Showing 294001 words to 296092 words out of 296092 words
ji ba bai gani ba, Yazid yafi ƙarfin wattanni baya rintsawa, tamkar zan haukace, haka na dinga faɗuwa da tsohon ciki Mummy Why?"
Khalil kansa jikinsa rawa yake yi, sosai hawaye ke zuba daga idon Daddy.
Ya ce "Ku je dan kanku, Allah ne kawai zai saka mini cutarwar da kuka yi mini, na barku da Allah.
Sosai Amina jikinta ya cigaba da rawa, Daddy ya ɗagata ya ce maza Khalil ya je ya fito da mota.
Hajiya Zainab kuwa ɗora hannu ta yi a ka, ta fashe da kuka tana nanata "Innalillahi wa innalillahi raji'un, kun cuceni Allah ya isa ban yafe ba".
Ganin ba abin da aka yi musu, ya sanya sum-sum, Hajiya Turai da Salma suka fice daga gidan.
Hafsa kuwa zuruuu ta yi, abin yana ɗaure mata kai.
Kuka Mummy take tana wani irin gunji, ba ta taɓa zaton su Turai za su yi mata haka ba.
Fadila da ta ɗan farfaɗo tashi ta yi ta ce wa Yazid ya bar falon da ita.
Hafsa ta ɗau jariran, ta bi bayansu.
Tare da Hajara aka tafi kai Amina Asibiti, Daddy ba magana sai kuka kawai.
Suna zuwa Asibiti, aka ce cs za a shiga da Amina da gaggawa, dan jininta ya hau ba za a bari ta yi naƙuda ba.
Nan da nan Khalil ya ɗau Hajara suka dawo gida, ya sanar da su Fadila abin da ake ciki, aka kwashi kayan Amina na haihuwa suka nufi Asibiti.
Daddy ya ce ba za a kira su Inno ba, sai an gama aikin.
Awa ɗaya da rabi, aka fito da jarirai maza biyu, an yi mata aikin.
Daddy sai ya rasa me zai yi, Amina firgici ne ya sanya jininta hawa, ga baƙin ciki ga farinciki.
Ba wanda ya kuma bi ta kan Hajiya Zainab, sai magariba, ya zo ya tarar da ita a sume a sashinta.
Hankali a tashe ya ɗauketa zuwa Asibitin da Amina take, sai dai babu wanda ya san musababbin suman nata.
Hajiya Turai da Salma kuwa, suna tafe a motar Hajiya Salma, suna faɗa, tana yiwa Turai masifar dan me zata tona musu Asiri.
Aikuwa Turai ta hauta da bala'i, tana cewa bata san me take ji a jikinta bane, ji ta yi idan ba ta faɗa ba zata mutu.
Suna wannan masifar, Tirela ta taho, garin su kauce mata motar ta kifa, Hajiya Turai ko shurawa ba ta yi ba.
Ahalin Daddy da basu san wainar da aka toya ba, sai labarin haihuwa da suka ji, suka yi ta murna suna cewa arziƙi ya sauka a gidan Alhaji Ahmad.
Khalil ne yake zuwa duba Mummy, Sai Yazid.
Yazid ya yi ta yiwa Fadila faɗa a kan lallai kar ta ce zata ƙullaci Mummy, dan ba wanda baya kuskure a rayuwa.
Da Hajiya Zainab ta sake farkawa, ta ga Fadila da Yazid, ga Hafsa ga Khalil a tsaye a kanta, sai ta fashe da kuka tana faɗin "Dan girman Allah ku yafe mini, kuma ku rufa mini asiri, ina miji na in nemi yafiyarsa ina Amina, ashe abin da take gaya mini gaskiya ne, Fadila ku yafe mini".
Yazid ya ce "Mummy duk sun yafe miki, Daddy ma zai zo wurinki in sha Allah, Amina an mata aiki ta haifi yara maza biyu"
Ta kalli Yazid ta ce " Ɗan nan dan Allah ku yafe mini, na san ba zan tsawon rai ba, likita ya tabattar mininda shaye-shayen magungunan hausa barkatai da na dinga yi, wanda ban san da me aka haɗasu ba ya sanya ƙodata ɗaya ta gaza, dan Allah ku yafe mini, kar na mutu da hakkinku".
