Showing 9001 words to 12000 words out of 19751 words

Chapter 4 - BINTU DIYAR BAYI Book 1

13 Aug 2024

1768

da ta ke mai dad'i, wai ga ta a makarantar su, tare da Aisar su na zantawa ya sa ta ji sam ba ta so ta farka. Gwaggo Munari ce ta katse mata jin dad'i ta hanyar jijjaga kafad'ar ta, wannan karan da d'an karfi domin kuwa sun jima da isa Masarautar Fabarusa, yanzun haka kofar fada su ke, Uwalanze har ta fice daga motar amma Bintu na nan ta na baccin asara.

A firgice Bintu ta tashi jin jijjigar ta wuce hankali, ga busar algaita da ke tashi, har da hayaniya da wak'e dake tashi daga bakin mutan Fabarusa da su ka cika kofar fada domin ganin isowar amaryar Yerima Barde.

Ganin alamar Bintu ta tashi, Gwaggo Munari ta shiga gyara ma ta alkyabba yanda fuskar ta zai rufu da kyau, ta na fad'in

"Ko ke fa Gimbiya d'iyar Sarki mai dole, ai ke kuwa bacci be same ki ba"

Kalmar nan ta Gimbiya da jama'a ke kiran Bintu da shi sam ba ya mata dad'i, gani ta ke tamkar ana raina mata iyayen ta, ya ga wanda su ka haife ta amma fin k'arfi zai sa a raba ta da su? In dai haka zama Gimbiya ya ke Allah wadar da irin na Sa'ayrasa.

Ta na kan wannan tunani ne gilashin motar ya sauka, yayinda Jakadiyar Fabarusa ta bayyana a gare su, kana ta ce

"Gide mutan Fabarusa, na cikin gari hallo da na fada, kwan mu da kwarkwatar mu, mun hito domin tarbar amaryar zaki, Yariman mu abin alfaharin mu. Mu na neman alfarmar bayyanar wagga Gimbiya ta Sa'ayarasa, da ta kasance Gimbiyar Fabarusa da ga ranar jiya har illa MashaAllahu"

Gwaggo Munari na mai murmushi ta amsa mata da

"Gimbiyar ta mu, wacce ta kasance fure a gare mu, wacce babu shakka za ta wadata ku da kyawu gami da kamshi da ke tattare da ita, Gimbiya Fatima ta Sa'ayrasa ta amsa kiran mutan Fabarusa"

Jakadiya ta rangwad'a gud'a, tuni waje ya kaure da hayaniya,yayinda mata da yara su ka hau wak'a su na tafi, fad'i su ke

"Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!"
������������
[17:20, 30/08/2017] ‪+234 708 037 9015‬: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


8⃣


Sidiya ce.....✍��


Shiryayyan d’aki mai had’e da 6and'aki aka aje su Ladiyo, su Bintu kuwa d’aya daga cikin d’akunan Goggon nan a matsayin ta na uwar gida aka sauke su kan a gama wankan amarya a mik’a ta ga na ta 6angaran.
Su na shiga masaukin na su ba da jimawa ba, wata baiwa ta sake dawowa d’auke da kaya, gaban Bintu wacce ke zaune bisa gado har lokacin ba ta bud’e fuskarta ba baiwa ta zu6e, ta na mai aje kayan gaban ta, ta ce
‘’ an gaida Gimbiya Fatima, wagga kaya tsaraba ne da ga Goggo nan, ta ce a shedawa Gimbiya Fatima ta sanya su yayinda za ta hito wajan wankan amarya nan ba da jimawa ba’’
‘’Gimbiya Fatima ta amsa, ta na godiya’’
Cewar Gwaggo Munari. Bayan fitar baiwar Gwaggo Munari ta yaye alkyabbar Bintu, sai ga ta ta yi wuri wuri da ido.
‘’Gimbiya yanzun ga ba lokacin tuntuntuni ba ne, kin dai san dalilin da ya sa ki wanga Masarauta da kuma a gurbin wacce ki ka zo, gwara dai ki sake shawara ki nutsu in har ba so ki ke ki rasa ran ki sa’annan ki haddasa yaki da gaba wanda ka iya halaka ta mu Masarauta gaba d’aya’’

