Showing 3001 words to 6000 words out of 162126 words
don bata lift saidai ko kallo basu isheta ba,hakan,na yawan faruwa da ita kasancewar unguwar nasu na maqotaka da unguwar nasarawa G R A,duk sanda hakan ta faru takan yawaita neman tsarin Allah,sannan takaici mamaki gami da tsoron maza kan sake yawaita cikin zuciyarta,basu da burin da ya wuce suga sun samu damar da zasu shiga rigar mutuncinki su wuce su barki babu batun aure
da qyar ta samu wata da yara yan makaranta biyu a ciki,ta masa kwatance inda zai ajjiyeta
cikin murna raliya ta tarbeta,cikin falonta suka zube bayan ta cikata da kayan ciye ciye suka hau hirarsu da bata qarewa fadil na bisa cinyarta,
''kinga kawo fadil din na riqe miki shi tunda yayi bacci ki samu kici wani abun,idan ba haka ba bazai barki kici komai ba''
''a'ah qyalemin shi''
cikin haka wayar raliyan ta soma tsuwwa,ta cirota ta duba screen din tana fadin ''abban fadil ne''
magan sukayi ta tsawon minti biyar sannan ta kashe tana duban maryam bayan ta miqe
''yace yana miki sannu da zuwa,bari,na saka miki wani film ya dan debe miki kewa ni shiga kitchen ya kamani,abban fadil ne zaiyi baqi''
''haba kema raliya naji zancan shiga kitchen kuma na zauna,ai kinsan sai anyi da ni''
''sannu uwar madafa''ta fada cikin zolaya
''na karba,ko kin manta kan abinda na samu degree kenan''
''wannan gaskiya ne,bani fadil din to na kwantar da shi sai mu wuce kitchen din ko?''
qarfe hudu da mintina ashirin suka kammala,lafiyayyen girki ne wanda maryam ta gwada basirarta akai,ita kanta raliya komawa tayi gefe tana kallonta don bata zaci qawar tata takai haka ba,biyar saura ta suna falo,ta soma hada kayanta don tafiya gida ''amma diyana(haka suke kiranta wani lokaci a makaranta)ki sake wanka mana wannan aiki da kika sha''
''ai dole ne,amma fa idan na isa gida''
''ai ko wlh anan zakiyi''
murmushi tayi wanda har dashashinta sai da ya bayyana
''kinsan dai bana wanka na maida kayan da na cire,ni kuma ban taho da spare ba''
''tsarabarki ta south africa tana nan,saiki zabi daya a ciki kisa''
duk wayon,maryam sai da raliya ta sata yin wankan ta kawo mata ledar tsarabar ta zabi doguwar riga guda daya da tasha adon jajayen dutsina masu yawa da sheqi
a falo ta taddata''kinga kuwa maryam yadda rigar nan ta miki,Allah ya kawo miji na gari,gaskiya ba qaramar hidima zamu sha ba''
''har yanzu babu abinda ya ragu a surutun raliya''
''haka miskilanci kyau da ajin maryam diyana har yau yana nan''duka sai suka sa dariya,yana daya daga abinda ya sa qawancensu ke ma maryam dadi,raliya akwai vbarkwanc,inda kuma halinsu yazo daya ta bangaren haquri da dauke kai
qarar bude get din gidan ne yasa suka ankara da isowar abban fadil
''kinga har sun iso ina nan a zaune,biyar harda kwata''maryama ta fada tana miqewa
''kinga malama koma ki zauna tunda sun riga sun iskemu tare ai bakya tafi ba,ki bari mu tari baqinmu qarasa ladarmu tare''babu yadda ta iya haka ta koma ta zauna,ta fiddo wayarta tqna yiwa hndatu texs ta sanar da mama tana nan tahowa raliya ce ta tsaidata
tana cikin sending sallamar baqin ta ratsa dodon kunnenta,a sanyaye ta dago tana amsawa,su uku ne abban fadil na hudu,duka sai taji ta a takure gashi raliya ta shiga ciki sako mayafi,sai ta miqe tana daukar jakarta tace
''sannunku da zuwa,abban fadil yanzu raliyan ta shiga ciki bari na mata magana''
dakatar da ita yayi
''a'ah yi zamanki,nasan a gajiye kike kunsha aiki bari na fito da ita,jabir bari na fito da madam''
falon yayi shiru su duka harda baqin,wayarta na hannunta tana danne danne amma sai take jinta a takure,gashi daga raliyan har nasir din shiru kamar an shuka dusa
''madam haka ake kula da baqi?''