Fadila ta fashe da kuka, ta rungume Mummy, tana Cewa "Mun yafe miki Mummy, ba zaki mutu yanzu ba, dan Allah ki daina faɗar haka".
Fadila ta tashi da sauri, ta koma ɗakin da Amina take kwance, Daddy na zaune a gefe, da jarirai a hannunsa. Fadila ta zube a gaban gadon Amina ta riƙe hannun Amina ta ce "Dan Allah Amina ki yafe wa Mummy, kin san wani abun ba laifinta bane ba, Daddy dan Allah ku yafe mata, likitoci sun tabattar da Mummy ta gamu da renal failure".
Waro ido suka yi gaba ɗaya, Amina duk da halin da take ciki sai da ta tsure ta ce 'Ciwon ƙoda kuma?"
Fadila ta jinjina kai tana kuka. Tashi Daddy ya yi ya fita, dan tun da aka kawo Hajiya Zainab bai leƙa ya ganta ba, saboda ya sha mamakin abin da ya ji ta aikata ba tare da ta musa ba.
Yana zuwa ya tarar da ita, ta rirriƙe Khalil tana kuka.
Tana ganin Daddy ta saki Khalil, tana miƙawa Daddy hannu tana kuka.
Daddy ya ƙarasa kusa da ita ya zauna, ya kalleta ya ce "Wane likitan ne ya ce kina da wannan ciwon?"
Cikin kuka ta ce "Likita ba zai yi ƙarya ba, ƙodata ɗaya ta samu matsala, Ahmad na san na cutar da kai, dan Allah kayi haƙuri na san ba zan yi tsawon rai ba, na yi dana sanin abubuwan da na aikata, dan Allah ka yi haƙuri Ahmad ka yafe mini".
Daddy ya dubi Khalil ya ce "Ka je ka zo mini da likitan da yake dubata".
Jiki a sanyaye Khalil ya fita daga ɗakin, kasancewar Amina ta fara takawa, dan kwanaki uku kenan da yi mata Cs, hankali a tashe ta shigo ɗakin da Mummy ke kwance ta riƙa hannun Daddy tana kuka, amma ya ƙi magana sai Hafsa da Yazid da kuma Fadila.
Amina ta ƙarasa gaban gadon tana faɗin "Sannu Hajiya, wai ciwon ƙoda ni ai ban san a nan Asibitin kike ba".
Duk da wani irin kishi da yake tasowa Hajiya Zainab, a kan Amina, amma ta ga ƙoƙarin Amina da ta zo dubata.
Likita ne ya shigo, suka gaisa da Daddy, Daddy ya tambayeshi meke damun matarsa.
Nan likita yayi masa bayanin cewar, magunguna da take sha ba bisa ƙa'ida ba, ya sanya ƙodarta ɗaya ta taɓu.
Amma idan aka bi ƙa'idojin da zasu saka, zata iya rayuwa da guda ɗaya.
Hajiya Zainab ta riƙo hannun Amina ta ce "Ba wani tsawon rai da zan, ni na san mutuwa zan yi, dan Allah ki yafe mini, na san kema na cutar da ke, ki kuma saka baki ya yafe mini dan Allah".
Amina ta kalli Daddy ta ce "Daddy, dan Allah do something, dan Allah ka yafe mata.
Fadila ma kuka take yi sosai da sosai.
Daddy ya yi ajiyar zuciya ya ce "Shikenan, Allah ya bata lafiya, ni yanzu fatana ta samu lafiya Allah ya yafe mana baki ɗaya".
Yazid ne da suka bashi tausayi, ya ce "Allah ya saka da alheri Daddy, Allah ya ƙara girma.
Fadila ta rungume Daddy tana yi masa godiya.
Ita ma Hajiya Zainab godiyar ta dinga yi, ta ce "A bani jariran na gansu, Hafsa ku yafe mini dan Allah"
Hafsa ta ce "Bakomai Mummy" cikin murmushi ta sauko da jaririyar ta miƙawa Mama, Fadila ma ta ce Mummy bari na karɓo miki Hidaya ma.
