Showing 12001 words to 15000 words out of 15735 words
_A wonderful world & Special anti terroRism squad_
____________________
*MARYAM NASEER MIRRAH*
~AMMEY LAYLERH ✍️~
✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~*
BOOK Two…………………………✍
7&8
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
# The friendship
# Romance scene
# His bloved_friend Meerah
# Meerah Ak drama's
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
_NIGERA'n_
~Lagos~
Tunda Isa manu yaji abinda ɗan nasa ya faɗa ya tattare nasa ya nasa ya gudu daga gidan baki ɗaya, Idan ya gama haukar tasa inyaso daga baya sun fuskanci juna, Amma kuma saidai me? Washe garin ranar sai labarin yasha banban.domin kuwa kai tsaye gidajen jarudu suka juya labarin kamewar da mom surry tasa aka mai da wani labarin na daban.
_A wayewar garin yau kahadi mun tashine da rikicin kame babban ɗan wannan shahararren uban ƴan siyar wato Isa manu, bisa auren manufa da sukaso yi da wannan shahararriya fitacciyar ƴar jaridar wato, _MARYAM ABDULLAHI GWANI_ {MERRAH}. Wanda kai tsaye black mailing mahaifinta yaso yi tunda kowa yasan malam Abdullahi gwani babban malamine. Don dama bayau manyan ƙasarmu suka saba blackmailer's na mutane ba saidai kuma shi Allah ba azzalumin bawansa bane dan haka ma shine ya kuɓutar da merrah daga sharrinsu, ganin basu sami cikon burinsu bane ya sanya babban ɗan nasa yunƙurin kashe ƴar yayarsa da aka misanya masa da ita a matsayin Merrah ɗin..._
Wannan labarin da isa manu ya riska a washe garin ranar shi yafi komai ɗaga masa hankali.domin tuni labarin ya zama shine very latest a safiyar ranar, mantawa yayi da komi yaje har station ɗin hankali tashe domin ganawa da ɗan nasa, sai de amma sammm salman ya hana uban nashi ganinsa. Shi kuwa isa manu babban burinsa kawai so yake yaji daga bakin ubanwa waɗannan maganganun suka fito, domin tsananin tashin hankalin da yake a ciki yafi gaban kwatance. Haka yabar station ɗin hankali tashe kai tsaye babban gidan gonarsa ya wuce domin tattaunawa da ƙashin bayansa masu cin mushe tare masu fuska biyu a cikin al'umma....._
Daga nan kuma suka saki duk wani baɗakalar party'n da su salman suka gudanar tun ana saura kwana biyar bikin. Har dama becholer's night ɗin da sukayi wanda yafi ko wanne haramci tunda buguwane sukayi sosae tare da romance na ƴan matansu.
_MOm surry_ (Hajiya Nafisa)
Wata kafurar dariya ta kwashe da ita tare da doka ƙafa harda su riƙe ciki a loƙacin da take ganin labaran data tsara kai tsaye ta fiya maƙudan kuɗaɗe domin a fitar da labarin, "Koya yaci tuwa dani! Hhhhhhhhhhh ba kunce ku ƴan iska bane wllh inhar ba zaku risina ba yanzu wasan ya fara. Gashi tun a zagayen farko ni ce winner's idan kun shirya muje zuwa a sannu zanta bankaɗo manyan sirrika ina tonawa Hadiza kiyi haƙuri dolece ta sanyani hakan"
Wani murmushin kina kasheni da salonki mom Surry ta jefi mahaifiyarta dashi, hannu ta bata suka kashe tana me cewa.
"Farin cikinki a rayuwata shine gaba da komai shalele! Ki rubuta ki ajje salman isa manu har gaban abada naki ne ke kaɗan ki indai ina raye. Ba tare dako kishiya yayi yunƙurin yi miki ba yadda ni kaɗai na rayu da mahaifinki don haka kema ke kaɗai zaki rayu a naki gidan kiyi yadda kikeso da gidan dama me gidan gaba ɗaya"
"I sonki mommana!"
