Showing 87001 words to 90000 words out of 113235 words
gani saidata Isa gaban maleek zatayi mgna idanuwanta suka sauka gefensa daya da jekadi ke tsaye sunkuye da Kai goshinta duk jini daga gani itama tana cikin tsananin tashin hankali
A haukace lailah ta waiwaya ta kalli gawar dake rufe agurin taji qafafunta na sagewa tayi baya zata Fadi macen dake sanye cikin uniform na hukumar qasar ta tareta tana riqeta dakyau da alamar dama ita ake jira.
Ta fizgo da qarfi tana kallon maleek bakinta na rawa cikin tsananin tashin hankali tace"
Wanene???
Me yake faruwa anan?
Kallo daya yayi Mata ya juya yana sauke siririn numfashi sbd gabaki daya al'amarin ya sauya acikin qanqanin lokacinda basuyi zatoba.
Kallon gawar padima yayi akaro na hudu Yana tunanin yanda 'yar uwarta zata iya handling wannan mummunan al'amarin Sam an shammacesa a guri mafi mufi Dan kuwa yanzu acikin jekadi da lailah baisan wazai fara wankewaba duk da dukkanin shedu lailah suka nuna ita tayi kisan sbd baro baro jakadi ta fada cewar lailah ce tazo ta bugeta ta Suma itama lailan ta nuna hakan ta Yaya za'a fitarda lailah daga wannan ta bangare daya ta Yaya NURU zataji wannan mummunan labarin?
##MAMUH#[10/5, 8:15 AM] *_Mamuhgee 42_*
*Assalamualaikum warahamatullah taala wabarakatuhu*
08121491609
*Aisha s bayero traditional medicine and herbal reaserch center*
08121491609
08121491609
1_maganin sanyi
2_maganin niima set
3_maganin nankarwa
4_maganin kiba babba 8kkkarami
5_maganin hips
6_maganin gyaran nono
7_maganin rage kiba
8_maganin saka feeling
9_maganin cida kwai
10_zuma yar asali
11_maganin basir kowanne iri
12_hodar niiama
13_maganin mallaka
14_gumbar nonon rakumi 10k boket😨
15_gumbar madara 10k boket😨
16_turaren farin jini
17_kaza Mara kwai
18-turaren mallaka 3step
19_hadin matar minister
20_ kaza me kwai
Step 2
1.Turaren mallaka me kwalba
2. Me kunama Dan matsi 3k
3.tuaren goshi
4.turaren girji
5.tauwadar Mata
6.memory
7.kahon mallaka 8.yajin maza tea din maza
9. Dambun matsi
10. Man ayu 11.man damo pure daga zuwa sama
12. Kwallin idonka idona
13 garin Sha daka me kyau
14. Kubewar Mata gasunan dai da yawa bazan iya lisaafawaba harda na kyakkayin cinyoyin da matse matsi kina shafawa zakiji wasai
08121491609
dadai sauransu serious buyer yabiyoni private
me shawara ta bari saita gama karki batamun lokaci plx
**08121491609
******************
Kasa hakuri lailah tayi cikin sabuwar qaramar haukar dake Shirin kamata agurin take tafara kwacewa tana kallon maleek da sauran mutanen dake gurin cikin tsananin ihun dukkanin jikinta na rawa take cewa"
Meyasa zaku tafi Dani?
Bani nakashetaba wlh,
Dan Allah ki tsaya nayi muku bayanin abinda yafaru wlh tallahi bani bace
Dan girman Allah maleek kace su barni kasan bazan taba iya aikata wannan mummunan abin ba
Ba halina bane,
Dan Allah ki sakeni wallahi bani bace ku tambayi jekadi Dan Allah maleek karka Bari su tafi Dani....
