Showing 18001 words to 19751 words out of 19751 words

Chapter 7 - BINTU DIYAR BAYI Book 1

13 Aug 2024

1769

ta san Bintu na da irin wannan fushin ba, ta furta

‘’akan wani dalili za a yiwa baiwa horo? Gide ita na ta ba sak’o ba ne? idan adalci ne na lalle sai kin nuna an min ba daidai ba ki hukunta shi Barde wanda ya aiko ta mana? Saboda ita baiwa ce? Su bayi ba su ‘yanci? Bayi su an bola?’’
Jiki a sanyaye Maman Cangwau ta furta
‘’hakan da na yi kad’ai zai nuna matsayin ki na d’iyar sarki, dan kuwa babu d’iyar sarakin da za a yiwa wanga cin fuska ta kasa aikata yanda na aikata, in ba dai so ki ke asiri ya tonu ba. Na san yanda ki ke ji, amma fa kada ki manta ko nima baiwar ce, ina fatan za ki fahimce ni.....’’
A fusace Bintu ta tashi tsaye, ta na mai girgiza kai ta ce da Maman Cangwai
‘’ba zan ta6a fahimtar ki ba in dai bisa zalinci ne, ba da yawuna ki ka aiwatar da hukuncin ga ba, umarni na anan shi ne ki gaggauta dagatar da shi!’’
A fusace ta wuce d’akin ta, wanda kan ta kai ga shiga sallamar wata baiwa ya tsaida ita. Ta na ji baiwar na gaishe ta amma 6acin ya sa ta kasa amsawa ta d’aga k’afa za ta shige kenan amma jin furucin na baiwar ne ya tsada ta. Jin ta na fad’in

‘’Yarima Sadauki ya na da murad’in ganin dukkanin bayin Sa’ayrasa!’’

A hankali Bintu ta juyo, wato 6acin ran da take ciki ya sanya ta rikidewa hatta Maman Cangwai, bare kuma su Ladiyo, tashi guda ta tashi daga Bintun da su ka sani ta zame mu su wata daban mai wuyan fasaltuwa. Ta na mai duban baiwar ta furta

‘’wa an Sadauki? A matsayin sa nawa ya ke da muradin ganin bayin Sa’ayrasa gide? Akan wani dalili?

Baiwa ta yi jim dan kuwa ta tsorata da yanayin da ta ga fuskar Bintu, cike da 6acin rai da kwarjini ga kuma tambayoyi na gadara da ta mata akan Yarima Sadauki. Nisawa ta yi kafin ta amsa mata da

‘’Allah huci zuciyar Gimbiya, Yarima Sadauki shi an Yaya ga Yarima Barde wanda ya ke maigida a gare ki, dalilin sa na murad’in ganin bayin Sa'ayrasa shi kad’ai ya barwa kan sa sani’’
Bintu na mai jinjina kai ta ce da baiwa
®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.



1⃣7⃣


Sidiya ce...✍��






Bintu na k’arasa magana ta shige uwar d’aka. Baiwa kuwa tashi ta yi cikin jinjina maganar ta na mai gyad’a kai ta fice ta bar Manman Cangwai da su Ladiyo cikie da mamakin sauyin Bintu lokaci guda duk akan kishin bayi. Minti kad’an sai ga ta ta fito sanye da lifayar nan da ta cire kafafun ta sanye da cikin farin takalmin fata ta ce da Ladiyo

‘’wuce mu tai d’akin horo’’

Da sauri Ladiyo ta yi gaba Bintu na biye da ita, ita kuwa Maman Cangwai bin Bintu ta yi da ido, cikin ran ta kuwa fad’i ta ke lalle dole ta aika da sak’on neman taimako Sa’ayrasa domin kuwa alamu ya nuna Bintu mai yin gaban kan ta ce.

