Showing 255001 words to 258000 words out of 296092 words
halinta, kayi haƙuri lokaci na nan zuwa da zan faɗi in da take"
Khalil ya ce 'Shikenan Daddy. Na kammala aikin da ka sakani, kuma nima a satin nan zamu koma Abuja in sha Allah"
Daddy ya ce "Masha Allah, Allah ya dafa a gaishe mini da ɗiyata".
"Za taji in sha Allah, a gaida Antyn"
"Zata ji in sha Allah"
Baba Hassan tamkar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha, saboda murnar ya ji zai je Saudiyya, masu taya shi murna nayi, masu yaƙe na yi, dan zukatan su Baffa babu daɗi zinƙire yake da hassada a kan yadda Allah ya ɗaga 'yarsa duk da suna cin arzikinta, dan kusan duk wata kayan Abinci da kuɗi na tafe, kuma tare da su ake ci amma basa gani.
Yazid ya kammala sallolin darensa kenan, da addu'oi, Kamar yadda ya saba ya ɗora hannunsa a kan Fadila, yayi ta mata addu'a sannan ya kwanta.
Ya kwanta babu da daɗewa, yaga Fadila ta tashi, fitsari ya tasheta, har ta nufi banɗakin cikin ɗaki, amma ta fasa saboda tsoro take ji, saboda ba wuta gashi bata san in da fitilarsu take ba, dan haka ta tafi banɗakin tsakar gida.
Shi ma kasa shiga banɗakin tayi, ta tsuguna a tsakar tayi fitsarinta, ta tashi tana wanke ƙafarta, tayi arba da wata mage ɗirkekiya.
A guja ta ƙwala ihu ta shiga ɗaki da gudu, ta faɗa kan Yazid tana rirriƙe shi.
A rikice ya ce "Lafiya menene?"
"Mage ce" ta bashi amsa.
"Kuma sai ki dinga gudu haka? Maimakon kiyi addu'a"
Cikin shagwaɓa ta ce "Mhmmm ni tsoronta nake ji, dan Allah ka tashi ka koreta, ka rufe mana ƙofa karta shigo".
Ya ce "A'a nima gaskiya tsoronta nake ji"
"Dan Allah ka tashi"
Shima ya shagwaɓe murya ya ce "Ni gaskiya tsoronta nake ji, kuma naga kamar ta shigo ma"
Sake ƙanƙame shi tayi ta na jin tsigar jikinta na tashi, saboda bata son mage. Hakan ya bawa Yazid damar nufin cikar kuɗirinsa a matsayinsa na mijinta.
Yadda hannunsa ke yawo a jikinta, ya sanya ta sake shiga tsoro da firgicin gaske.
Kamar wadda aka cirewa kuzari, ta kasa kayaɓus balle tayi yinƙurin hana shi, sai da taji abin nasa ya wuce tunaninta.
Lokaci guda burkin sarrafa kansa ya ƙwace masa, sai da ya kai ga samun abin da zuciyarsa ta makance a kan samu.
Fadila ba ta jin haushin Yazid kamar yadda ta ji haushin kanta ba, tana jinjina sokonci da wautar da tayi, na barin Yazid yayi awon gaba da abu mafi daraja a tare da ita, yanzu sai ya ce dama abin da take so kenan.
Haka ya taimaka mata ta kintsa, yana jiran kwandon bala'in da zata sauke masa, amma tayi masa shiru ba ta ce komai ba.
Washegari da safe ko abin karin da ya bata bata karɓa ta ci ba, ya gama surutansa da rarrashinsa amma ko kallonsa ba tayi ba.
Gashi yana da jarrabawa ƙarfe sha ɗaya na safe. Ba yadda ya iya haka ya fita ya barta.
Yauma yarinyar nan Maryam ita ta shigowa Fadila, Fadila ta ji daɗin zuwanta, tayi mata shara da wanke wanke.
Yau Yazid saboda sauri, ko gyaran gidan bai yi ba, ya ƙare a zaman rarrashinta.
Da kanta ta shiga bedroom ta tattare kayansa da ya cire ya ajiye, ta kwashe nata ma, ta gyara ko ina, tunawa tayi a gida wataran a falo ma take yada komai, sai dai a kwaso a biyota da shi, bata son ƙazanta amma bata iya gyara sai da ayi mata. Haka nan duk da jikinta babu daɗi ta gyara ɗakin.
Ta dawo ta ɗauko musu abincin safen da ya dafa, suka ci ita da Maryam.
