Showing 30001 words to 33000 words out of 41188 words
dakai saika aureta kaji na fada maka tashi kaban gu" Alhaji Mukhtar ya karasa maganar a fusace.
Jin abinda yace yasa da sauri Hajiya Salmah dake gefe tana jijjiga kai ta tsomo baki batare da an bata izinin magana ba tace "to Alhaji ya za'ai Sultan da hankalinsa da tarbiyyar sa yarda ya aure ballagaza jakar mats bayan ga abinda ya faru wallahi Nabilah ta 6ata muku ahli ko zakaji haushi na saina fad'a ashe dama yaudararsa take bayan ta gama wulakanta kanta a titi gurin wani shegen wanin tambad'dd'an d'an iskan saurayi irinta d'an duniya mara asali tsintaccen kan hanya wa yasani ma ko ba iya shi kad'ai take kulawa ba dama can take saba akansa ne asirinta ya tonu gashi abun ba'kin ciki ubanta sananne yanzu ta zubar masa da mutunci ta 6ata masa suna a gari humm bama iya gari ko jiharmu ba a duniya gabadaya zance tunda yace zai yad'a videon wa yasan iya inda abin zai tsaya dan kawai anyi shari'a an kashe case d'in toni a guna bai kasu ba wallahi tallahi Alhaji kome zakai kaji rantsuwa ko? Wallahi Sultan bazai auri Nabilah ba har abada domin shi bai kasance d'an iska kuma fasi'ki kamar taba taje can ta samu irinta mazinaci ta aura..............................................
Tana rufe baki Alhaji Mukhtar ya d'auketa da mari wanda ba ita daya mara ba hatta Sultan saida ya zabura yana matsawa baya ya d'auka shi zai kawowa dukan itakam a gigice ta fara ihu tana tsalle-tsalle da kuka kamar yarinya ta fad'i a kasa harda burgima tana cewa.
"Na shiga uku na lalace Alhaji akan na fad'i gaskiya shine kake neman makanta ni wallahi tallahi kome zatai Sultan bazai auri Nabilah ba idan kuwa ka matsa saiya aureta ni saidai ka sake ni gara nabar maka gidan inyaso saika zauna da Nabilan amma nikam bazan ta'ba kallonta a matsayin surukata ba wallahi Allah ya sauwa'ke saida ta gama tallar kanta a titi sannan za'a takurawa d'ana a cusa masa ita salon ta saka masa cutar data kwasa a gurin tsinannun mazan da take bi".
Tunda Alhaji Mukhtar ya mi'ke ya mareta bai koma ya zauna ba harta gama maganganun ta sannan ya jinjina kai yana cewa "dama ko baki fad'a ba daga yau bazaki sake kwanar mun a gida ba ki tashi ki tattara dukkan abinda kikasan naki ne ki barmin gida na sake ki kai Kuma zan dawo kanka" yana karasa maganar yana nuna Sultan da yatsa cikin fushi kafin ya juya ya fice daga parlon kururuwa Hajiya Salmah keyi tana yage-yage kamar me ciwon hauka Sultan dake zaune jin abinda Alhaji Mukhtar d'in yace ya ta'be baki yana mi'kewa yaje ya dagata yad'au kwalinta ya mayar mata kanta yana kallon yadda hannun Alhaji Mukhtar ya fito d'arr a fuskarta har bedroom ya kaita ya d'ebo mata ruwan zafi tana d'und'uma fuskan nata shi kuma ya fara had'a mata kayanta a cikin akwatuna mi'kewa tai tana saka hijab d'inta ta ja trolley d'aya ta fita dashi zuwa harabar gida Sultan ne ya d'ebo mata sauran ya saka a mota ta shiga ya kaita gidansu acan wurinta ya zauna bai dawo gidan ba saboda haushin marin da Alhaji Mukhtar yayiwa mahaifiyar sa.
Su Rasheedat basu san me yake faruwa ba sun dawo daga anguwa da basuga Hajiya Salmah ba sunyi tunanin ko taje anguwa ne amma ganin shiru yasa abin ya basu mamaki sunyi kiran wayarta ta fad'a musu abinda ya faru d'azu tsakanin su har ya saketa yanzu haka tana gida gobe da safe suzo tana nemansu karaf a kunnen Alhaji Mukhtar ya shigo yaji me Hajiya Salmahn take cewa da sauri ya karaso a fusace ya kar'be wayar ya fasa ta sannan cikin murya me nuni da tsantsan 6acin rai yace musu duk wacce tsautsayi yasa ta kuskura taje inda Hajiya Salmah take sai ya d'au tsattsauran mataki a kanta.