Cikin sak’ar zuci Sadauki wanda ke zaune bisa daddumar da ke shimfid'e a lambu ya ke duban baiwar da ta zo masa da amsar Bintu gare shi. D’aya da ka cikin bayin sa ne ya furta

‘’gide Gimbiya d’iyar Sa’ayrasa ba ta da masaniya akan girman Yarima Sadauki, ko shakka babu za ta tuba Allah shi taimaki Yarima’’

Baiwa na mai gyad’a kai cikin amincewa da maganar na bawan ta ce

‘’kwaran gaske, tuba ta ke ran Yarima ya dad’e’’

Murmushin mugunta Yarima Sadauki ya saki, cikin ran sa ya na mai jaddada dana sanin da Bintu za ta yi bisa ga kuskuran da ta yi a gare shi, tabbas ta tari aradu da ka dama dai ta bar abin ya tsaya ga mijin ta da ya fi mata sauk’i, zai kuwa nuna mata bakin rijiya ba wajan wasan makaho ba ne. Mik’ewa yayi tsaye yayinda bawan sa yayi saurin matso da takalman sa gaban sa. Cike da tak'ama ya sanya bayi na masu ram masa baya su ka d'au hanyar fita.

‘Dakin Horo kuwa Lantana ce ta idda sak’on Maman Cangwai, nan da nan kuwa Dogarin horo ya shiga gyara tsumagiyar sa domin aiwatar da umarnin Gimbiya Fatima. Sauran bayi fada kuwa tuni labari ya zaga, sun yi tattaki zuwa d’akin haro domin ganin yanda baiwa za ta fuskanci hukunci. Kujerar horo aka sanya baiwa ta zauna yayinda aka zuba mata ruwa bisa cinyar ta har zuwa k'asan k'afafun ta yanda ko da zafin tsumagiya zai sa fitsari ku6uce mata ba zai nuna ba. Waje yayi tsit kuka baiwa kad’ai ke tashi yayinda Dogarin horo ya d’aga tsumagiyar sa ya na shirin sauke ta bisa cinyar baiwa muryar Ladiyo ya dakatar da shi ta hanyar fad’in

‘’dakata Dogarin horo, Gimbiya Fatima ce tafe!’’

Tsayawa yayi cak yayinda Bintu ta taho, bayi na bud’a mata hanya haka kuma ba su fasa kai gaisuwa gare ta ba har ta iso gaban dogarin horo. Cikin bayin kuwa har da Bakar number wato babban bawan Barde wanda jin an ambato sunan Bintu ya shiga baza ido domin ganin matar uban gidan sa.

Ganin Bintu gaban sa Dogarin horo ya saki tsumagiya k’asa ya na mai kai gaisuwar sa ga Bintu ta hanyar nuna ladabi da mik’a kai a gare ta cikin aminci. Bintu na duban baiwar da ta had’a hawaye da majina, a hankali ta k’asara gare ta, hannu ta sanya ta tada ita tsaye kana ta ce

‘’gide bar kukan ga haka, wagga hukunci baya bisa kan ki, maza tai abun ki, idan uwar gijiya ba ta zama mai tausayawa ga bayin ta ba shin ana tunanin za mu sami tausaya daga mai duka wanda mu an bayi gare shi?’’

Jin haka bayi su ka hau sowa, shewa da tafi, daga masu fad’in

‘’Allah shi ta ya mi ki, Allahu y ja da ran gimbiya, Allah ya sa ki dad’e ki na yi’’
Sai masu fad’in

‘’madallah da Gimbiyar Sa’ayrasa, mun biki, mu na madallah da ke’’

Ita kuwa baiwa ba ta san sa’in da ta zube k’asa hannayen ta rungume da k’afafun Bintu tsabagen farin ciki ma kasa magana ta yi. Bintu na mai murmushi a gare ta tare da duk kanin sauran bayi da ke wajan ta zame k'afafunta, bayi na mai darewa domin su bata hanya cike da nuna k’aunar su gare ta haka ta d’auki hanyar komawa turakar ta.