tajiyo maganar lokaci guda,ta daga kanta don ganin me maganar,shije zaune opposite dinta,sanye yake da shadda hartin da hula,murmushi ta danyi a taqaice
''ai bani bace matar gidan,ku jirayi fitowarta''
''ke da ita din ai daya ne,don na tabbata yarda ce tasa suka barki da baqinsu''
sai ta maida idonta kan wayarta don bata da abun ce masa,Allah ya taimaketa masu gidan suka qaraso
gaishe gaishe ne suka biyo baya da 'yan hirarrki,saidai duk lokacin da bisa kuskure idonta ya kai sashen da wanda ake ka kira da jabir sai ta tsinci idanunsa na bisa kanta,wanda hakan har ya fara damunta,nasir ya musu jagora zuwa dining domin cin abinci hakan yasa ta cema raliya
''to ai na gama ko,bari na wuce gida''
''tunda ba da mota kika zo ba ki bari mu kammala sai mu wuce tare ko?''
ta jiyo muryar jabir din na fadi
''kasan kuwa kusa da unguwar take ba''inji nasir
''haka,ne fa,shikenan kin huta hawa keke napep''inji raliya
''amma kinsan baxaiyiwu su kaini gida ba,idan mama ta ganni kuma nace mata su waye?''
''indai mama kike ji zan kira tq na gaya mata''inji raliyar
cikin zuciyarta ta ja tsaki,
''wannan jabir dan shiga hanci ne wlh''babu damar musu tunda duka ido na kanta haka ta koma ta zauna tana jira su kammala,yana bisa dining din amma idanunsa na kanta har raliya ta ankara,cike da gulma ta tabota
''ke,inafa tsammanin kinyi tsuntuwa yau a gidannan''
cikin rashin fahimta tace
''ta me fa?''
hararta tayi ''kiji min 'yar rainin sense,kina nufin baki lura da irin kallon da jabir ke miki ba?''
''shine me?''
''wlh sonki yake bisa dukka alamu''
wannan karon ita ta maida nata hararar''kijimin mata,kawai daga kallon sarkin fawa sai miya tayi zaqi?''
''wlh da gaske nake,jabir mutumin kirki ne diyana,kada kice zaki qishi don Allah''
''a'ah,kinji ta da wani guntun wa'azinta,ashe har yace miki ma yana sona ko?''
''ni na gaya miki zai fada miki''
Can saman dining dinma jabirne ke cewa cikin qasa qasa da murya
''kai mutumina nifa nazo gidanka a sa'a,Allah yasa bata da wani''
dariya ya saka''tuni na harbo jirginka ai,indai bilkisu ce a iya sanina ba'a tsaida mata miji ba''
''ai kuwa bazan tsaya kallon ruwa ba,a yau zan kafa kaina''
A bakin layinsu tasa ya tsaida motar,ta bude murfin tana cewa
''na gode''
''haba madam da sauri haka?''
sai ta juyo cikin mamaki tana dubansa
''eh mana,ya zaki min illa kuma ki tafi ki barni ba tare da kin bani magani ba''
ci gaba tayi da dubansa,sai ya saisaita nutsuwarsa,baiji ko,nauyi ba ya bayyana mata duka manufarshi,da farko ta ja masa yace shikam yace baisan wannan zancan ba,babu inda,zata tafi ta barshi cikin qila wa qala,idan,ko ta tafi to zai tare ne a qofar gidansu har sai ta amsa masa koda zai shekara
maganar da sukayi da raliya ce ta fado ranta
''maryam,wlh indai aure kike so kiyi kada kiqi karbar tayin jabir matuqar yayi miki maganar,jabir bazai taba tararki da maganar banza ba,nasan jabir tuntuni,abokin nasir ne da dewa,halayensu kusan daya,hakan shi ya qara danqon abotarsu''
ita kanta a zahirance bata ga wani aibu ba tattare da jabir din,yana da kyau daidai wanda duk hassada ba zaka kira shi mummuna ba,a iya abinda ta gani da bayanan da raliya ta mata ta fuskanci zata iya amsa tayin jabir,ko don ma ran mahaifiyarta yayi fari,ko don ta samu itama ta zauna a nata dakin kamar sauran qawayenta da 'yan uwanta
ganin shirun nata yayi yawa yasa ya sake marairaice mata ga tsammaninsa zata wofantar da buqatarsa ne
''shikenan,Allah ya shige mana gaba''
''um um maryama,wannan ba amsa bace,kice ina sonka jabir shine magana''
kanta ta girgiza cikin alkunya tace''don Allah ka barni na wuce gida,na tabbata zan sha fada gun mama,don na kai magariba a waje,tunda ka kwaahe min numbers ai sun isa''
fitowa yayi ya zagayo ya bude mata murfin yana cewa''shikenan,kin bani izini na kiraki?''