🙇🏻♀️AYI HA'KURI YAU TYPING D'IN BA YAWA.
We will meet again nagode.
11~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil 'Kaiminah.
Manzon Allah s.a.w
Kaine me kyau ganinka yafi zama d'an aljannah a kyanka ne akai kyan matan aljannah gabanka kyau yana komawa mummuna ai anta ajamalul kal'ki nabiyur-rahma ya sibgatullahi ni kai min alfarma na ganka ko a barci baban Fad'imah ya shugaba cika mini burin 'kalbina.
YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨
🌹🌷🌹🌷🌹🌷🌹🌷🌹🌷🌹🌷🌹🌷
TYPING📲 Tue, Jan6/25 8:24AM
YUSRAH MUSA ABUBAKAR 🤘💯.
💕Minister Ashraf💕
💫ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫
🕳️Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake.
STORY WRITTEN ND EDITING
📝✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë.
12~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Kaidinah.
BISMILLLAHIR RAHMANUR RAHIM 📿.
💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦
PG____13&14
Bayan lafawar komai Alhaji Ashraf har gida yazo domin yayiwa Alhaji Tajuddeen jajja6in abinda ya faru amma sai yake masa wata magana wacce baiji dad'inta na musamman daya fahimci kamar Sultan ya 'ki amincewa da auren Nabilah har lokacin ya'ki yarda sharrine kallon Alhaji Tajuddeen yayi yana cewa.
"Kayi hakuri dan Allah Tajuddeen abinda ya faru naji kana cewa Sultan ko d'aga wayarka bayayi balle yazo kuyi magana akan Nabilah kardai kace min ya fasa auren ta meyasa ya fasa d'in"?.
Cike da damuwa Alhaji Tajuddeen ya girgiza kai yana cewa "ban sani ko fasawar yayi amma alamun 'karfi yana game 'kiba tunda har kaga take taken sa hakan yake nufi nikam bansan yadda zanyi da wannan al'amarin ba kaina gabadaya ya kulle" ya karasa maganar yana yana dafe Kai cike da takaici dafa kafad'ar shi Alhaji Ashraf yayi cikin rashin jin dad'in ganin irin kaddarar data samu abokin nasa yace. ..
"Subahanallahi Allah ya rufa asiri kayi hakuri Tajuddeen insha Allahu koda ace Sultan ya fasa Nabilah bazata rasa mijin aure ba balle bama fatan ya fasa d'in za'a san yadda za'ai ayi auren ni ka hadani da Sultan d'in ka tura min shi muyi magana dashi ko ka bani number wayarsa nasan abinda zan fad'a masa wanda komai zai wuce" kai Alhaji Tajuddeen ya girgiza yana sauke numfashi yace.
"Sultan yana da taurin kai tunda har yace ya ha'kura bazai dawo ba kome za'ai masa bazan ma 6ata bakina ba kawai ka manta da al'amarin insha Allahu Nabilah zanyi aurenta ko bada Sultan ba muje ka duba ta tana bedroom bata jin dad'i" ya fad'a yana mi'kewa shima mi'kewa Alhaji Ashraf d'in yayi yana cewa.
"Bata da lafiya meyasa baka kaita asibiti ba"?.
"A'a na kaita asibiti kusan sau uku wannan zuwan karshen ma har gado aka bata kwanan ta goma aka bata sallama muka dawo gida abun ne sai a hankali muje ka dubata".
"Ok" Alhaji Ashraf ya fad'a suna shiga bedroom d'in Nabilah a zaune suka sameta ta jingina bayanta da fuskar gadon ta zubawa guri d'aya ido hawaye ya ji'ke mata fuska shakaf girgiza kai Alhaji Ashraf yayi yana d'an sunkuyawa kad'an yace "sannu Nabilah ya jikin naki"? A hankali ta d'aga kai muryarta yana fita da'kyar sakamakon maganar data daina yi yanzu tace "da sau'ki Daddy".
"Allah ya sauwake Nabilah Allah ya baki lafiya".
