bin bayan sa cikin lambu ta yi saurin fad’in
‘’iye na’am? Mu na da d’an dama ran Yarima Barde ya dad’e, wagga shiga ita an shigar bayin Sa’ayrasa, dukkanin mu wagga shiga mu ka yi Allah shi da ran Yarima’’
Yarima Barde na mai duban ta ya ke d’an tuntuntuni, dan kuwa ko shakka babu ya san wagga baiwa ta gaban sa ba ita ce mai warin da ya gani a lambu jiya ba, duk da dai be ga fuskar waccan da kyau ba amma ya san a jiki waccan tafi domin kuwa Ladiyo irin k’ananan matan nan ne. Shi kuma a yanzu be da buri da ya wuce ya gano baiwar nan da ke wari ko ya sami lafiya domin kuwa muddun ta na nan ba zai iya zama ko da na minti hud’u a turakar amaryar ta sa ba, abun mamaki shi ne ta yaya bayin Gimbiya kamar Fatima za su na zama da wari har haka ba tare da ta d'auki mataki ba? Hakan ke tabbatar masa da k'azantar da ke tattare da ita.
Juyawa yayi ba tare da ya sake tankawa Ladiyo ba, wacce ta yi kasake ta na duban sa ta rasa yanda za ta yi da ran ta, ganin dai da gaske ficewar ya ke ta bi bayan sa da sauri, amma ina kan ta cima su tuni ya d’au hanya, Bakar numba biye da shi. Da gudun ta ta dawo d’akin Bintu in da ta zu6e k’asa ta na kuka fad’i ta ke
‘’ki min rai Gimbiya, kwankwatsi ban san shi an Yarima Barde ba, aradu da na san shi na da ban bi bayan shi ba, in k’arya na ka yi aratta kashe ni’’

Cike da mamaki Bintu ta yane lifaya da ta rufe fuskar ta, tambaya ta ke

‘’gide lafiya? Yo to minana? Mi Yariman yay mi ki da har ya sanya ki kuka Ladiyo? Ina Yariman ya ke?’’

Ladiyo wacce duk a zatan ta Yarima Barde ya gano ta ne ran sa ya 6aci har ya juya ya fasa ganin Bintu ta ce

‘’ Yarima Barde ya juya ya koma, ki min rai kar ya sa a tsire ni, ina ni ina lek’en surrun Yarima Barde, ki taimaka ki min rai, wayyo ni Ladiyo sai kuma yanda aka yi da ni d’an daudu a kabari’’

Ganin dai Ladiyo ba ta da niyar bata cikakkiyar amsa ya sanya Bintu tashi ta fita da kan ta, ita ma Ladiyo bayan ta ta biyo wanda kukan ta ya sa sauran bayi fitowa. Maman Cangwai na mai tambayar ko lafiya? Ina Yariman ya ke? shin me ya fito da Bintu daga uwar d’aka ita kuma Ladiyo kukan me ta ke?
Kasa amsa mu su Ladiyo ta yi har sai da Maman Cangwai ta daka mata tsawa sannan ta iya labarta mu su yanda ta bi bayan Yarima Barde zuwa Lambu ba tare da ta fad’i jan Bintu zuwa lambu da ta yi ba, yanzu haka ya gano ita ta ke lek’en asirin sa.

Cikin jimami kowa ya ke duban Ladiyo wacce ta had’a zufa, hawaye da majina. Ita kuwa Bintu waje ta samu ta zauna cikin neman mafita, dan kuwa muddin abun da Ladiyo ta fad’a gaskiya ne, ko shakka babu dole sai an hukun ta ta, lek’en asirin Yarima ba k’aramin laifi ba ne, za a iya amfani da wannan ace so ta ke ta idda wani mugun nufi kan sa ko kuwa dai ta ha’d’a baki da abokan gaba ta na san halaka shi.

Yarima Barde kuwa da fitar sa kai tsaye gun Jakadiya ya nufa. Ya tadda ta bisa sallaya tana lazumi kan ta zo ta shiryawa sarki sauwar dare. Ganin Barde ta san da matsala wanda shi ma be 6oye mata ba ya sheda mata cikin azanci ba tare da ya fayyace mata komai ba.
‘’ya Jakadiya, a had’a fanteka na turaruka, na jiki zuwa na kaya, a aika ga Gimbiyar Sa’ayrasa, a kuma sheda mata Yarima Barde ma’abocin k’amshi da tsafta ne, ta gaggauta sauya gimshikin kusurwar ta’’

Cewar Yarima Barde, wanda ya juya ya tafi ba tare da ya tsaya amsa tambayoyin da Jakadiya ke shirin jera masa ba. Abun da kuwa ya fi d'aure mata kai shi ne fantekar turaren da za a kai, ga kuma batun na Barde na Bintu ta gaggauta sauya gimshikin kusuwar ta, ko shakka babu Barde ya ji wari daga wani 6angare na Bintu ko kuwa bayin da ke tattare da ita.

Ba tare da 6ata lokaci ba Jakadiya ta aikata yanda Barde ya ce. Cikin baitul mali ta shiga, daga cikin daular iyalan Sarki Abdulrahman ta jido turarurruka fanteka guda, cikin bayi ta za6i wacce ta fi tsana sannan ta d'aura mata fanteka ta tere da bata sakon Barde zuwa ga Bintu. Jin sak'on da aka bata sai ga baiwa a k'asa ta na yiwa Jakadiya magiya da kada ta tura ta da wannan mugun aike, amma ina sai ma tafiyar ta yi ta barta ta na share hawaye dan kuwa dai ta ta ce ta same ta kishiya tara rana d’aya.