Fad’in Gwaggo Munari cikin gazawa da halayyar Bintu dan kuwa idan ba ta yi da gaske ba ko shakka babu asirin su mai tonuwa ne. A sanyaye Bintu ta ce
‘’ina tuba....’’
‘’ba tuban ki mu ke buk’ata ba!’’
Gwaggo Munari ta katse Bintu, kana ta k’ara da
‘’ Aikin ki mu ke buk’ata Gimbiya! Wanda za ki fara yanzu ta hanyar zama Gimbiya ba d’iyar bayi ba. Allah ya mi ki zubi irin na jinin mulki, kowa ya gan ki ya san hakan nan Allah ya yo ki, ba ki gada ba amma Allah ya baki su a halittar ki, Dan haka tak’ama da isa shi na ke so daga gare ki, ki saka a ran ki wannan dama ne da Allah ya baki dan jin dad'in rayuwa da kuma taimako ga Masarautar mu, idan asirin mu ya tonu gaba d’aya farin cik’in masarautar mu ne zai koma ga zubar jini, ina fatan kin fahimce ni?’’
Bintu ta gyad’a kai. Kana Gwaggo Munari ta dafa kafad’ar Bintu ta ce

‘’madallah da d’iya ta gari. Sai ki yi shiri yanzu su Ladiyo za su zo su had'a mi ki ruwan wanka. Hakuri za ki yi na san kin saba yiwa kan ki komai amma daga yau komai yi mi ki za ake yi, ki jure Bintu wata rana sai alkhairi’’
Bintu ta dad’a jinjina kai. Ana hakan kuwa su ka ji an sake turo kofa an shigo. Maimakon Ladiyo da Gwaggo Munari ta ce, Lantana ce baiwar da Yarima Nuhu ya za6a ta musammam domin kular masa da al’amran Bintu ta shigo ta zube gaban su. Gwaggo Munari na mai duban ta tace
‘’Lantana gide ke ce mai shirya ruwan wankan ne? yo to ina sauran? Kar dai sun tsaya kallan kauye mu ka biya ku fa sai mu makara!’’
Lantana waccen ita dama da ka gan ta ka ga zubin munafunci, dan ko magana ka ke da ita haka za ka ga ta na sinsin da idanu sam ba ta bari a ga kwayar idanun ta. Ta kada baki ta ce
‘’ai ga su nan tafe, sauri na yo dama na shirya ruwan wankan kada a makara’’
Jin haka Gwaggo Munari na mai mata nuni da bayan gidan da ke cikin d’akin ta ce
‘’yauwa madalla da ke, maza je ki ga bayan gidan can shirya mata gide’’

Sim sim ta shige bayan gida. Sai da ta fara taran ruwa sannan ta shiga had’a ruwan da turaruka iri iri kamar yanda su ka saba had’a ruwan wankan Gimbiyoyi. Ko da ta zo kan turaren karshe, sai ta faki idanun Gwaggo Munari ta tabbatar hankalin ta na kan su Ladiyo da shigowar su ke nan, ta na mu su bayanin yanda ta ke so su kasance wajan taro. Sannan ta jawo kofar bayi ta rufe. Gefan zanin ta ta kwance, ta dauko wani kullin magani, cikin sauri da azanci ta bud’e maganin ta na mai zazzage shi cikin ruwan wankan Bintu. Tuni wani irin bakin hayaki mai wari ya taso daga ruwan yayi sama, ita kan ta Lantana sai da ja baya ta na mai toshe hancin ta cikin tsoran kada fa su Bintu su ji duk da dai Yarima Nuhu ya tabbatar mata babu wanda zai ji warin bayan ita da ta zuba. Sai da ruwan ya dena kumfa da hayaki sannan ta mayar da sauran kullin maganin cikin zanin ta ta kulle, ta fito hankali kwance kamar ba ta aikata komai ba.


������������
[17:20, 30/08/2017] ‪+234 708 037 9015‬: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.