Suna ta hira har sha ɗaya, ta lura yarinyar a nutse take, a hirar tasu ne ma, yarinyar take gaya mata Yazid malaminsu ne a makarantar dare, har take bata labarin 'yan ajinsa ajin sauka sunce zasu gidansa, da irin kirkin Yazid, ko a makaranta.
Fadla ta ce "Suwaye 'yan ajin saukar?"
Maryam ta ce "waɗan suka yi sauka, suka kuma dawowa?"
"To ya za ayi maza su zo gidana?"
Maryam ta ce "Ai ba maza bane, 'yan mata ne fa manya, suma suna koyarwa, ai zasu zo ki gansu".
Haka nan Sai Fadila ta ji babu daɗi, har da ɗan ɓata rai.
Can Maryam ta ce 'Anty, ba zaki ɗora girki ba?"
Fadila ta ce "Kin iya girkin ne?"
Maryam ta ce "Eh ina yiwa Antyna"
Fadila ta ce "Ina mamanki?"
"Ta mutu, shi ne yayata ta ɗaukeni"
Tausayinta ya kama Fadila ta ce "Allah sarki, Allah ya jiƙanta to me kika iya dafawa?"
"Duk abin da kike so na iya"
"To tashi mu je Kitchen ɗin"
Fadila saboda zama da Yusra, ta iya wasu abubuwan a girki, dan haka ta wayance, tana ganin yadda Maryam ke girkin, saboda ko bakomai yakamata Yazid ya dinga hutawa, ta dinga rage masa ayyuka.
Taliya suka dafa da miya, sai azahar lokacin islamiyya sannan Maryam ta tafi, Fadila ta rasa me zata bata, dan yarinyar tana taimaka mata, alhalin ba wanda ta shiga a layin ta yiwa sallama ta ce gata ta tare, ba Yadda Yazid bai yi da ita ba, amma taƙi zuwan.
Yazid ya sha mamaki da ya dawo, ya shiga Kitchen amma ya tarar da abinci. Ya dawo don ya tambayeta, duk da tunda ya dawo harara ce kawai take shiga tsakaninsu.
"Sweetheart, a ina muka samu abinci".
"Kaje can ka nemi Sweetheart ɗin ka"
"To Allah ya baki haƙuri, waye ya kawo mana abinci?"
"Dafawa nayi" ta bashi amsa.
"Wow, inyee ashe ta iya girki babyn"
Zumɓura baki tayi ya shareshi.
Duk yadda ta so ta basar da Yazid, amma ya zuba abincin, ya dinga zuba mata santi, ta ji daɗin yabawar da yayi, amma ta shareshi dan haushinsa take ji.
Tashi tayi ta koma bedroom ta kwanta abinta.
Yau da daddare ta tubure ba zai hau mta katifa ba saboda ƙarfin hali, falo ya koma ya ƙyale mata ɗakin ma gaba ɗaya.
Tayi juyi ya kai sau biyu, amma Yazid na kan sallaya yana ibada.
Ita yawan ibadar Yazid har mamaki yake bata.
Ji tayi yayi shiru da karatun da yake yi, ya tattara hankalinsa a kan wani abu, da bata san ko menene ba.
Ƙasa ƙasa taji Kamar Yazid kuka yake yi.
Kasa kwanciyar tayi, har ta fito ta je daf da shi, bai sani ba. Hannu ta saka ta zare hoton da yake hannunsa.
Wata kyakkyawar Bafulatana ce a jiki, mai matuƙar kyau na ɗaukar hankali.
"Wacece wannan?" Ta jefo masa tambayar.
Shiru yayi ya zuba mata ido, ya kasa furta komai.
Littafin kuɗi ne, ku tuntuɓeni domin saya.
Ayshercool
08081012143LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143
76
Cikin ƙosawa ta sake cewa "Ka yi
magana mana, ka yi shiru kana kallona"
Ya saka hannu ya karɓi hoton daga hannunta, yana ɗan jujjuya shi sanyaye ya lumshe idanunsa sannan ya buɗe su ya ce "Wato Fadila, duk wanda ya rasa uwa yayi kuka. Shiyasa duk da ina murna na aureki, amma bana jin daɗin nesanta ki da Mummy da Daddy yayi ba. Ita uwa wata kyauta ce daga Ubangiji da bata da madadi.