Ta fita da sauri, ta koma ɗakin da aka kwantar da Amina, Inno tana goye da Hidaya, Hajara kuma na bawa jariran madara.
Fadila ta ce "Inno, Mummy ce zata ɗau Hidaya"
Inno ta yi murmushi ta ce "To muje in sake duba jikin nata".
Fadila ta ce "Yauwa Hajara taho da 'yan biyu ma".
Haka suka ɗunguma zuwa ɗakin da Mummy take.
Duk suka jere mata yaran, tana kuka ta dinga shafa kan yaran tana kuka tana su yafe mata.
Amina ta ce "Hajiya dan Allah ki daina kuka, komai ya wuce tun da dai kin fuskanci gaskiya, Allah ya yafe mana baki ɗaya ya baki lafiya".
Gaba ɗaya jikin Hajiya Zainab yayi sanyi, duk motsi ta dinga neman afuwa kenan.
Mutanen da suka sake dawowa sunan Amina, sun yi mamakin ganin Hajiya Zainab duk ta rame tayi sanyi.
Ammi su Hajiya Maryam, da Azima da 'yan makarantar su Amina duk sun zo suna, kuma sun yi wa Amina alkhairi.
Hajiya Salma dai, ba ta mutu ba, sai dai lakarta ta taɓu, ba zata iya yiwa kanta komai ba, sai dai a kwantar a tayar.
Bayan sunan jariran Amina, Fadila ta ce zata koma gida, dan jikin Mummy ma da sauƙi sosai da sosai.
Amina ta cigaba da lallaɓa Daddy, tana nuna masa Cewar Hajiya Zainab ta saduda, dan haka yayi haƙuri komai ya wuce.
Allah ya sa Amina ta shawo kan Daddy, ya biya kuɗi aka fita da Hajiya Zainab Indiya, domin cigaba da kula da lafiyar ta.
Daddy ya bawa Yazid aiki a kamfaninsa da zai buɗe na kwangila a Kano.
Yazid dai ya karɓa ne kawai, amma ya barwa kansa cewa zai cigaba da lalaubawa idan ya samu wani aikin zai tafi, baya son ace Daddy ya dinga yi masa komai, dan yana auren 'yar sa.
Still Daddy ya kuma bawa Abdul aiki a kamfanin, dam ba zai manta alkhairin sa ba shima, a lokacin ya auri Yusra ma.
Babban muƙami Daddy ya bawa Yazid, ga zuwa makaranta, Yazid ya zama busy sosai, ya nemawa Fadila School of Nursing, cikin ikon Allah kuma ta warke daga ciwon iskokai.
Baba Uwani kuwa, matar Baban Yazid ita ma ta rasu tuni, amma Yazid bai yadda ya yanke alaƙa da 'yan uwansa gaba ɗaya ba.
Bayan Hajiya Zainab ta dawo daga indiya, jikinta yayi kyau sosai da sosai.
Daddy ya sakata a gaba, zuwa Dutse ta dinga bawa mutanen da ta ɓatawa haƙuri ciki har da danginta.
Ta yi nadama sosai da sosai, tayi mamakin zaluncin da su Hajiya Turai suka yi mata.
Tana ji tana gani dai, Amina ta ƙwace mata gida, sai abin da Amina ta ce shi ake yi, sai dai Aminan na iya ƙoƙarin ta wurin yi mata adalci.
Abubuwa suka ƙara yiwa Amina yawa, ga 'yan biyu watanninsu takwas ta kuma samun ciki, an sha daru sosai dan cewa ta yi zubarwa za tayi, ita ga karatu, ga kula da yara ga kuma ciki.
Sai da Daddy aya zazzare mata ido sannan ta haƙura, ga laulayi ga makaranta, dan ma Kusan kodayaushe twins suna wurin Hajara ko Hajiya Zainab.
Ganin yaran na ɗebe mata kewa, Fadila ma ta zo ta dire mata Hidaya ta tafi makaranta, suka mayar da ita tamkar Nanny.
Mijin Hajiya Salma ya tsallake ya je yayi wani auren ya barta, ɗanta Salim ya tattara ɗan abin da take da shi, ya dinga facakarsa, suka barta a wahala ga jinya.