Tana ihun tashin hankali dukkanin jikinta Babu inda baya wani irin mazarin tashin hankali da ficewa hayyaci musamman data tabbatarda tabbas kisa akai Kuma itace ake nufin tayi kisar kenan kasheta za'ayi itama tabar duniya da 'yayanta
Tunanin hakan ke saka haukatarda kwanyarta tafara fizgewa tana kokarin zuwa gurin maleek dake tsaye batareda ya dago ya kalletaba sbd kunyar hakan da baqin cikin hakan dake cinsa koba komai ita din uwar 'yayansace matarsa ta farko wadda koman lalacewarta za'a kirata da matarsa ta farko har qarshen rayuwarsu.
Dayake har bakin kofar sassansa qatuwar baqar motar jami'an tsaron take suna Isa aka sanyata aka rufe tana wani irin kuka da neman ceto daga maleek tana rantsuwar ba ita din bace har muryarta tafara dishewa musamman daya zamto kallon karshene takewa koina Dan tasan hukun kisarta bazai dauki delay ba tunda komai a bayyane yake tasake sakin wani mahaukacin kuka tana buga kanta da tint windon motar da qarfi tana kuka tana Kiran sunan maleek cikin dukkanin bada imaninta ga shikadaine zai iya cetonta
Haka aka janyo jekadi itama aka saka cikin motar aka rufe Kafin
Ja motar suka wuce sai alokacin maleek ya dago ya kalli Mr Omar dake tsaye a gefe tsaye kansa sunkuye cikin yanayi na tsananin jimami idanuwansa suka kada sukai jajir ya dago Yana kallo 'yan motar asibitin dasuka Kira suka matso Dan daukar gawar su wuce da ita saiga shelar sanrwar tahowar NEGES da kansa zuwa sassan Dan tuni abinda yafaru ya karade gizah saidai Babu Wanda yasamu iko ko damar shigowa sassan hakama Babu Wanda yasamu masaniyar shin wanene aka kashen daga jami'an tsaron da Mr Omar yakira sai motar asibitin da jami'an tsaron sukazo dasu Dan daukan gawar sai Anneti data iso sassan cikin tsananin tashin hankali tana zubda hawayen ganin wannan mummunar qaddararriyar ranar ace kisa acikin gizah Kuma daga sassan maleek qari da Dadi tsohuwar matarsa da jekadinsace cikinsu daya ya aikata wannan mummunan Abu me duniya zatayiwa MALEEK kallo?
Gashi Anki bude gawar bare asan wanene aka kashen.
Neges na zuwa cikin tsananin jimami da tashin hankalin wannan mummunan al'amarin ya kalli MALEEK Yana bayyanarda damuwarsa da rashin Jin dadinsa akan al'amarin yace"
Ina me jajanta maka wannan al'amari
Saidai nayi maka alqawarin hukunta duk Wanda aka tabbatarda shine yayi kisan a tsakaninsu biyun Dan kuwa wannan al'amari babbane dazai iya tana darajarmu gabaki daya da ikonmu Dan Haka komai zai tafi abisaga adalci da doka wannan alqawarinane.
Sai alokacin maleek ya dago ya kallesa da idanuwansa dake bayyanarda zallar bacin Rai da wani irin zafi na iko da mulki dake yawo jininsa ahankali ya bude Baki cikin kamewa yace"
Godiya maleek yake Kuma Ina fatar zaka tuna wannan alqawarin naka Dan cikakkene jinin delas basa alwawarinda basa cikawa Ni nayi maka alqawarin tayaka cika wannan alqawarin za'a tafiyar da komai bisaga adalci da doka.
Jinjina Kai neges yayi Yana danne abinda yakeji gameda maleek din ya sassauta kallonsa zuwaga gawar da aka dauka za'a shigar ambulance ya waiwaya ya kalli yakoob Yana cewa"
A tabbatarda gawar kafin su tafi da ita.
Matsowa Mr Omar yayi Ya tarewa yakoob hanzari Yana sauke Kai cikin tsananin girmamawa ga neges Yana sassauta harshe da cewa"
Allah yaqarawa neges girma
Ina neman afuwar rashin barin abude gawa irin wannan agabanka sbd darajarka fifitacciyace dabazai yiyu irin wannan abudeta a gabanka sbd dukkanin suturarta a yage take Wanda ya nuna alamar Tasha dama da makashinta kafin samun nasararsa
Ni zanyi shedar tabbarda gawar aduk lokacinda buqatan hakan ta taso agurin Sharia.