9⃣

Sidiya ce......✍��



Fitowar ta ba da dad’ewa ba Gwaggo Munari ta sanya Bintu wankan dole dan kuwa ba da san ran ta ba. Da taimakon su ladiyo da Hansai Bintu ta fito fes cikin doguwar riga ruwan d'orawa, rigar da Goggon nan ta aiko mata. Material ne mai tsada ke, sai kuma mayafi kore mai turawa da ratsin ruwan d'orawa. Gwaggo Munari ruke da hannun ta domin kuwa ita ta ke gane mata hanya su ka fito, Su Ladiyo biye da su yayinda aka mu su iso zuwa babban zaure in da mata da iyalan Sarki ke jiran isowar su.

Babban zaure ne wanda ya fi k’arfin a k’ira sa da zure sai dai ko d’akin taro, tsawon sa kamu d’ari, fad’in sa kamu hamsin. Haka kuma ko wacce kusurwa na zauren an masa ado da itacen al’ul a bisa ginshishik’an sa. Bayan ga dadduma mai kulliyar jikin damisa da ke shimfid’e tun daga fari har zuwa k’arshen zauren da kuma tintin masu adon jikin damisa da ke baje bisa daddumar, akwai duwatsu wanda aka auna sa’an nan aka yanka su da zarto ciki da baya daidai da juna, aka jera su zagaye cikin zauren tamakar kujerun zama irin na zamani. Haka kuma bangon zauren zane ya ke da tambarin Masarautar Fabarusa.
Cikin zauren su ka tadda dukkanin iyalan Sarki Abdulrahman tare da y'anuwa da abokan arziki wanda su ka zo domin ta ya su murna. Matan Sarki Abdulrahman uku wanda su ka had’a da Goggon nan (uwar fada), sai ta biyu wacce su ke kira da Goggo ta dole(uwar dole) sai ta ukun wacce ake kira Uwar Soro, wacce itace mai k’arancin shekaru cikin matan sarki. Kowacce hakimce, k’ishingid’e bisa tuntin. Gaban su kuma wani tulu ne wanda aka masa ado da azurfa cike da ruwa mai d’auke da turare da garin lallel.

Haka kuma ‘ya’ya da jikokin sarki da na su wajen daga gefe wanda d’irga su ba k’aramin aiki ba ne kasancewar ‘yay’an sa mata ma su aure da ‘ya’ya sun kai su goma sha takwas, kuma dukkanin su ba su yi k'asa a gwaiwa ba haka su ka zo da sassa da yankunan Jamhuriyar Nijar domin tarbar amaryar d’an uwan na su. Duk da dai ciki akwai mu su bakin cikin lamarin kasancewar ciki d’aya su ke da Yaremi Sadauki. Musammam Yaya Mai Soron Baki, babbar d’iyar Sarki Abdurahman da mai bin mata wato Yaya Jidda wanda su 'ya'yan Goggon nan.

Wajan da aka tanadarwa Bintu gaban su Goggon nan aka zunar da ita. Tun da ta yi wanka da ruwan nan na Lantana hankalin ta ya ke a tashe, gashi gaban ta sai fad’uwa ya ke, ta na son fad’awa Gwaggo Munari amma ta tsoran za ta yi zatan fad’an da aka mata ne be shige ta ba, dan haka a dole ta hakura da ikon Allah. Maimakon Gwaggo Munari ta zauna gaban ta, sai gani ta yi ta ja gefe daga wajan su Gwaggon nan. Cikin girmamawa ta mik’a gaisuwar ta tare da damk’a amanar Bintu gare su bisa ga al’ada. Goggon nan wacce a ran ta ta yi farin cikin fasa auren d'iyar Sarkin Sa'ayrasa da Sarki Abdulraman yayi, ta kuma yi bakin cikin aurar da aka aurawa Barde a maimakon d'an ta Sadauki, ta fara kar6ar amana ta hanyar saka hannu ta bud’e mayafin Bintu da ke gaban su, tuni Bintu ta yi k’asa da idanun ta cikin fad’uwar gaba. Sai da ta kalli fuskar Bintu na d’an wani lokaci ta na mai yamutsa fuska ta saki mayafin ba tare da ta rufe fuskar gaba d’aya ba. Kana ta ce