kai ta gyada masa,kafin ta dauko jakarta yayi sauri ya rigata ya bude zif din ya jefa mata kudi,ta noqe alamun ba zata amsa ba shi kuma yace indai bata karba ba to tana nufin bata sonshi,tilas ta karbi kyautar tasa,sukai sallama amma sai taga ya ja ya tsaya,kallonshi tayi ya daga mata gira
''sai na hango,shigarki gida don tsaron lafiyarki da kuma gane gidan naku koda na tashi zuwa''
murmushi kawai tayi tajuya domin shigewa layin nasu
katsam idonta kan isyaku,kai ya gyada sannan ya kwasa da gudu yayi gida,la'ilaha illa nata subhanaka inni kuntu minaz zalimin,tasan tamkar a idanun iyayenshi tayi,cikin fargaba taci gaba da takawa jabir na mata rakiya da idanu har ta shige gidan
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📓✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:49 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺
▶4⃣
sai da tayi dira dira a soron kafin ta gano ainihin hanyar wucewa,saboda cike yake da 'yan zance,can hauwa can binta can maijidda kai abun takaicin ma harda zainabu wadda du du du ba zata wuce shekaru goma sha hudu ba kacal a duniya
ta tsakiyarsu ta raba ta wuce,taji dadi sosai da babu wadda ta tanka mata a cikinsu
cirko cirko ta samesu a tsaye cikin tsakar gidan,inna hadiza ce da baba huwaila sai babansu dake bakin famfo yana daura alwala da alama haramar sallar isha'i yake yi,sai kuma isyaku dake qame a gefe da alama tuni ya gama fesar da abunda ya qunso
''la ha ila ha illallahu,muhammadu dan abdullahi''suka dauko salatin tare yayin da huwaila ta dire ita daya ta kuma dora
''wlh yaya da gaske ne yaro baya qarya,tayani gani don Allah,suturar jikinta ma ai ba da ita ta fita ba,lallai dandi na dada samun gindin zama a gidannan''
inna hadiza dake ta faman gyada kai tana kallon maryamu wadda ke tube takalmanta a qofar dakinsu ba tare da ta dubedu ba tace''qwarai da aniya,ya gama yawon barikin da ita ya kwashi na kwasa ba dole ta canza sutura ba,yo zata shigo mana gida ne da najasa ne''
''ke meramu zo nan''
kiran baban nata da baqin qazafin da suka jefeta da shi ya daki zuciyarta lokaci guda,a sanyaye ta dawo gabansa ta durqusa kanta a qasa
''wanne dan iska ne ya dauko ki a mota har gidan ubanki?''
muryarta a sanyaye tace''ba dan iska bane baba,gidan raliya muka hadu yace yana sona''
''yana sonki?''
huwaila da hadiza suka fadi kusan a tare
bai biya ta kansu ba ya dora da nashi bayanin
''alhmdl dama ni na gaji,na gaji wallahi kullum rana a unguwarnan sai anyi da ni kan na ajjiye babbar mace a gida,saboda haka ki shaida masa matuqar da gaske yake to na bashi kwana goma ya fito ayi kowa ma ya huta''
''yo idan banda abunka malam amadu saurayin qwarai ne zai dinga yayibar yarinya yaro kwararo kwararo kuma yace zai aureta,ai qarya ne dan yaudara ne kawai''inna hadiza ta,cafe maganar
''oho,koma dai meye nidai na gama magana,tashi ki bani guri''
jikinta a sabule ta miqe tayi hanyar dakinsu,har yanzu kunnuwanta badu daina jiyo mata qananun magan ganun da suke yi bq marasa dadi akanta ba,taimakon da Allah yayi mata daya yau baban nasu bai bi ta kansu ba yayi ficewarsa masallaci,wannan wace iriyar masifa ce?,tamkar ita ke da ikon rubutawa kanta qaddararta?,ita ta hana kanra aure ne?,shikenan a rayuwa babu dama Allah ya qaddara maka wani abu sai jahilan cikin mutane su dinga ganin tamkar kai ka jawowa kanka ko da amincewarka hakan ta faru?,
mamanta na cikin rumfar a zaune amma tamkar bata a cikin gidan,wannan dabi'arta ce,tana da dauke kai da yakana akan 'ya'yanta,da wuya ka taba mata yaro kaji bakinta,da wannan damar mutanen gidan ke amfani suke cin karansu babu babbaka a kansu,duk da wasu lamuran hindu na masu tambotsai idan taga cin kashin yayi yawa,don ma mama na kwabarta
yanzun ma baqinciki ne ya hanata motsi da kuma umarnin maman,don tana zaune ne tana karatun waec da fitilar qwai a gabanta,sallamar ta kawai hindun ta amsa ta dora da cewa
''yanzu fisabilillahi yaya maryam haka zaki ci gaba da zama ana miki cin mutunci ba zaki kare kanki ba?''