Inna wuro kenan, ni kuma ina kiranta Innata. Kamar yadda na samu labari Bafulatana ce ta riga a can wani ƙauye a Jalingon jihar Taraba. Galibinsu fulani ne, sai dai galibinsu ba musulmi bane ba, rigar su Innarmu musulmi ne sai dai basu damu da ilimin addini ba, ba abin da suka sani sai kiwo da kuma tallan Nono. Inna tana da yayye mata biyu sai kuma ita ta uku, suke nan a wurin mahaifinsu. A wurin tallan Nono ne da suke shiga garin Jalingo yi Inna ta ci karo da ilimin addini ta gane Cewar a duhu suke zaune na jahilci, addinin ma basa gudanar da shi yadda ya dace a rigarsu dan haka ta ɗau ragamar neman ilimi.
Idan taje tallan Nono, sai ta zauna cikin makarantu ta ɗau karatu. A lokacin babu wanda ya damu da sai an saka a makaranta kan kaje, ta samu wata makarantar islamiyya tana zuwa.
Ta ƙuduri aniyar yin karatun addini mai zurfi. Domin ya zama babbar malamar ita ma ko dan ta dinga wayar da kan 'yan ƙauyen su. Sai dai wannan buri nata bai cika ba, mahaifina ya haɗu da ita, lokacin da suka je rigarsu shi da wani abokinsa sayen shanu.
Kasancewar dama ba karatu suke yi ba, kuma 'yan uwanta duk da wuri ake yi musu aure, ya sanya ita ma mahaifinsu ya amince da mahaifina a kan ya kawo kuɗin aure a sanya ƙanƙanin lokaci.
Mahaifina yana da mata biyu, mahaifiyata ce ta uku, uwar gidansa Baba Uwani, sai kuma ta biyun Baba Hanne. Babban abin da ya damu mahaifiyata shi ne burinta na karatun addini babu lallai ya cika.
Bayan ta auri Mahaifina, ya tafi da ita garinsu da yake cikin Ranon jihar Kano ta tare a gidansa da ke ɗauke da matansa da kuma yaransa biyar da suka kasance duk mata.
Kalata ta wurin uba tana nan a raye, amma a lokacin bata garin Rano, tana wani wurin tana aure bayan rasuwar kakana, dan haka babana yana da yayye biyu maza, sai ƙanwarsa mace.
Mahaifiyata na da matuƙar haƙuri da kawaici, mabaifina yana sonta sosai da sosai, hakan ya sa ta bijiro masa da son ta koma makaranta, amma ya ce bai yadda ba abin zai zama surutu a gari.
Tun da mahaifina ya auro mahaifiyata matansa suka sakota gaba, suke nuna mata ƙiyayya a fili. Idan baya nan suyi ta sakata aiki mai wahala. Mahaifina tsayayyen mutum ne a kan gidansa, yana da rufin Asiri sosai a garinmu an san shi sosai yana da kuɗi, yana dillancin dabbobi har zuwa kudu da maƙotan Nigeria, gidanmu ba a yunwa ko rashin sutura, sai dai ba a damu da ilimi ba sam.
A na haka mahaifiyata ta samu juna biyu, sai dai ba wanda ya sani, saboda ba ta laulayi daga ita sai mahaifina suka sani.
Babu wanda ya farga mahaifiyata na da juna biyu, sai ganinta kawai suka yi tana naƙuda. Ta yi doguwar naƙuda bata haihu ba, Babana ya ɗauke ta zuwa Asibitin cikin gari, dan duk da rufin Asiri na mahaifina yana cikin karkara da iyalansa.
Mahaifiyata ta haifi ɗa namiji, Mahaifina yayi murna sosai da sosai, zai samu magaji, mahaifiyata kuma murnar da take yi, shi ne Allah ya cika mata burinta a kan yaron nan, ya zama masanin addinin Muslunci sosai.
Tun da suka koma gida sai ƙananan maganganu, mussaman da suka ga yadda mahaifina ke ta rawar kai a kan haihuwar.
Ranar suna mahaifiyata ta roƙi mahaifina ya saka mini suna Yazid.
Mahaifina bai sani ba, sunan wani babban malami ne a cikin garin Jalingo da Innata ke zuwa masallacin sa jim wa'azi.
Son da yake yiwa mahaifiyata ya sanya shi ya amince, ya sanya mini suna Yazid.
'yan garinsu mahaifiyata sun zo, duk da fulani ne amma wasunsu ba musulmai bane ba suka zo taron suna, mahaifina sai da ya yanka manyan raguna da saniya, aka dinga ci ana rabar da naman a garin, ko baka je suna ba, abu ne mawuyaci ka kasa cin naman da aka yanka da kuma abincin suna.