‘’ni Munzaratu jikar Sarki Abdulrahman na difa, d’iyar Sarki Abdulmuminu iii na Agadez, matar Sarki Abdulraman ii na Fabarusa, na bud’e fuskar amaryar dan mu, d’iyar Sarkin S’ayrasa, Sarki Sule Inuwa Magaji da zannuwa hamsin, kallabi hansin tare da bayi guda uku’’

Jakadiya ta rangwad’a gud’a, yayinda waje ya d’au sowa. Ita Bintu ta yi k’asa da idanun ta, ji ta ke kamar ta dan ta k’arasa rufe fuskar ta gaba d’aya. Amma me za ta ji? Goggo ta dole ce ta sa hannu ta k’ara yin baya da mayafin Bintu yanda za ta ga fuskar Bintu da kyau, kafin ita ma ta jero sunan ta da nasabobin iyayen ta, ta bud’e fuskar Bintu da silallan gwal. Ita kuwa Uwar Soro da tashi na ta bajintar da dawakai tare da rak’uma ta bud’e fuskar Bintu. Tuni Bintu ta zama mai arziki da kadarori, su Ladiyo cikin ran su sai mamakin baiwa da Allah yayiwa Bintu, su na jin ina ma dai su ne.
Bayan da matan Sarki suka gama budar ka, sai kuma sauran 'yan uwa da abokan arziki, yayye da k'Annan Barde su ma su ka nuna ta su bajimtar.

Bayan an gama ne Jakadiya ta mik’a wa matan Sarki tulu. Matan sarki su ukun nan su ka tsaya bisa kan Bintu su na mai tsiyayo mata ruwan cikin tulun kad’an kad’an bisa kan ta, yayinda Jakadiya ke bada wak’a jama’ar wajan na amsa mata

"Ayyare daure jure
ayyaraye daure jure!
zaman gidan wani tilas ne!
ba kan ki ne aka fara
ba da kan ki ne aka fara ne
da kin ci kuka kin k'oshi
ke yar tsohuwa mai 'yar tulu
Allah ya kar ki watan gobe
Mu ci gumba’’




������������
[17:20, 30/08/2017] ‪+234 708 037 9015‬: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
��������
������������
��������������



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


1⃣0⃣



Sidiya ce....✍��


Ana gama wankan amarya Bintu ta ja jik’akken mayafin ta ta rufe fuskar ta tana mai shar6ar kuka. Ba tare da 6ata lokaci ba d’aya bayan d’aya sauran iyalan Sarki su ka dinga zuwa Jakadiya na gabatar da su, har su ka k’are sannan aka rufe taro da addu’a. Da aka gama maimakon a kai Bintu d'akin auren ta, 6angare ne na musammam cikin gidan Sarki, sai wani 6angare aka sake kai ta na daban daga cikin 6angaran Goggon nan wanda ya kunshi d’aki biyu kowanne da bayi sai kuma falo. Nan za ta zauna har sai sanda ta kai budurcin ta d’akin mijin ta. Za6in bawai d’aya daga cikin bayin ta wanda za su na kwana 6angaran ta aka bata. Gwaggo Munari ce ta za6a mata Ladiyo dan kuwa ta fi yabawa da hankalin ta, sauran kuma wuni za su na yi, idan lokacin bacci yayi ko kuwa Bintu ta sallame su sai su koma 6angaran da aka tanadarwa bayi.


Yarima Barde kuwa duk wannan bikin da ake masa ya na daga na sa 6angaran. Su Yarima Jafar da Khalil tun suna iya jure shirun da ya mu su har su ma su ka gaji su ka yi na su gurin. Da ya gaji da zaman ne ya watsa ruwa yayinda ya sanya jallabiya, kai tsaye in da ya saba zuwa duk sanda ran sa ya ke 6ace ya nufa, wato lumbun da yake k’yatare da 6angaran matan Sarki. Nan bisa dutse ya kusa raba dare, sai da ya ji idanun sa sun masa nauyi sosai sannan ya tashi a hankali ya nufi 6angaran sa. Ko da ya zo giftawa ta 6angaran da ya san babu shakka nan aka sauki amaryar da aka aura ma sa, sai ya tsinci kan sa ya na mai mummunar fad’uwar gaba. Hakan ya sa shi wucewa da sauri ya na mai ambaton ubangiji. Bakin kofar sa ya tadda dogarai da bayin sa sun yi jugum jugum kasancewar ya mu su hani da biyo shi, ganin sa su ka fara masa kiran lafiya su na mai fad’in