''kinci gidanku nace hindatu,nace kinci gidanku,da baban nata zatayi sa'insa ko da matan ubanta?,ke maryamu,ina kika samo kayan jikinki?''
kai ita kam dai ta shiga uku,wato ko ina cikin tuhuma take
''mama tsarabar da raliya ta bani ce,na tayata aiki tace bazan taho ba sai nayi wanka,shine aciki na cire nasa wannan''
''madalla,amma daga yau kada ki sake ki sake kaiwa magariba a waje kina jina ko?''
''to mama''
dakinsu ta shige ta ajjiye jakarta saman katifarta,qoqari take ta shanye dukkan wani bacin rai,batason ta barshi yayi tasiri a ranta,tunda idan da sabo ai yaci ace ta saba,sau nawa ake ruwa qasa tana shanyewa,ta zare rolling din kanta ta dawo tsakar gida ta daura alwala,sai da tayi nafila raka'a biyu ta kaiwa Allah kukanta,ta dade saman carfet tana jan,hasbunallahu wa ni'imal wakeel sannu a hankali taki sauqi na zuwar ma zuciyarta
kira ne ya shigo wayarta data duba agogo sai ta tabbatar jabir ne don bata da alaqa da wani da zai kirata a irin wannan lokacin,shi dinne kuwa,awanni kusan biyu sukayi akan wayar har ta soma gajiya don bata saba doguwar hira irin haka waya ba,cikin awanni tayi amanna da kyawawan halayen jabir,bayan ta,jada da wanda raliya ta gaya mata,a yanzun mafita kawai take nema,koda wanda bai kai jabir din ba zata iya aurenshi matuqar zaya riqeta da daraja
sunayin sallama hindatu ta shigo dakin da tarin litattafanta ta watsasu tata katifar,kasancewar dakinsu daya don maryamu bata da sha'awar raba daki da 'yar uwar tata,doguwar hamma ta ja,maryam ta dubeta tana dariya ''boko wahala''
''mtsw,ke dai bari yaya maryam,yanzu a haka kukayi degree?''
''me kayi da maza inji karya,idan banda abun hindu ke,da sai yanzu ma zaki bar secondry din''
''gaskiya ne kuma fa''ta fada tana fadawa kan katifar tabayan ta ture liattatafan da ta watsa gefe
''yauwaaa''maryayam ta gada tana janyo jakarta ta ciro kudin da jabir ya bata dazu
''ungo irga kiga nawa ne''
''an biya ku salary ne ya maryam?''tace lokacin tame lissafa kudin
''a'ah jabir ne ya bani''
''ya maryam Allah ya tsaida jabir din nan mu sha budiri''murmushi itadai kawai tayi
''ten thousand ne''
''ok...to ko riqesu,zan cika miki kudin rigistration din exam dinku''
''na gode ya maryam,na gode''
''don mind,ni dake duka daya ne,kawai ki tayani addu'a hindu''
''ai babu fashi wannan ya maryam''
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
cikin sati,guda kacal sabo ya shiga tsakaninsu da jabir,yana da sauqin kai,fara'a da haba haba da jama'a,yan sonta ji da ita da tattalinta,cikar satin ta isar masa da saqon baban,murna da farinciki tamkar zai goya ta,washegari kuwa magabatansa suka iso,a take aka tsaida magana harda sa rana,farincikin mama bazai misaltu ba duk da tana boye wa,yayin da huwaila da hadiza sukejin kamar an musu transfer zuwa jahannama
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
shiye shirye tuni suka fara kankama domin sati biyu kacal ya rage,cikin yammacin gab da sallar magariba jabir yazo gurinta kawo mata invitations kasancewar akan hanya yake yasa bai shiga daga cikin gidan ba,suna tsaye jikin motarsa taga kamar an wulgasu,ta dago kanta don ganin me wucewar,maraqisiyya ce har ta gota su taga ta dawo,da baya,qare musu kallo tayi sannan ta gyada kai ta shige cikin gidan fuuu da uban akwatinta dake rinjayarta
wani faduwa taji gabanta yayi wanda yasanya har sai da ta rufe idonta,duk lokacin da maraqisiyya tazo gida to babu alkhairi a zuwanta,don bata taba komawa inda ta fito sai ta assasa wani bala'in cikin gidan
''lafiya?''jabir ya tambayeta cikin kulawa
murmushi tayi wanda yafi kama da na yaqe ta girgiza kai''babu komai''
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺
▶5⃣
Babu sallama sam bisa tsarin maraqisiyya,don kaf gidan tafi kowa lalacewa,jamila ke rufa mata baya,a tsakar gida ta iske uwarta hadiza da 'yar kanzaginta huwaila,basu ga shigowarta ba sai yif kawai sukaji na warbar da akwatinta da tayi da zamanta jabar kusa da su
inna hadiza ce ta dafe qirjinta''na shiga uku ni dije,kada dai kice min yauma korokin yayi?''