"Amin" tace tana goge hawayen fuska tata kafin ta zame ta kwanta tare da rufe idonta kawai tayi tsam shiru Alhaji Ashraf yayi yana kallon fuskarta datai jawur ta rame sosai ji yayi wani irin abu ya tsirga masa na 6acin rai ganin irin halin data tsinci kanta juyawa yai yana kallon Alhaji Tajuddeen yace.
"Shikenan Allah ya rufa asiri muje Nabilah Allah ya sauwake in an jima zan turo doctor ya duba ki" kaita d'aga tana cewa "to Daddy nagode" "aha ba damuwa Nabilah Allah ya sauwake muje Tajuddeen" kallon Nabilah Alhaji Tajuddeen yayi ya kalli abincin breakfast d'in da aka kawo mata bataci komai ba harya bud'e baki zaiyi mata magana sai kuma ya kyale ya juya suka fita a bedroom d'in.
Kamar yadda ya fad'a ko awa biyu cikakkiya Nabilah batai ba doctor yaxo ya dubata harda ruwa ya d'aura mata sannan yayi mata allurar zazza'bi da magunguna sannan yace zuwa jimawa zai sake dawowa ya dubata ya fad'awa Hajiya Fatima cewa ta ri'ka zuwa tana dubuwa saboda kar ruwan ya 'kare ba'a cire da wuri ba to tace masa bata ma fita daga d'akin ba ta zauna har saida ruwan ya qare ta cire ta dau'ki d'ayan tasaka mata kafin ta mi'ke tana fita shiru Nabilah tai idanonta a rufe tun d'azu babu abinda take sai aikin tunani da tuna rayuwar su ta baya ita da Sultan bata ta'ba zaton Sultan zai zargeta ba koda ace da gaske ta aikata a tunaninta zai iya yafe mata da wani ne yace Sultan zai mata haka bazata yarda ba saida ya nuna mata taga zahiri da kanta nannauyan numfashi take fitarwa da'kyar ji take kamar an d'ora mata dutsi me nauyi a kirji har hanata numfashi mekyau yake har batasan lokacin da hawaye yake shararo mata ba tun tana tunani har tayi barci.
***Washe gari tana kwance a bedroom kamar yadda take kullum ta rufe dukkan jikinta da bargo d'akin shiru kamar ba halitta a ciki bud'o kofa Hajiya Fatima tai tana shigowa abinda ta fara kallo abincin data kawo mata tun na breakfast bata tashi tayi ba gashi yanzu karfe daya da rabi na rana cike da tsananin damuwa ta karaso tana yaye bargon da Nabilan ta lullu'ba dashi tana kallon ta dama abinda take tunani kenan ba barci take ba sai zazzafan hawaye da suke ambaliya a fuskarta idonta ya kumbura yayi jawur zama Hajiya Fatima tai a gefen gadon tana ta'ba jikinta jin wani irin mugun zafi kamar wuta yasa a firgice ta sake kallon fuskarta tana cewa.
"Nabilah".
Bata iya amsa mata ba saboda yadda muryarta tai nauyi sakamakon magana data daina yi sam a karo na biyu ta sake kiranta wannan karon runtse ido tayi da qarfi tana fashewa da ba'kin kukan damuwa wanda hatta Hajiya Fatima saida taji hawaye yana tarar mata a ido da sauri ta d'ago Nabilan tana tashinta zaune ta rungume ta cike da tausayi irin na uwa da d'a itama ta fara zubar da hawaye wacce irin kaddara ce wannan ta same su Allah ya kawo musu karshen ta............
D'agowa Hajiya Fatima tai tana goge mata hawayen fuskarta cikin lallahi tace "Nabilah kefa musulma ce kiyi ha'kuri ki dau'ki kaddarar ki kiyi kokarin cinye jarrabawar ki nasani wannan yaron ya cutar dake ya cutar damu yasa yaso 6ata mana suna a gari da yake bamu da alhakinsa Allah ya karemu daga sharrin sa dan Allah Nabilah kodan haka kiyi hakuri ki d'aure duk yadda kike ji a zuciyarki ki zama mai dangana a duk lokacin da wani abu ya sameki kamar irin wannan lokacin ki nuna kwarin gwiwa ki zama me jajircewa akan komai karki d'orawa kanki wata damuwa ki nutsu ki dawo cikin hankalin ki kinji Allah yana tare dake yasan komai zai musanya miki da mafi alkairi".