Surry ta faɗi tana me rungume mahaifiyar nata dan tapping gadon bayanta ta shiga tana furta. "Wannan alƙawarinane Shalelen mommah kar kiji komai"
Acan gidansu salman kuwa idan hankalin Mum salman yayi dubu to a tashe yake, ganin ɗan nata a hannun hukuma domin sammm ita bata da masaniya akan auren manufan da mahaifinsa yayi niyar masa da yarinyar kawai dai abinda ta sani tasan bata son aurenshi da ita yarinyar har cikin zuciyarta domin haka kawai taji babu alkhairi a auren.
Sosai hankalin Malam Abdullahi ma ya sake tashi, kenan ta tabbata Allah tseratar masa da ƴarsa yayi daya aiko masa da tsohon abokinsa ta hanyar nemawa jijinsa aurenta. Su kuwa sauran matan gidan da haryau sun gaza gano wanda aka ɗaurama meerah ɗin aure dashi sshine yafi komai soya zuciyarsu. Tunda malam Abdullahi'n be faɗa musu ba suma sai bayan ɗaurin Allah ya sheda musu cewar Allag beyi da salman ba amma Alhamdulillah basu tozarta ba domin kai tsaye wani tsohon abokinsa da dama nemarwa jikinsa auren yazo ya tarar da wannan matsalar yace kawai a daura auren a take.
Wanda dama Malam Abdullahi'n yana cikin tashin hankaline domin ana dab da ɗaurin auren aka bayyana masa wasu shegun miyagun halayyar salman ɗin, yana cikin alhinin ne kuma Allah ya kawo masa mafita da ɗauki ta hanyar ɗaura mata auren kai tsaye ba tare da fuskantar wani tashin hankali ba. Wannan shine ainihin abinda suka sani kaɗai. Kuma duk iya kissa da kisisinarsu sun gaza gano mijin da aka ɗaurama merrah aure dashi kakaf garin lagos, sun kuma gaza gano wanene tsohon abokinsan daya ambata musu.......
Anne kuwa baka isa gane ainihin abinda ke rai da ruhinta ba. Abinda ta sani kawai shine banbancin bugun zuciyarta daya sauya akan yadda take fuskanta akan auren salman, a loƙacin da malam gake me sanar da ita ga ainihin abinda ke faruwa a taje taji bugun zuciyanta yana sanjawa da wani irin sanyi sanyi Me kama duka sassan jiki a hankali.
Toshe kunnuwanta tayi ga duk abinda yake shige da fice akan lamarin auren merrah ɗin. Domin taji nutsuwa kam ba ƙarya akan shi wannan auren nata na yanzu akan na baya, hakan yasa ta shiga binta da tarin adda'_oin kariya a duk inda take wannan kenan.
Tana tsaye daga tacan bayan ƙofar kitchen take leƙen Mum salman dake zaune ta rafka uban tagumi. "Ai kaɗan ma kuka gani don baku ga komai idan har ban wargaza wannan ahaliba niɗin ba wushiyatu bace" zeey ta faɗi tana me sakin wata shegiyar dariya ƙasa². Kamar wanda aka hankaɗo sai gashi ya faɗo ɗakin babu ko sallama. Da sauri ta miƙe tana taryarshi tare da faɗin, "Aha Ina salman ɗin kuma Alhaji?"
"Hmmmmmmm" ya saki wata ajiyar zuciya yana zama tare da zame hulan kanshi yana firfita da ita, "Alhaji magana fa nake ma! So nake ka warware min komi domin ni kaina a kulle yake da wannan batun, kana ina ita surayya'n ko duka aka haɗa aka tafi dasu?"
Ta sake jeho masa wata tambayar ganin me tankata ata farkon ba, "Aike zan tambaya tunda kin haɗa baki keda ƴar uwarki kunci amanata,wllh Hadizah kiji tsoron Allah ai dama nasan tunda baki so aurensa da merrah ba dole zaki ɓata!. Saidai banyi zaton da wuri haka ba tunda muma amfaninta kaɗan ne a garemu, daga inda muka gama da ita jefarta zamu a bolar da muka tsinta, Amma shashashan shirmenki ya ɓata komai Hadizah"
"Aika sake rufenin ne Alhaji kenan dai ta tabbata auren manufar kuka so yi da ita yarinyar kenan?"