Cikin jinjinawa yace"
Shikenan hakan yayi Allah ya kyauta Amma duk da hakan Ana buqatan tabbarwan.
Matsawa mr Omar yayi tareda bawa yakoob hanya ya wuce Dan ya tabbatar din saidai Yana Kai hannun zai bude jami'an tsaron dasuke jiran ambulance su tafi tare suka dakatar dashi cikin yanayi na dokar aikinsu da girmamawa ga neges shugaban yace"
Allah yaqarawa neges girma Babu Wanda zai sake taba gawar Nan ayanxu sbd Babu abinda mukai bincike akansa zamuje da gawar lab muduba komai ayi aune aune daga lokacin ne bayan angama komai zamu bayar da gawar ayi Mata janaixa daganan ne kowa zai iya tabawa Amma yanxu muna bawa neges matuqar hkr
Saidai idan hankalinka yafi kwanciya da kwakwariyar shedane zamu iya cewa tunda maleek yagani hakan zai gamsar da Kai.
Numfashi boyayye neges yasake Yana jinjina Kai tareda kallon maleek cikin yanayi na kulawa da damuwa yace"
Duk yanda za'a ayi kada abari media suji wannan mumman labarin ayi komai a sirrance tunda hukumarma a sirrance suka shigo suka fice.
Motar asibitin tafara wucewa daukeda gawar kafin akabar jamian tsaro uku da sauran securities din maleek a bakin sassan na maleek sbd shima Yana cikin wainda hukumar zata tsare sbd komai a qarqashin bangarensa yafaru Dan Haka an saka tsaro a sassansa babu inda zashi zai zauna aciki bame Shiga sai mr Omar kawai aka bawa dama shima abincin kawai zai ringa shiga dashi yafito sai zuwa headquarter aduk lokacinda aka buqaci ganinsa harsai antabbatarda cikin su biyun lailah ce ko jekadin ce tayi kisan.
Da hakan zancen yasake qamari hankalin jama'ar gizah yayi mumman tashi musamman Anneti tana tsananin buqatan ganinsa saidai ba dama Haka Takoma sashenta cikin tsananin tashin hankali da damuwa tana daga hankalinta da rokon Allah sassaucin wannan mummunan masifar har lailah take roqawa sassauci sbd ita uwace tasan wannan Abu wani babban al'amarine daga ubangiji kowa na neman doki daga garesa Dan Haka kowa zata rokar Masa.
Ta bangaren Mr Omar Yana fitowa gizah tareda maleek cikin sirrantacciyar mota sai motar jamian tsaro da securities dinsa fitowarsu gizah kenan ga tarin dibbin mamakinsu 'yan media ne birjik suka yo kansu tareda zagaye motocinsu suna jeho tambayoyin dasuka kusan hargitsa tunaninsu su dukan Dan kuwa bayani ne akan cewa"
Shin me maleek zai iya cewa akan tsohuwar matarsa da jekadinsa dasuka taru suka kashe 'yar uwar matarsa?????
Tsit sukayi dukkaninsu Mr Omar na dagowa ya kallesu kafin ya 'dan waiwayo ya kalli MALEEK dake duba wayarsa hankalinsa kwance ya girgizawa Mr Omar din Kai take Mr Omar yabawa motar wuta sukai cikinsu da gudu sukaita kansu suna tsananta wutar al'amarin a social media da cewar tsohuwar matar UBAYD MALEEK M KALEEB tayi hadin gwiwa da jekadinsa gurin kashe yayar matarsa a Daren jiya.
Ganin yanda abin ke ruruwa Kamar wutar daji yasanya Mr Omar Kiran mum Sarah da gaggawa ya Bata umarnin duk wani Abu daya shafi kallon news ko wayoyin NURU da afia duk ta lalata kada tabari su samu news na abinda yake faruwa.