Nabilah tana shasshe'kar kuka tace "Mami damuwa ta yaya Sultan ne meyasa zaiyi min haka ina son sa amma kaddara tasa zargi ya shiga tsakanin mu har yana cewa shida aurena har abada Allah ya rufa asiri ya auri mazinaciya irina kiji fa Mami wai ni yake Kira da wannan sunan"? Nabilah ta fad'a cikin 'kunar rai tana sake fashewa da kukan ba'kin cikin tuna kalmar zina daya ambata a kanta.
Kai Hajiya Fatima ta girgiza tana cewa "na sani Nabilah Allah ne sheda ya san komai insha Allahu Sultan zai gane gaskiya zai gane yayi kuskure a lokacin dazai dawo yayi dana sani ke kuma sannan kinyi masa nisa domin wallahi Nabilah Nima ko yanzu Sultan ya dawo yace ya amince zai aureki bazan amince ba domin koda ya aureki hankalinsa bazai kwanta dake ba kullum yana cikin zarginki kawai kiyi hakuri Allah ya fito miki da wani na gari wanda ya fishi kyan hali wanda zai rikeki da mutumci yasan kimar mu" kai Nabilah ta d'aga cikin dauriya tace "insha Allahu Mami daga yau zan cire Yaya Sultan daga cikin zuciya koda ace hakan da zanyi zai zama silar rashin samun farin cikina Kuma bazan ta'ba waiwayarsa ba a cikin rayuwa".
"Yauwa Nabilah haka nake son ji Allah yayi miki albarka zan tayaki da addu'a in yarda ya yarda saikin samu mijin aure nagari san kowa 'kin wanda ya rasa ki cire damuwar komai ki manta dashi".
"Insha Allahu Mami zanyi kokarin hakan" Nabilah ta karasa maganar tana d'an yin murmushi kad'an wanda rabonta dashi harta manta mi'kewa Hajiya Fatima tai tana cewa "bari na kawo miko abinci me zafi kici domin wannan ya huce miki" ta fad'a tana mi'kewa ta fita shiru Nabilah tai zuwa wani lokaci ta dau'ki wayarta ta bud'e tare da binciko numbern Sultan ta zuba mata ido kamar shi take kallo daga baya taja tsaki tana yin blocking d'insa sannan ta aje wayar tana mi'kewa yuuu taji hajijiya na d'ibanta da sauri ta koma ta zauna tana dafe kan daya sara mata tun tana ganin duhu har idonta ya washe sannan ta sake mi'kewa tana nufar hanyar toilet domin tayo brush...................
✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë🌺
13~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Khaidinah.
See you tomorrow morning be with me at always my lover's.
DUTSE NEW WORLD 🌏 sabuwar duniya kuzo kuyi kallo dad'i yana Jigawa garin ilmi garin addini zaman lafiya Jigawa state.
TYPING 📲Wed, Jan7/24 11:34am YUSRAH MUSA ABUBAKAR✨🤘.
💕MÏÑÏSTËR ÄSHRÄF💕
WHATSAPP NO:+234 8160983083
yusrahmusa65@gmail.com
ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan haka taken mu yake.
💦Fatima Zarah Elham
Little Zarahn Aunty.
••• •••
Official
By=== === === ===
✍️ YÚSRÃHMS CE.
14~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Muttaqinah.
💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦
PG___15&16
Ganin kusan sati guda Sultan bai le'kota ba yasa Hajiya Salmah d'aga waya ta kirashi cewa yazo yanzu tana son ganinsa batai minti sha biyar da kiransa ba yazo tana zaune zama yayi yana kallon fuskarta da babu walwala ta mugun had'e rai tace.
"Sultan Alhaji ne ya hanaka zuwa inda nake kamar yadda ya hanasu Rasheedat ko kuma ra'ayin kanka ne yasa baka zo ba yau kwana kusan sha biyar"?.
Kaiya girgiza yana cewa "a'a Umma ba shibane kawai aikine yayi min yawa shiyasa ban shigo ba kiyi hakuri ba wani abu bane".
Jin abinda yace yasa Hajiya Salmah ta sauke ajiyar zuciya tana cewa "au aina d'auka ko akan Nabilan ne ya dakatar dakai daga zuwa guna yanzu a wanne mataki kuke kai dashi fatan maganar auren ta rushe"?.