Sammm isa manu ma ya gaza bata amsar komi, domin wani irin turiri zuciyarsa ke may ta tabbata dai kenan dole akwai wanda ke bibiye da al'amuransu, Lallai yayi sake da yawa amma ba komi hakan ma tamkar sun zaburar dashi ne. Duk da yadda mum ke masa magana shareta yayi upsaid's nashi ya nufa yana tsane uban zufar dake keto mishi, harta ɗau hanyar saman itama domin bin bayasan sai kuma tayi saurin juyawa tana me nufar bedroom nata car key nata ta ɗauka tare da fita waje, Cikin wata dallekiyar Mwb ta faɗa tun kamin ta isa get take danna hong da ƙarfi don kai tsaye tanason suyi magana da Addarta ne Mom surry.
Zeey na ganin fitar mum tayi wuf tana me nufar saman Isa manh. Yana tsaka da wayarsa yaji ƙarar door handle ɗin da aka taɓa saurin janye wayan yayi tare da katsewa ganin zeey ce, wata doguwar ijiyar zuciya ya sauƙe wani munafikin murmushi ta sakar masa tana ƙarasowa inda yake. Hannu ya ware maga a take kuwa ta faɗa jikinsa Hannuwansa ya sanya yana zagayeta tare da tambayarta. "Ta fita ne me gidan?"
Ɗan ɓata fuska zeey tayi tare gyada mai kai, kumatunta ya lakata cike da ssheƙiyanci ya furta, "Yau kenan anji tausayina za'a kula dani uhum?"
Wata shegiyar hararan gefen ido ta sakimmai a ɓoye daga nan suka shiga sheƙe ayarsu a ɗakin Aurensa na sunnah...
_KUWAIT★_
The third season of *Winter Wonderland #EMAAR's* has kicked off, offering a unique winter experience that combines entertainment and fun activities for the entire family. #الكويت
*UMAYMAH POV*
Zaune takai wani irin zafi take ji yana ratsa ta tun daga tafin ƙafarta har zuwa tsaƙiyar kwanyarta, dalilin hakan nema ya sanya mata karkarwar jiki tamkar wacce ta ji kiɗan gangi. Wanda hakan ne ya haifar mata da gumin da ke ttsatssafo mata a kowacce kafar da ke cikin ilahirin jikinta. Ba yau ne karo na farko da hakan ya taɓa faruwa da ita ba, sai dai a wannan karon ji take tamkar an saka ta a tukunya ana dafa naman jikinta da tafashashshen ruwan zafi ne.
Da ɗan ƙarfi ta ɗan ciji ƙasan laɓɓanta tana yarfe hannuwa haɗe da lumshe idanunta da takejin su tamkar a watsa mata barkono a ciki tsabar zafin da suke mata.
Amintacciyar hadimarta beenanzer da ke bayanta tana mata fifita cikin ƙwarewa a iya makirci ta sake rusunar da kanta ƙass.
"Hutawarki lafiya uwar ɗakina takawarki lafiya uwar magajin sarautar Emaar's zinariyar sarautar Emaar's haskenki bai tsaya iya shi kaɗai ba kin haske lungu da saƙon cikin Masarauta. Ina gwanar wani ga tawa! Kin yi taki kin yi ta kowa garnaƙaƙin dutse kike kowa yay karo da ke shi ka faɗi! Hadari malafar duniya kenan. ki kwantar da min da hankalinki Auren da suka ɗaura masa na bazata hakan ba zai sanja komi ɗin a yadda kika san shiba, kin manta kece uwar maza a wannan masarauta? Kin manta babu me gigin ɗaukar ɗaya daga cikin waɗan nan watsatstsun yaran ya basu sarautar Emaar's. Domin kowa shedane na sanin cewar suɗin ba kowa bane su facen drinker's Humanzer's wanda dattin zina da giya suka gama musu fenti, Ki ɗauki wannan auren ba'a bakin komai ki ɗauke shi a matsayin matacce! shuɗaɗɗe......
Wani irin juyowa ga hadimar tata tayi cikin wani irin zallar fusata ta furta.