‘’takawa sannu Yarima Barde, lafiyarka dama da hauni, dama da hauni lafiya, salamun salamun’’

Ganin ya zo daf da shiga kofar da za ta sada shi da 6angaran sa, su ka taka masa baya, har ila yau fad’i su ke
‘’gicciye dama Yarima, gicciye salamun’’
Tsayawa Yarima Barde ya yi, ya d'aga mu su hannun alamar baya buk’ata su biyo shi kafin ya sa kai ya shige ciki. Ya bar su waje su na kallan kallo, dan kuwa sun san lamarin auren Yarima Barde kan su zai k’are duk da dai ba su suka kar zuman ba, rataya aka ba su.

Washagari da sassafe jama’ar Fabarusa, Samari da ‘Yan mata har da tsuffin cikin adon su na burgewa su ka yi dandazo kofar fada domin kallan hawan angonci bisa al’ada. Amma Yarima Barde ya yi k’yememe ya ki fitowa ko da kuwa kofar 6angaran sa ne bare a sa ran zai hau. Ko da su Khalil su ka je da numin bashi baki, a bakin k’ofa dogarawa ma su tsaran kofar Yarima Barde su ka fad’a mu su buk’atar Barde na kada a bawa kowa damar isa gare shi. Dan haka sai hakura su ka yi, Magatakarda ne yayi shela ga jama’a cewar Yarima Barde be shirya yin hawan angoncin shi a ranar ba, su yi hakuri sai zuwa ran da ya shirya za a sheda mu su. Da kyar kamar ba su hakura ba su ka watse, dan ba k'aramin cin burin hawan angoncin Yarima Barde su ka yi ba, kasancewa akwai k’auna tsakanin sa da Talakawa, musammam ‘yan mata da samari, Yarima Barde na su.

"Bayan hayaniyar kofar fada ta lafa, jama’a sun watse su Gwaggo Munari da sauran tawagar Sa’ayrasa su ka yiwa iyalan Sarkin Fabarusa sallama, an had’a mu su koma ta arziki sannan su ka d’auki hanyar komawar su gida S’ayrasa, in da su ka bar Bintu tare da bayin ta, wato Ladiyo, Hansai, lantana da Maman Cangwai a sabon Masarauta. Gwaggo Munari ce ta shedawa Iyalan Sarkin Sa'ayrasa irin tarbar da aka mu su da tarin dukiyar da Bintu ta samu. Gimbiya K’amariyya kuwa sai da ta had’a da kwanciyar asibiti. D’aya daga cikin bayin da su ka juyo ne ta isar da sak’on Lantana ga Yarima Nuhu. Sakon na cewa ta aikata komai yanda ya umarce ta, kuma komai ya tafi daidai. Tsabagen dad’in sak’on na ta har kyautar zani da kallabi ya bawa baiwar domin kuwa in har maganar hakan ta ke babu shakka hakin sa ya cimma ruwa.


Kwanci tashi. Bintu ta cika sati guda Masarautar Fabarusa, amma ko da wasa Yarima Barde be ta6a takowa in da ta ke ba bare ma ta san kalar fuskar sa. Gata kuwa ta na sha gurin matan Sarki, musammam Goggon dole da Uwarsoro ,domin kuwannan su burin su ace amaryar Barde daga ta ta ce, Maman Cangwai ce ke saka Bintu a hanya kasancewar ita ta gane manufar su ba lalle alk’airi ba ne. Ita dai ta bi kowa sannu a hankali. Goggon nan kuwa mulki da jin kan ta kad’ai ya fi k’arfin ta, shi Yarima Barde ba gaban ta ya ke ba, bare uwa uba matar sa.




������������
[17:21, 30/08/2017] ‪+234 708 037 9015‬: ®
✏��
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

����BINTU 'DIYAR BAYI

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login