Bayan Yazid ya kammala makaranta, ya samu scholarship a Saudiyya, a lokacin Fadila ta gama school of Nursing ita ma, ya tattara ta da 'yarsa suka bar ƙasar. Cikin ikon Allah yana karatu a ƙasar ya samu aiki, ya sake mayar da Fadila makaranta, ya buɗe wa Hajiyarsa wurin sana'a a Nigeria.
Sai da suka shekara Bakwai a Saudiyya, sannan suka dawo Nigeria, Fadila ta kuma haihuwar ɗa namiji, Amina kuma ta kuma haifar maza biyu da mace ɗaya.
Yazid ya samu alkhairi sosai zamansu a Saudiyya, ya dawo ya samu aikin yi a Nigeria, ga gefe guda Daddy na ta sake janyo shi cikin harkokinsa, dan so yake ya sakar musu shi da Khalil shi kuma ya huta.
Kwatsam an gayyaci su Yazid za su yiwa wasu malaman jami'o'i wurin screening, waɗanda za a tura su wani course ƙasar waje.
Babu tsammani har da Kankiya a cikin waɗanda Yazid zai tantance, Kankiya ya rikice, ya ƙadarra Yazid ba zai bari yayi nasara ba, amma ya ga Yazid ya girmama shi, yana nuna wa abokan aikinsa ai wannan malaminsa ne.
Kankiya duk kunya ta kama shi, ya dinga neman yafiyar Yazid, a nan Yazid ya sanar masa ya auri Fadila har da yara.
Kankiya ya taya shi murna sosai, Yazid ya yi masa tantancewar sa cikin mutunci da girmamawa.
Haka rayuwa ta cigaba da gudana, dukkanin ahalin suka cigaba da rayuwa cikin farinciki, sai dai Hajiya Zainab ta ƙarasa rayuwarta tamkar mujiya, dan Mutane ba su daina zunɗenta da bada labarin mugun halinta ba.
TAMMAT BIHAMDILLAH, ALHAMDILILLAH, ALHAMDILILLAH, ALHAMDILILLAH.
A NAN NA KAWO MUKU ƘARSHEN WANNAN LITTAFI, NA GABA DA GABANTA.
INA JINJINA TARE DA MIƘA SAƘON GODIYA TA GA MASOYAN ALƘALAMIN AYSHERCOOL BARKA DA JUMURIN BIBIYAR LITTAFINA.
JAMA'ATA NA WHAT'S APP, MUTANEN AREWABOOKS, WANDA SUKA BANI KYAUTAR DATA DA SAURANSU DUK INA GODIYA, ALLAH YA BAR ƘAUNA.
WANDA SUKA SAI BOOK ƊINA SUKA FITAR MINI BANYA BANYA.....🙄 INA SAI BABBAN BOOK AKE FITARWA, AMMA KUKA SAYA KUKA FITAR MINI KUN KORI GABA, PAID BOOK NA GABA B.S B.S😒😒😒
IN SHA ALLAH LITTAFIN GABA GABANTA ZAI ZO A YOUTUBE CHANNEL ƊINA TA COOL HAUSA NOVELS NA BAYAN SALLA IDAN ALLAH YA KAIMU.
GA AZUMI YANA GABATOWA, IDAN ALLAH YA SA MUNA DA RABON GANI, ALLAH YA SANYA MU CIKIN 'YANTATTUN BAYINSA.
DAN ALLAH WANDA YA TUNA DA NI A CIKIN WANNAN WATAN MAI ALFARMA YA SANYA NI A CIKIN ADDU'A PLEASE 🙏🙏🙏
DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA A KAN DUKKAN BOOKS ƊINA.
GA LAMBAR WAYATA ANA IYA TUNTUƁATA KAI TSAYE.
08081012143
AREWABOOKS AYSHERCOOL7724
WATPAD AYSHERCOOL 7724
KAR A MANTA DA SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊINA.
SAI MUN HAƊU A SABON BOOK IDAN ALLAH YA KAIMU BAYAN SALLA.
MEENA VIP GROUP HAUSA NOVEL DOCUMENT for more information contact on
+234 7014979567
WhatsApp ONLY