"Kada in damu fa kike cewa beenanzer? Kinsan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli waɗan nan shegun yaran? A matsayin ƴaƴan sarki hassan Al-hassan wanda sune magadan sarautar Emaar's ko kin mance sune manyan ƴaƴan maza a masarautar nan?
shin baki ganin iyakata da mulki sai dai gani sai hange tunda sune manya akan nawa ƴaƴan? ko baki ga yadda komai ya fara juye min ba? Shi wannan tantiran ya ɗauke uban nashi da ina dab da cikar burina Amma shegiyar tsohuwar ta ɓata min aiki, Kuma sama taka an kuma shammatata ta hanyar ɗaura masa aure wanda shine babbar barana a gareni! Ya kike son nayi? Zuciyata na dab da tsayawa da aiki beenah! A ko wanne hali a ko wanne irin yanayi inason a sake tarwatsa ahalin Maryam inba ta kama da ɓatarwa tamkar shekarun baya da aka ɓatar da ƴar Razeenerh to suma a ɓatar min dasu,yanda ko labarinsu ba za'a sake tayarwa bare na baya su riska tamkar da yadda akama Eesha Emaar's"
Cike da wani irin tsoro jesrah taja da baya tana me toshe bakinta da hannuwanta, cike da tashin hankali da tsananin tsoro ta zaro ido da tarin mamaki bata gama dawowa hayyacinta ba taji Mum Mandood na sake faɗin.
"Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Maryam da yaranta, zanyi duk abinda ya kama domin in kauda _ABDOUL-MALEEK da kuma zAID_ A matsayin magadan sarautar Emaar's masu jiran gado, dan wlh Allah a wannan karon zan iya kashesu bawai ɓata su a matsayin mashaya da kuma maneman mata ba, domin kuwa wannan rana tana ɗaya daga cikin abinda yasa nayi bore a shekarun baya. Amma sai gashi nayi GUDUN ƘADDARAR wannan rana me kama da irin yau!. kuma sai gashi yanzun alamu na gwada min dukkan wani dagewa da taƙarƙarewata wajen gujewa wannan rana irin haka saidai kamar ma biye take da nawa sawayen ƙafa da ƙafa domin al'amura ne keta faman yimin warwara ya zamanane kamar ina dufka ana min warwara.
Loƙacin mutuwar _JADDERN ASHAAN_ yayi ba tare da wannn kwalmaɗaɗɗiyar tsohuwar ta sani a tunaninta ita kaɗaice me basira har wani tinƙaho take da babu wanda yasan ida jaddern ashaan take! Bayan kuma ta haifi ɗa mara amfani lusari Tirr da mutum me irin halin Hussein.....
Cikin tsananin kaɗuwa jesrah ta juya da sassarfa tana tafiya da baya baya harta samu tabar sassan Mummy Mandood Iska kawai take fesarwa Sam tama rasa ma wanne irin tunani zatayi,gaba ɗaya kwanyarta ta toshe Shin su waye waɗannan Eesherh da kuma jaddern ashaan? Tambayar da tazo ta mata tsai a zuciya kenan, ko gabanta bata gani babban burinta kawai ta ga Oum ɗinta domin tasan ita tana da amsar duka waɗan nan tambayoyin nata.
Karon da taji tayi da mutum ne ya sanyata saurin cin birki, itama a nata ɓangaren da sauri merrah taja nata birkin dafe da goshi. "Wayyo kin fasa min goshi"
Ta faɗi tana me duban jesrah ɗin da sukaci karo a hanyar shigarta palon Oum ita zata fito ita kuma zata shiga. Dake ba'a cikin nutsuwanta take bane ya sanya ta furta. "Sorry Habeebty banganine sosae" tana faɗar hakan ta shige palon Oum ɗin....
Oum dake tsaye har yanzun bayan fitan merrah ne tayi saurin duban bakin ƙofan, ganin saɓanin tunaninta ne ya sanya ta faɗin, "Jesrah bakin fita wurin aiki bane kamm?"
Kanta take girgiza mata tana kuma nufota ɗan daidaita numfashinta dake seezing tayi tana dannar setin haert nata tare da furta.