Ta bangaren iyayensu nu NURUn kuwa Abu Kamar hadin Baki Koda gari ya waye labarin ya baza duniya babusu Babu Wanda yasan Ina suka bace bat a dare daya ga 'yan kawo rahoto da 'yan jaridu daketa yawon gidansu sunason ganawa dasu akan al'amarin Amma babusu sai hakan yaqarawa tashin al'amarin girma sbd take aka fara kokarin Bata sunan MALEEK da cewar shine ya batarda iyayenta Dan boye laifin tsohuwar matarsa da jekadinsa.
Headquarter dasuka Isa wasu sabbin rubuce rubucen report aka shigar musamman akan ta Yaya 'yan jaridu sukasan macece aka kashe Kuma Yar uwar matarsa sbd Babu Wanda yasan gawar waye dagashi sai mr Omar ko jamian tsaro Kai tsaye ya hanasu duba gawar aka barta akan se Yan asibiti sungama nasu aikin tukuna
Kuma 'yan asibitin ma mutum biyune Kuma a asibitinda Babu Wanda yasan da ita aka aikasu to tayaya zancen yafita zuwaga 'yan media.
Suna dawowa gida ya shige sashensa ya zauna tareda sauke ajiyar zuciya ahankali tareda rufe idanu ya bude ya kalli gefenda Mr Omar yake tsaye Kai tsaye yace"
Kayi komai kaje da kanka ka taho dasu at any cost kada wannan labarin ya samesu harsai sun iso.
Dan dagowa Mr Omar yayi ya kalli MALEEK yace"
MALEEK anan din aikin Nan barinsa nada hadari.
Kaje komai Yana yanda ake son shi.
Angama Inshallah maleek.
Ficewa yayi Kai tsaye yakira Yana booking tickets Allah ya taimakesa washe gari da asuba jirjgin zai tafi Dan Haka Kai tsaye ya wuce ba wani delay.
Sai tsakiyar dare sosai ya Isa gidan Bai samu shigaba ta waya ya sanarda mum Sarah ta sanarda NURU da afia su shirya gizah zasu.
Da mamaki suka kalli juna lokacinsa mum Sarah ta sanar dasu saqon
NURU ta kalli wayarta da jiya ta wayi gari taganta a farfashe ta waiwaya ta kalli afia da tata ma tafi ta NURUn tashi aiki cikin sanyin murya tace"
Kina tunanin lafiya komai yake?
Sauke ajiyar zuciya afia tayi tana Dan duba agogo tace"
Inshallah lafiya."tafada hakan ne Dan bawa kanta qwarin gwiwa da bama NURUn positive answer Amma tun jiya takejin kanta cikin tsananin damuwa musamman dataga miscalls na mum dinta data kirata Bata kusa wayar na silent tunda ta karanta massage dinta taji tana kewar soyayyar uwa saidai Kuma zuciyarta na tunatarda da ita amfani mum dinta keson Yi da ita kawai tunda take nemanta.
Babu wani dogon musu sukahau shiru tsaf suka shirya hankulansu a tashe Babu me nutsuwa daurewa kawai kowannensu keyi Dan qarfafa Dan uwansa.
Sai washe gari da asubar fari jirginsu ya daga suka wuce Basu isaba sai cikin tsakar dare har lokacin 'yan jerida na daddabe boye a wajen masarautar gizah suna jiran rahoto
Dayake Mr Omar yasani saida sukazo gate din Yan jaridar na tasowa yace driver yayi cikinsu da mota duk da hakan sama sama afia taji dayan na jeho tambayar data sakata kallon waje da sauri inda Yan jaridar ke kokarin biyo motar askarawan securities din makeken gate din shiga masarautar suka taresu da sauri suka koma maboyarsu suna jiran sa'a.
Afia jitayi tana gigicewa da abinda kunnuwanta suka ji cewar
Tsohuwar matar maleek tayi kisa
Kenan shine dalilin daukosu da gaggawa ba shiri?