Matan Babana suka kuma mahaifiyata a gaba, abin mamaki a wannan karon har da facaloli, suna mata gorin wai 'yan uwanta maguzawa ne.
Mutanen gari suka dinga yi wa matan mahaifina Allah sarki, duk wannan wahalar yaransu mata ne, lokaci ɗaya daga zuwan mahaifiyata ta fara haihuwar namiji, idan babana ya mutu ba zasu samu komai ba.
Kasancewar mahaifiyata ba sawa ba fitarwa, ya sanya bata damu da abin da suke yi ba, sannan bata nuna kara a kaina kasancewata ɗan fari.
Ba abokan zaman mahaifiyata ba, hatta 'yan uwana yayyena, suke kishi da ni, basa son na raɓesu.
Tun ina ƙarami mahaifiyata ke mini kirana da Gwani Yazidu magajin malam.
Bayan na fara tasawa, ɗan abin da mahaifiyata ta sani na ilimin addini ta fara koya mini, hatta magana tayi iyaka ƙoƙarin ta bakina ya buɗe da la'ilahailallah. Irin koyon maganar nan na yara, da bisimilla istigfari ta dinga koya mini bakina ya buɗe da su, bana zuwa ko ina ba wanda yake ɗaukata kullum ina tare da mahaifiyata hakan ya sanya nayi saurin iyawa.
Shekaruna uku a duniya, Innata ta matsa a kan lallai mahaifina ya kaini makaranta, ya nuna mata nayi ƙanƙanta da yawa amma ta dage, da ƙyar ta bari na shekara huɗu. Ya sakani a wata makarantar addini da take ƙauyenmu, sai dai akwai nisa sosai daga gidamu zuwa makarantar dan haka mussaman yake biya malamin makarantar kuɗi, ya dinga sawa ana zuwa a ɗaukeni ko a dawo dani.
Cikin ikon Allah nan da nan, kasancewar ƙwaƙwalwar yarinta, na dinga ɗaukar karatun Alkur'ani da malamin ke tsaye a kaina yana koya mini.
Tamkar ɗan ƙaramin ɗansa haka ya mayar da ni, ya kan ɗorani har a kan cinyarsa yana koya mini karatun Alkur'ani.
Sai dai ƙiyayyar da ake nuna mini a gidanmu ta sanya bana sakewa ko a cikin yara, dan ko tsakar gida na fito wasa, sai yayyena su ci zalina.
Kullum ina naniƙe da Innata ko ina makaranta.
Batun gata a wurin mahaifina ba a magana, duk abin da ya ɗinka sai ya ɗinka mini, ga mahafiyata ma bata wasa da Abincin da zan ci, bata bani cimar banza, gashi da ƙananan shekaruna amma girmamani take saboda sunan da aka saka mini.
Daga cikin abin da yake ƙonawa mahaifiyata rai, shi ne yadda abokan zamanta kan kirani da jikan maguzawa saboda a danginta akwai wanda ba Musulmi ba, cikin izgilanci idan ta kirani magajin Malam, sai suce ko kuma jilan maguzawa ba.
Sai da na shekara bakwai a duniya, sannan mahaifiyata ta kuma haihuwa, ta sake haihuwar ɗa namiji, aikuwa matan gidan nan tamkar su kasheta, saboda 'ya'ya maza take haifa. aka saka wa jaririn sunan Huzaifa.
Duk da Inna ta kuma haihuwa, hakan bai hana ta daina sona ba, tare da cigaba da kula da mu.
Ban fi shekaru goma ba, Mahaifina ya fara tafiya da ni wuraren kasuwancin sa, idan yana gari wasu lokutan haka yake zamansa yayi ta hira da ni, yana mini hirar kasiwancinsa duk da ba ganewa na ke yi ba. Ya biya aikin umara ni da shi ya tafi da ni.
Hakan ya ƙara rura wutar ƙiyayyata a zukatan matan gidan, kamar su cinye ni su huta. Inna tana yawan gaya masa ya dinga ƙoƙarin yin adalci a tsakanin yaransa bai kamata ya tafi da ni umara ba. Amma buɗar bakinsa ya ce mata "Su 'ya'yan su da nake aurarwa na ke kashe musu kuɗi nawa na taɓa bawa Yazid, ina adalci a tsakanin su"
Ƙanina Huzaifa shima ya fara tasawa, sai dai halina da na Huzaifa ba iri ɗaya bane ba. Huzaifa yaro ne mai ƙiriniyar gaske, ga ta'adin tsiya, Inna tana can tana aiki Huzaifa zai fita tsakar gida ya shiga neman magana a tsakar gida.