"Oum Su waye _JADDERN ASHAAN_ da kuma _Eesherh_ ?"
Da wanj irin masifar karfi Oum ta juyo tare da riƙo hannuwan jesra ɗin cije da matsanancin tashin hankali ta fuskanceta dakyau tare da faɗin.
"A ina kika ji? Waye kuma Jaddeern Ashaan? Easher kuma ƴ.. Ƴar...... Sai kuma ta ƙarasa furta abinda take son faɗin sakamon zuciyarta da taji ya mata wani irin mugun nauyi, tare da hautsuno mata da wasu shuɗaɗɗun al'amura maban banta cikin abinda bai wuce second biyu ba.
Zaune takai gefen haɗaɗɗen royal bed nata tare da matse hannun jesrah ɗin cikin nata tana fesar da numfashin daya mata tsai a ƙahon zuciya.
"Komai ya kusa bayyana kansa, komai kuma ya kusan zama tarihi Insha Allah kiyi shiru da bakinki Allah yana daga bayan me gaskiya"
Haka kaɗai Oum ta faɗim ma jes tace ta fita aikinta Allah ya bada sa'a jiki a sanyaye ta fita ba tare data fashimci komai ɗin da taso ffashimta, amma ba komi insha Allah a matsayinta na ƴar jarida dole sai tasan wani abu daga cikin labarin kafin bayyanar komai ɗin kamar yadda oum ɗinta ta fadin mata......
Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sake a loƙacin data gama tabbarwa da cewa jesrah tabar room ɗin baki ɗaya Goshinta takai ƙasa tare da furta.
Ya wadud,Ya zul'arshin makin, Allahu ahad kaci gaba da ƙare wannan bayin naka daga duk wani sharrin me sharri. Ya Rabbis samawati wal'ard karkaci gaba dabe mugyaye damar da zasuci gaba da zalumtar keɓantattun bayinka, Allahu kaine Allah kaine me yadda kaso a duk sadda kaso ɗin kuwa Allah ka mana maganin Azzaluman da burinsu suci zalinmu su zalumcemu Ya ilahi ya mujibud da'awati Allah kare ɗaukakin keɓantattun bayinka wanda basuji ba basu gani ba, Allah ka mana maganin wanda suke ganin sunfi ƙarfinmu Allah ka zarta da ikonko na _KUN FA YAKUN_ akansu ya Allah!!!"
Oum takai ƙarshen adda'ar nata tana me fashewa da wani iri kasalallen kuka irin wanda ya daɗe yana cin zuciyar nan.
★★★
_AK_
Gaba ɗaya ɗakin tsit yake daga sautin karatun Afif muhd taj bakajin komai a room ɗin sai iskan dake kaɗawa irin ta farkon daminar nan da kuma ta sanyin AC kawai kakeju. Sai wani irin ƙamshin Air freshsheners da turarukaan wuta masu daɗi da babu jimawa aka gyara may, Ɗakine me girman gaske dake ɗauke da setin royel furnitures masu tsananin kyawun gaske White colour sai ɗan adon milk color daya aka musu. Daga ta nan bakin bed ɗin wani haɗaɗɗen kuwait carpet ne me tsananin laushi da aka shimfiɗa wanda yakai har tsaƙiyar ɗakin, daga gefen window's kuma wata keɓantacciyar kuwait sofa ce Ajiye da ƙaramin fridge.
daga gefen mirror kuma wani babban table ne da aka jera littattafan Addini shimili guda gasunan, daga ta gefen gabas akayi wani zagayyen wuri na musamman wanda ke shimefiɗe da wata kalan lallausan praymed me taushin tsiya, sai wasu zagayayyun kuwait decoration's irin masu haskaka room ɗin, sammm ɗakin baya da woni tarkace haka yake simple gwanin birgewa wanda mutum zaiyi normal real life nashi cike da bada cikakkar nutsuwa.
Agogon ɗakin ne ya buga ƙarfe 11:31 am na ranar yau Monday daidai bjgawn agogon ɗakin yayi daidai da Mirza handle na ƙofar bathroom ɗin da Ak yayi, Anutse ya fara