Rawa jikinta yafarayi ta dago idanuwanta nacikowa da hawayen tashin hankali ta bude Baki zatayi magana daidai tsayawan motar bakin sashensu a fixge tasamu damar fizgo maganar daqyar ta bakinta tace"
Mum tayi kisa?????
Da sauri NURU ta waiwayo ta kalleta gabanta na mummunan faduwa
Saidai ganin afian na kallon Mr Omar da idanuwanta da take sukai jajir yasa NURUn juyowa tana kallonsa da jiran amsarsa Dan kuwa take jikin NURUn yaso fin na afia daukan rawa Dan kuwa a yanda tasan lailah kila maleek ne kawai Wanda zata iya kashewa sbd kishi da baqin cikin abinda yayi Mata batasan lokacinda bakinta Yana rawaba ta furta"
Wa aka kashen???
Sauke Kai Mr Omar yayi cikin tsananin jimami da kasa fadar komai akan tambayoyinsu Wanda yasakasu tabbatarda maganar kenan Haka take abindaya faru kenan.
Take hawayen afia suka balle duk inda hankalinta yake Yana tsananin tashi
Mr Omar yayi saurin fitowa ya budewa afia kofa suka fito har NURUn tsabar rudewa ta manta da sashenta za'a qarasa da ita.
Afia tayi ciki da sauri ko gabanta Bata gani sbd tashin hankali wani takeson tambaya taji shin da gaskene kokuwa gizo maganar tayi Mata,
NURU kuwa sagewa dukkanin kafafuwanta sukai ta nufo cikin tana daga kafa daqyar farhat datai bacci saidai bayinda suke shigarda kayansu afian suka shigo da ita
Tana shigowa palon daidai lokacinda baiwar da afia ta dakawa tsawa tana cewa"
Ki fadamun abinda ke faruwa a cikin delah gizah nace..""taqarasa fada cikin tsananin karajin daya tsorata baiwar a firgice tace"
Kisa akayi a...a..sassan MALEEK.
Innalillahi'wainna ilaihirrajiun" shine abinda afia tafara maimaitawa cikin tsananin fita hayyacinta tana girgiza Kai da sauri da sauri.
NURU kuwa Jin sunan maleek a maganar yasa jiri dibarta Saida mutum biyu sukai saurin tarota dama Mr Omar yasakasu kiranta Dan qarasawa da ita Bata masaukin suka fito da ita ko ganin gabanta batayi sosai kokai dake aiki jikinta ya tsaya harta shiga mota aka ja Bata saniba,
Suna Isa bakin masaukinta mr Omar ya bude Mata kofar Motar
gabaki daya Bata lurada wani sashene aka kawota dabam ba asalin nataba Dan tafiyar kawai takeyi batasan inda take jefa qafa Haka Mr Omar ke bude Mata kofofin palukan dasuke wucewa har zuwa na karshe daya bude ya dakata ta shige ya janyo kofar ya juya ya koma Yana ficewa daga sassan gabaki daya.
Hankalinta baya jikinta saidata takunta yafara nisa cikin palon taji iskar numfashinta ya sauya da qamshin dayake shiga hancinta ta dakata ahankali tareda dagowa ta kalli inda take tana waiwayawa gefen damarta numfashinta saidaya kusa daukewa sbd bazatan yanayin datashiga ganinsa zaune kan kujera sanyeda jallabiya brown fuskarsa na fidda wani irin zatin kwarjini Yana kallonta da fararen idanuwansa dake zube tas akanta...ta rufe ido ahankali ta bude ta tabbatarda shi dinne
Zuciyarta da gangar jikinta sunkasa hakura ta nufesa da wani irin gudu dake bayyanarda dukkanin sirrin zuciyarta akansa idanuwanta na cikowa da hawaye,
Yana ganin hakan ya miqe tsaye ahankali daidai isowarta ta fada jikinsa yayi sama da ita kamar yarinya qarama Yana kallon idanuwanta da hawayenta suka tsinke take suna gudu kan fuskarta ya sauketa tareda matseta jikinsa ahankali Yana kallon kyakkyawar fuskarta da fararen idanuwanta dake fidda hawaye sosai
Ya dauke gira daya Yana sake boyayyan murmushi tareda kamo fuskarta da tafin hannuwansa biyu Yana kallon cikin idanuwanta data dago ahankali tana kallonsa itama har lokacin idanuwanta hawayen sun kasa tsayuwa
Ahankali ya matso da fuskarsa dab da tata yakai bakinsa kan kunnenta Saida ya sauke wani numfashin daya sanyata dauke wuta cikin sirrantacciyar muryar da Bata taba jiba a hankali yace"
Kukan menene wannan??
