Showing 90001 words to 93000 words out of 121529 words
lips din nata sannan tace
"Yayi?"
"Saura kwalli, bakwa san saka kwalli yaran yanzu, ido firkai firkai "
"Kai Daadah." Ta dauki kwallin ta saka. Kallon ta Daadah tayi
"Ya kunnen ba dan kunne?"
"Daadah wai zance zani? Nifa dan kunne takura min yake."
"Saka dai, ko kanana ne, mace sai da kwalliya."
Bud'e wajen da take ajiye su tayi ta dauko ta saka.
"Ko ke fa, muje toh."
Tasa ta gaba suka fito. Dan corridor ne ya raba falon da dakin Raihanan. Dariya take suna magana da Dadah tana tsokanar ta kawai taga mutum a zaune, shine yake facing direct ta inda zasu fito sai Kamal da Lamido da dayar kujerar. Wani irin shock tayi, ta tsaya chak ta kasa karasawa saboda tsabar rud'ewa. Kasa k'asa yake kallonta, kallon da yasa taji kamar na bige mata guiwar ta, taji kamar ta juya saboda tsabar yanayin da ta shiga.
"Raihana, karaso mana kika tsaya anan." Kamal yace yana mata murmushi. Da k'yar ta iya maida masa murmushin ta karaso ta zauna kusa da Daadah ta manne mata kamar zata shige jikinta ta gaishe shi.
"Lafiya lou, ya gida ya kwana biyu?"
"Lafiya lou sir, ina wuni Sir?"
"Lafiya lou." Aryan yace yana kallon centre table din dake gaban sa. Ganin ta gaba daya ya sauya masa lissafi, ga wani irin nauyin Dadah da take wajen kuma yasan kowa yaga irin kallon da yayi mata.
"Mikewa Lamido yayi yace
"Oga muje ko, Raihana ki kai mana abinci falon baki yanzu."
"Ok." Tace ta mike da sauri tayi hanyar kitchen har tana hardewa.
"Ba yau zaku koma ba amma ko?"
"Eh sai sun ga Abby."
"Ok, shima ya fita ne ya shiga gari, kila sai magriba zai shigo."
"Ok Allah ya dawo dashi lafiya."
"Amin." Ta amsa suka fita ita kuma ta bi Raihana kitchen din da sauri
"A tsaye ta ganta jikin fridge bata taba komai a kitchen din ba, shigowar dadah tasa ta motsa ta kalleta tayi murmushi
"Lallai dole yarinyar nan kiki dan uwanki,."
"Kai Dadah, wai dama sune suka zo amma baki fada min ba, wallahi naji kunya."
"Toh ba gashi kin gani ba, ni kuma naga abinda nake son tabbatarwa."
"Nifa babu wani abu fa, ni ba ruwana wallahi."
"Munafuka,ni zaki wa karya? Ban ga abinda ya faru bane ba? Maza wuce ki kai musu abincin kizo muyi magana."
"Kai shikenan na shiga uku." Tace tana dora kayan akan wani babban tray sannan tasa plate uku da spoons ta dauka ta fita ta bi ta kofar da suka shigo din. Sallama ta fara yi a hankali ya amsa ta shigo kirjinta na faduwa. A tsaye yake dama tun shigowar su bayan su Kamal sun ce masa zasu dan je su dawo. Shigowa tayi tana kallon kasa, saura kad'an ta zubar da kayan hannun ta yayi saurin tarewa yana kokarin saka idanun sa a cikin nata da take ta kokarin boyewa. Sakar masa tray din tayi ya ajiye shi a tsakiyar falon. Juyawa tayi ta nufin barin dakin yayi saurin tare gabanta ya hanata fita.
"In...a...wuni?"
"Ai mun gaisa." Yace idon sa a kanta.
"Gani a gidanku, nazo takanas na baki hakuri akan laifin da nayi miki."
"Ai nace na hakura."
"Ban yarda ba, me yasa kike avoiding idona."
"Ni kawai, ba komai."
"Oya, look at me."
Dagowa tayi kamar munafuka ta kalle shi, tayi saurin maida kanta k'asa.
"Please ki kalle ni... Yadda nake kallon ki."
"Ba zan iya ba."
"Are you shy?"
Da ka ta amsa da eh ta juyar da kanta. Murmushi yayi me taushi sannan yace
"Wannan gashin ki ne?"