fuska ta yatsine
''yau ba shi ya kore ni ba ni na taho,don na gaji da zama da matsiyaci direban babbar mota kuma mashayi''
''oh ni 'yar nan,auwalu matsiya cine''
''lamba daya''maraqisiyyan ta qarashe mata
huwaila tace
''aini na ma kasa magana,yara duka aure ya zama na tafashi kada,babu daya qwaqqwara?''
matsowa maraqisiyya tayi sosai kusa da su ta ma manta da tata matsalar''wai hadiza ni fa ban gane ba(haka suke kiran iyayen kansu tsaye)idanuna kamar wancan mujiyar nake gani da wani jikin wata qatuwar mota,ko gixo take min''
caraf huwaila ta kama''itace mana 'yar nan,kinga babarku babu yadda banyi da ita ba mu tashi tsaye ko malaman da mata ke shiga muma wannan karon mu fada amma tace bata da kudi,dame zata ji,da matsalolinku ko da kisan kudinta da take nema da qyar?kawai mu qyaleta tunda wancan karon hakanan taqi auruwa to wannan karon ma hakance zata faru''
''hadiza ai ranar biyan buqata rai ba a bakin komai yake ba,ku yanzu ko kunya bakwaji,ai abun kunya ne a tattarw da ku maryama ta auri irin mijin dai da na ganta tare da shi,wlh dukkanin alamu sun nuna mai akwai ne,yaranku suna zaune?,wadanda ma aka aurar din gamu cikin wahala?,kuma ita tahaye?,si wallahi inaaaa,zaman gida bai qarewa maryam ba,ku matso kuji''
shewa sukayi bayan sun tafa kamar wasu,sa'anni wanda yayi daidai da shigowar maryam din
''sannunku,maraqisiyya ya hanya?''babu amsa sai uban tsaki da taja kamar zata cire harshenta
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
washegari ta shirya tsaf don zuwa karbo dinkunanta da kuma yin sallama da uwar dakinta wadda take aiki a qarqashin katafaren kamfaninta nayin girke girke da shirya guraren biki,tayi sallama da maman ta,fito tsakar gidan
saiji tayi maraqisiyya na dura ashar,cikin takaici ta,juya don ganin da wa take,ita da hindatu ne ta,sirka ruwanta ta wanke kanta rabi zatayi wanka maraqisiyyar ta,sheqar mata ta,tara wsni don shiga nata wankan
''wannan banzar yayar taki ma bata isheni ba bare ke karan kada miya''
hindatu dama dake qullace da su tace
''dalla gafara can malama,banza a banza kawai,wadda ta kasa zsmsn gidan aurenta,yayar tawa kuma da,kike maganarta kuwa wallahi tako ina ta sha gabanki,aure kuwa nasan bazati irin naku ba auren jeka nayi ka,wanda dashi gwara babu''tofa baki yasan abinda zai fada baisan me za'a mayar masa ba
kamar ta zubawa maraqisiyya ruwan zafi ta,lsilayo wani uban ashar din''wlh zaki san kinyi da huwaila 'yar hadiza,auren da kike taqama ayishi mu gani''
''Allah ya fiki