Rintse idanuwa tayi da qarfi tana sake qanqamesa kirjinta na mannuwa da nashi yayi baya Ahankali Yana dafe kan kujerar dake bayansu Yana riko numfashinsa dake neman sauyawa ya lumshe ido tareda budewa ya kallon idanuwanta zuwa hancinta dayayi ja sbd kukan datake
Ya zura hannunsa daya zuwa bayanta ya riqo qugunta Yana sake Kai bakinsa kan kunnenta can qasa yace"
Kina tsoron mutuwana ne??....
Wani sirirn kuka ta fashe dashi Jin abindaya fada sbd har lokacin Bata gama fitowa da mummunan tashin hankalin tunanin rasashiba
Ya kamo hannunta suka zauna Yana kallon fuskarta tareda tallafo fuskar da hannuwansa Yana cikin yanayi na kulawa yace"
Ok shikenan ya Isa haka,
Ban mutu ba,Babu abindaya sameni ok?.
Rungume kanta yayi Yana shafa bayanta ahankali Yana zuwa kanta hartagama kukan tafara sauke ajiyar zuciya sai alokacin shima ya sauke boyayyar ajiyar zuciya tareda lumshe fararen idanuwansa yanajin nutsuwa na shigarsa sbd kukan nata ya wargaza duk wata nustuwarsa dama tunanin komai.
Saidaya tabbatarda tadawo hayyacinta tagama samun nutsuwa ya dagota ya kalli fuskarta datai qasa da ita sai alokacin takejin kunyar kanta ta Dan juyar dakai tana Jin sanyi da nutsuwa na dawo Mata.
Hannunta cikin nashi suka nufi bedroom dinsa da komai ya nuna yakuma bayyanarda Nan din ne asalin turakar sarki Dan kuwa duk wani Abu dake tsare a dakin me adon zaibane(golden) sai makeken gadonsa dako rabinsa ya ishesu su biyun hadda saurama
Sai wasu dogayen labulayen windunansa dasukafi Kama da kofofi sbd girmansu ta waiwaya inda madubinsa yake ya cinye kusan Rabin bangon gefen dayake ta tsaya gaban madubin tana kallon kanta cikin nutsuwa da nazartar rayuwa sbd wato Babu Wanda yasan me ubangiji ya tanadarwa rayuwarsa agaba.
Ta cikin madubin suka kalli juna ta sauke kanta ahankali tana juyawa daga kallon madubin ta taka ahankali tabar gabansa ya riqo hannunta Yana dawowa da ita baya gabansa wannan karon kallo daya yayi Mata ya dauke Kai sbd kokarinsa kada ya tashi a banza Dan kallonta kawai na canja Masa tsarukansa da dama.
Zamewa tayi ahankali tareda nufar toilet dinsa tashige ta rufo kofa tareda sauke ajiyar zuciya me sanyi tana rufe ido cikin sanyi tace"
NURU why did you loose your control¿
Ta Jima ahaka tana sauke numfashi harsaida tadawo nutsuwarta gabaki dayanta kafin ta zare kayanta ahankali ta daure gashinta tsakiya ta yanda bazai jiqeba tayo wanka ta janyo towel dinsa blue ta dauro ta fito.
Kwance tasamesa a tsakiyar gadon takasa kallon gefen ta nufi madubinsa turare kawai tashafa ta juyo tarasa abinyi sbd sallah takeson Yi
Dole doguwar rigarta ta Dora kan towel din tayi sallolinta