Su kama mutan gidan su kama Huzaifa su yi ta duka suna zagi, abin da yake matuƙar ƙona mini rai, in ga an daki ɗan uwana. Duk rashin maganata ina jin haushin in ga an taɓa gudan jinina.
A lokacin na kai shekaru goma sha uku, ina haddar Alqur'ani sosai da sosai, tun Huzaifa na shekara uku nake tafiya da shi makarantar mu. Idan muna gida kuma ina koya masa karatun.
Ba zan manta watarana ba, babbar yayarmu da aka yi mata aure tuni, mai suna Yaya Gaji ta zo ita da yaranta.
Suna cikin wasa tare da Huzaifa da yaranta, faɗa ya kaure a tsakanin sa da ɗanta Sani, yayyensa suka haɗu suka dinga dukan Huzaifa, da ƙyar na ƙwace shi, na kalli ɗaya daga cikin yayyena da har da su a dukan Huzaifa, abin da ban taɓa ba nace "Allah ya saka maka" ba tsammani na ji saukar mari yayata mariya ta mareni tare da ɗorawa da zagina. Duk ƙanƙantar Huzaifa da yaga an mari yayansa, haka ya fara kaiwa Mariya duka, haka na janye Huzaifa muka bar tsakar gidan.
Sai dai ko mintuna goma ba ayi da dukana da Mariya tayi ba, ta ƙone a hannu da ruɗen tuwo, a take ta kurma ihu, ba a ɗau tsawon lokaci ba hannun ya saɓule a take.
Mariya ta sha jinya dan kamar hannun ba zai warke ba, shi kuwa Huzaifa kamar an sake tunzura shi kullum rashin jinsa gaba yake yi.
Hatta Innarmu suna yawan yin faɗa da Huzaifa, ni kuwa ko Inna bana son na ga tana taɓa mini Huzaifa.
Gaba ɗaya hankalina baya kan kasuwancin da mahaifina ke ta janyo ni kan harkar. Ina nan na mayar da hankali a kan karatu na, tare da kula da ƙanina abin ƙaunata.
Kwatsam! Matan mahaifina suka tsiro da wani camfi, wai in dai aka taɓawa Inna 'ya'ya sai wata masifa ta afkawa mutum, bayan jikan maguzawa da suke kirana da shi, suka fara ƙoƙarin laƙaba mini maita ni da mahaifiyata.
Ina da shekaru goma sha huɗu, na sauke Alƙur'ani hadda, malaminmu ya fara batun a turani makaranta cikin gari, domin samun cigaba da karatuna na addini.
Mahaifina ya fara iƙirarin karatun ya isa haka, yana son ya sakani a kan kasuwancin sa sosai, amma mahaifiyata ta cigaba da lallaɓa mahaifina, a kan ya bar ni na cigaba da karatun.
Son da yake yi mata ya sanya wasu lokutan, baya son yin abin da zai sanya ta cikin damuwa. Makarantar da zan tafi ta kwana ce, amma zallar ilimin addini ne ake koyarwa a ciki.
Inna tana ta yi mini shirye shiryen tafiya, ni kuma kewarta da ta ƙanina ta fara damuna, ina son karatuna amma kuma ina ƙaunar iyayena da ƙanina. A nata shirin tafiyata ne, a lokacin kuma Innarmu ta fara wata irin rashin lafiya, ga kuma tsohon ciki, ga wasu irin ƙuraje da suka fara fito mata a jikinta.
Nan na ji ba zan iya tafiya na bar sanyin idaniyata a wannan hali na rashin lafiya ba.
Inna ta dafa kafaɗata ta ce "Haba Gwani ɗan Inna magajin malam, ba ka son Inna ta yi alfahari da kai, ka zama babban malami?"
"Inna ina so, amma baki da lafiya fa"
"Bakomai, kar ka damu zan ji sauƙi in sha Allah"
Huzaifa ya kalli Inna ya ce "Inna, wai almajiranci za a kai yayana, ni gaskiya zan bi shi in da za shi"
Inna ta ce "A'a ba almajiranci bane ba, karatu zai je yi"
Huzaifa ya fara kuka ya riƙe ƙafar Yazid ya ce "Gwani Dan Allah kar ka tafi ka barni, dukana su Mariya zasu cigaba da yi, kuma wa zai kaini makaranta? Da wa zan dinga cin abinci?".
Na durƙusa na rungume ɗan uwana, ina rarrashinsa. Inna ta matsa na tafi