"Ai Umma ki kwantar da hankalinki babu wannan maganar a yanzu yayi lallahin duniya yayi fad'a amma nace bazan aureta ba ni yanzu bana sonta Kuma bazan 'kara sonta ba".
D'adi ne ya cika Hajiya Salmah harda sakin murmushi tana cewa "yauwa Sultan sakyau abinda nake son ji kenan kada ka kuskura ka tausaya mata ko mutuwa zatai ba asibiti aka kaita ba ko pharmacy ne akanta kar kaje dubata karka tausaya Mata kome zasuyi ko suce maka ka share su hatta Alhaji karka saurare shi kana kallo akan haka ya sake ni ko? to wallahi matukar ka auri yarinyar nan Nabilah saina tsine maka kaji dai na fad'a maka".
"Karki damu Umma nifa na daina sonta babu ruwana da ita yanzu meye had'ina ita dahar zanje inda take maganar Abba zai tilasta ni a'a domin yayi min fad'a harya gaji ban saurare Shiba balle naje d'in kinga kuwa ai mun raba hanya yanzu harya ha'kura ya daina cemin komai".
Kai Hajiya Salmah ta jinjina tana cije lips tace "yauwa d'an albarka kaga yanzu ka rabu da mangoro ka huta da 'kuda da ka'ki ganewa kullum ina fad'a maka amma sonta ya rufe maka ido sai yanzu da kanka ya gwaro da bango ka gane gaskiyar ita 'yar iska ce ka rabu da ita ta ruwan sanyi yanzu abinda nake so dakai zan kira 'kawata Hajiya Suwaiba zamuyi magana akan 'yarta Hajeer jiya ma tazo gurina ta gaisar dani nasan zaku dace kuma yarinya ce kyakkyawa kana ganinta zakaji tayi maka zan sanar da Hajiya Suwaiban duk yadda mukai saika shirya kaje ka ganota ko"?.
Kaiya d'aga yana cewa "ok shikenan Umma ba damuwa yadda kukai dasu ina jira kisa Aunty Atikah suje su kar'bo min lefe na daga gidan can Kuma koda jan baki ta d'auka bazan yarda ba saita biyani".
Murmushi Hajiya Salmah tai cikin jin dad'i domin tasan tunda yace ba damuwa bazai bata matsala ba kuma dama idan ta fad'i magana baya musa mata sai akan neman aurensa da Nabilah ne yaso bujire mata kaita jinjina tana cewa "karka damu lefe yana nan tun kusan kwana ashirin nasa an kar'bo min yana gurina na kaishi gidan Hajiya Falmata danaga ka daina xuwa inda nake ma na d'auka ko dalilin karbo akwatunan da nasa akai ne Alhaji yaji labari ya kiraka yayi maka zagin tsamar nama" kaiya girgiza yana mi'kewa yace...
"A'a inaga baisan kun kar'bo ba kamar yadda nima ban sani ba kuma suma maybe basu nuna ba da ace ya sani da yanxu ya Kira ni akan hakan bari na koma Umma saina dawo duk yadda kukai da wancan yarinyar zanzo jibi sai naji komai" dad'i daya gama cika Hajiya Salmah ji take kamar ta tashi ta taka rawa tace.
"To Sultan Allah yayi maka albarka na tabbata bazan yi maka xa6en tumun dare ba zakaji dad'i matukar dad'in zama da Hajeer ba ruwanta yarinya bata da hayaniya ba kamar wancan fitsararriyar yarinyar ba Mai idon ganin gari".
"Ok Umma na tafi" ya fad'a yana aje mata kud'i mi'kewa tai tana masa rakiya har harabar gida kafin ta dawo murna da farin ciki ya gama cikata jikinta har 6ari yake ta kira Hajiya Suwaiba tana ce mata gobe zata shigo anguwarsu akan maganar Hajeer da Sultan.
Husnah bata gari tun bayan lafawar hayaniyar abinda Sir Ahmad yayiwa Nabilah ta tafi Abuja gidan 'kanin babanta kusan watan biyu tai kafin ta dawo duk tsawon wannan lokacin saurayin ta Suraj bai ta'ba kiranta ba idan ta kira layinsa baya tafiya dalilin haka yasa bata karasa hutunta ba ta dawo Dutse a ranar data dawo ta dau'ki aron wayar Hajiya Sadiya ta saka numbar sa ta kirashi abin mamaki sai taji kiran