Babban bawan Barde da tun kan Bintu ta bar wajan ya ruga domin komawa ga Barde, tuni ya labarta masa yanda ta kasance tsakanin Bintu da bayi, ya k’are da

‘’lillahi warasulihi Gimbiya Fatima ta isa d’iya adala wacce ta san darajar bayi ko shakka babu halayyar ta ya yi kamanceceniya da na ka ran ka shi dad’e, aradu ma kuwa. Bayin Fabarusa za su zama su na alfahari da ita tun daga rana ita yau’’

Barde na mai duban Bakar number, duk maganar nan da ya ke hankalin sa ba gun sa ya ke ba, tunanin K'amariyya ne ya addabi ran sa ya na mai takaicin ina ma dai ita aka d’aura masa ba k’anwar ta ba, shin da wani ido ake so ya dube ta a matsayin mata har ya kai ga kusantar ta?


****

Sadauki da tashi tawagar kuma a nasu 6angaran fitowar shi daga lambu bayan ya gama d’an shawagin sa ya na mai tunanin matakin da zai d’auka bisa matar Barde ya hangi Bintu da Ladiyo a kan hanyar su na komawa turaka. Tsayawa yayi cak idanun sa bisa Bintu ba komai ya ja hankalin sa ba sai yanayin zubi da tafiyar Bintu da ya gani iri d’aya sak da na baiwar nan ta Sa’ayrasa da ya gani a daren jiya har ya kai ga aikawa Gimbiya Fatima muradin sa na ganin bayin Sa’ayrasa. Idanun sa kan Bintu ya furta

‘’gide wagga d’iya ba ita an baiwar Sa’ayrasa da na gani a daren jiya ba?’’

Bawan sa na mai duban Bintu da Ladiyo ya furta

‘’kwaran gaske, waccar mai tafe bayan Gimbiya Fatima na d’aya daga cikin bayin Allah shi taimaki Sadauki’’

Sadauki na mai girgiza kai cikin nuna rashin yarda da maganar bawa ya ce

‘’bayan Gimbiya Fatima? Wacce Gimbiya Fatima? Matar Barde gide? Yoto ai ni bayi biyu na ka gani, waccar mai tahiya irin na d’awisu, ma’ana mai sanye da lifayar can, ko shakka babu ita na gani sanye cikin kayan bayi a daren jiya, ba na mance abu mai kyau, ba zan manta da wagga tahiya irin ta ta ba, duk duniya ita d'ai ta na gani da wagga baiwa na iya taka k'asa kamar d'iyar Saraki'’

Bawa na tsoran kada ya yiwa Yarima Sadauki musu ya fuskanci hukunci, dan haka wannan baiwar da ta kawo sak’on Bintu ya yiwa nuni da hannu ya na mai tambayar

‘’ya ki nan, gide shin ko waccar mai tahiya tare da baiwar Sa’ayrasa baiwa ce?’’

Ko da baiwa ta ware ido ta hangi Bintu tuni ta shiga girgiza kai kana ta ce

‘’ina mai tuba, wagga Gimbiya Fatima d’iyar Sarki Inuwa na Sa'ayrasa ce ran Yarima ya dad’e’’

Jin haka Sadauki ya shiga shafa gashin bakin sa, har ila yau be d’auke idanu daga kan Bintu ba, dan ya tabbata ita d’in ya gani cikin shigar bayi, abun da ya kasa ganewa shi ne

‘’me zai sa Gimbiya, d’iyar Sarki kuma matar Barde shigar bayi? Shin menen dangantaka ko alak’a da ta ke da Shi mai k’arfi haka tsakanin ta da bayi da har za ta aiko masa da bak’ar magana dan kawai ya nemi ya gana da bayin Sa’ayrasa? Ko dan ta san ya gan ta daren jiya ne? Shin akwai wani lamarin 6oye dangane da ita?’’

Tambayoyin da ya ke ainawa cikin ran sa kenan yayinda tunani kala kala ke ratsa zuciyar sa. Ya na mai duban bawan sa ya ce

‘’ban yarda da wanga lamari ba, ina so a yi min bincike akan lamarin wagga Gimbiya, a gaggauta yi ba tare da sanin kowa ba, in kuwa na ji magana ta fita rariya sai da uwar mutum ta haifi wani!’’




������������
Copied By
YAYA HAYAT
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
Cool novel, makeup and kitchen2⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen3⃣)


WHATSAPP NO:
+2349030159301

5
6
7

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login