������������
[16:08, 11/09/2017] hm: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.




1⃣6⃣


Sidiya ce...✍��



Ta na tafe ta na hawaye haka ta isa 6angaran Bintu in da ta tadda Ladiyo zaune gaban Bintu ta sha kuka ta k'oshi, daga gefan Bintu kuwa Maman Cangwai ce zaune a k’asa, d'ayan 6angaran Hansai da lantana ne zaune. Bintu ta sallami dukkanin bayin Fabarusa domin samarwa Ladiyo masalaha.

A gaban Bintu baiwa ta aje fanteka ta na mai rawan jiki, tun gaisuwar da ta kai ga Bintu, bakin ta na motsi amma tsoro da kwarjinin Bintu ya sa ta kasa furta komai. Maman Cangwai na me duban ta ta furta
‘’ke mu ke sauraro ya ke d’iyar Fabarusa....’’
Maimakon Baiwa ta fad’i dalilin zuwan ta da kuma sak’on Barde, sai gani su ka yi ta fashe da kuka ta na mai fad’in
‘’tuba na ke ran Gimbiya ya dad’e, ki min rai na tuba ki rufa min asiri, tuba na ke’’
Nan fa su Ladiyo da lantana su ka shiga kallan kallo cike da mamaki. Bintu ma mamaki ya ne ya lullu6e ta, cikin ba da umarni ta ce da Maman Cangwai ta bud’e fantekar ta ga abun da baiwar ke tafe da shi. Ko da Maman Cangwai ta bud’e fanteka sai da gaban ta ya fad’i ganin turaruka iri daban daban masu yawa ciki. A hankali ta kai kallan ta ga Bintu wacce ita ma ta hango me ke cikin fantekar kafin ta maida kallan ta ga baiwar, kana ta furta
‘’wannan kuma daga ina?’’
Baiwa ba ta fasa hawaye ba ta furta

‘’gide sak’o ne daga Yarima Barde zuwa ga Gimbiya Fatima, hallo ya na mai sheda mata cewar Yarima Barde ma’abocin k’amshi da tsafta ne, ta gaggauta sauya gimshikin kusurwar ta.......’’

Ta k’arasa furucin na ta ne cikin rawan murya. Shiru kake ji babu mahalukin da ya furta komai tsabagen bazata da kalamin baiwar ya mu su, babu shakka Barde na me shedawa Bintu wani abu daga 6angaran ta ya na wari duk da dai be fayyace mata ko menene ba, wanda turo fantekar turaren da yayi ba k'aramin cin fuska a gare ta ba ne, ba dan ma an riga an d’aura mu su aure ba da hakan daidai ya ke da ya ce ya fasa auren ta saboda wari da ya ji na daga wani 6angare da ya shafe ta.
Sai a sannan Maman Cangwai ta gane kukan da baiwa ta ke, dan kuwa a k’aida ya zama dole Bintu ta hukunta ta bisa ga sak’on cin fuska da ta iya duban tsabar idanun Bintu ta sheda mata, in kuwa ta yi sake ta rabu da ita salin alin, toh tabbas ta siyawa kan ta raini daga kan jama’ar fada har izuwa sauran bayin na fada babu wanda za ta k’ara yiwa kwarjini bare a ji shakkar ta.
Jin Bintu ba ta furta komai ba Maman Cangwai ta dawo daga gefan ta, in da ta zauna kamar me jiran umarni daga Bintu, a kaikaice yanda baiwar ba za ta fahimta ba ta ce da Bintu
‘’hattara Gimbiya, wanga batu ba na sassauci ba ne, dan haka zan ari bakin ki in ci albasa, ina mai neman alfarma rashin maganar ki bisa hukumcin da zan aiwatar kan wagga baiwa ta fabarusa’’
Ba tare da ta jira amsar Bintu ba ta mayar da kallan ta ga baiwa, sannan ta ce
‘’bisa ga umarnin Gimbiya, ta yaba da kyautar Yarima a gare ta, sa'annan wagga baiwa da ta kawo sak’o gare ta, zaki amshi bulala hamsin na daga tsimagiyan Gimbiya Fatima’’
Da sauri Bintu ta kai kallan ta ga Maman Cangwai cike da 6acin ran jin furucin na ta ta yi k’ok’arin dakatar da ita, wanda hakan ya sa Maman Cangwai saurin fad’in
‘’na yi kuskure Gimbiya, bulala sittin Gimbiya ta ke nufi, maza Lanta tashi ku fitar da ita zuwa d’akin horo, ki kuma sheda ma su umarnin Gimbiya kowa ya ji ya gani ya kuma sheda!’’

Baiwa na kuka ta na fad’in
‘’tuba na ke ran Gimbiya ya dad’e’’

yayinda Lantana ta tasa ta gaba, ta na mai fad’in
‘’godiya ta ke Allah shi taimaki Gimbiya’’
Su na fita hawayen da ya ciki idanun Bintu tuni ya gangaro bisa kuncin ta tsabagen tausayin baiwa da ba ta san hawa ba ba ta san sauka ba an k'ak’aba mata horo tsabagen rashin adalci. Cike da 6acin ran da ita kan ta Maman Cangwai ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login