Da sauri ta juyo ta manta ma shaf bata rufe gashin ba ta baya, ta hau tura shi a cikin dan kwalin.
"Rowa ake min? Idan kana neman aure ai ya halatta a barka ka kalla ko sau daya ne."
"Aure?" Tace tana dagowa
"Umm, aure. Ko ba zaki aure ni ba?."
Bagatatan maganar tazo mata, dan haka bata ma san me zata ce ba, kamar wadda ruwa ya cinye haka ta yi tsit ko kwakkwaran motsi ta kasa yi. Tana jin idanun sa akanta.
"Please, kice wani abu, will you marry me?"
Hadiye yawu tayi da ya tsaya mata, ta daure tace
"A ah."
"Me yasa? Bakya so na?"
"Nima ban sani ba?"
"Ni na sani, amsar kuma yes ce."
"La'ila,haka nace?"
"Action dinki ne yace."
"Karfin hali." Tace a zuciyar ta, haka kawai mutum kai tsaye be ce yana son ta ba, babu wata magana a tsakani sai yace ta aure shi? Haka akeyi dama?"
"Zamuyi maganar a waya, karki kashe wayarki yau i will call you, zo ki zuba min abinci yunwa nake ji, sannan zan samu tea din nan?"
Duk yana tafiya yake maganar ya karasa gaban tray din ya zauna ya barta a tsaye a wajen. Sai da ya kara maimaita abinda yace sannan ta karaso ta durkusa ta dauki plate ta soma zuba masa abincin cike da mamakin gut din sa. Tana ta zubawa yana kallon ta sai da ta cika sosai sannan ta ajiye masa a gaban sa ta saka spoon zata mike ya hanata
"Wannan abincin ina zan kaishi? Ko tare zamu ci?"
"A ah, ni naci abinci."
"Toh ni ina naga cikin da zanci wannan abincin?"
"Gashi nan."
"Rage toh, idan ba haka ba sai dai ki zauna muci tare, ina ci ina kallon beautiful face dinki kinga bansan sanda zanci da yawa ba."
"Na shige su." Tace a ranta, wai me yake damun Aryan din ne yau. Dauka ta sake yi ta rage ta ajiye masa a hankali yace
"Wannan soft hands din naki, i can't wait to touch it again."
Ai bata san sanda ta mike zumbur ba, tayi hanyar barin dakin da sauri, murmushi yayi ya dan daga muryar sa
"Please ki kawo min tea din."
Karasa ficewa tayi, tana fita ta dafe kirjinta da hannunta da yake wani irin harbawa, sai kuma ta samu kanta da yin murmushi. Salon sa daban ne a komai, maganar sa me sanyi da aji ta dinga yi mata yawo a cikin kunne. Kitchen din ta koma ta dauko kayan dafa shayin dan basa taba rabo dasu ta dora ta tsaya a kitchen din ta jira ya gama ta zubo a kettle din ta dauro cups uku zata fito daga kitchen din Muhd ya shigo ya tsare ta ransa a bace.
"Waye wannan da yazo?" Ya tambaye ta yana kallon kayan hannun ta
"Oga Kamal ne da Aryan, na wajen da nake PPA dina."
"Amma sune har sai sun biyo ki har nan? Me suka zo yi toh?"
"Waje na suka zo? Wajen Hamma Lamido suka zo ai, sun san juna tun da Baban su abokin Abby ne."
"Wanda ya zalunci Abby ya tarwatsa muku rayuwa shine har zaku kawo su cikin gidan nan har kina dafa musu tea zaki kai musu?"
"Hamma, ni menene nawa? Sani fa akayi."
"Still dai, a gabana baban su ya kira Abby ya kuma ce ba zai taba yafe masa ba, amma me zai kawo yaransa gidan nan just two days da maganar, tun farko ma be kamata ku tarbe su ba."
"Wannan dai toh Hamma Lamido zaka fadawa tunda shi yace suzo, ya kuma san abinda yake faruwa da Daddyn yace su zo din."
Ta wuce shi zata fita yayi saurin tare kofar
"Ba sai kinje kin kai masa ba, bani na kai."
"Please Hamma ka matsa na wuce."
"Why? Saboda kina son shi ko me?"
"Zan wuce please."
"Sai kin fara sanar dani amsata, kwana nawa ina binki kina min hanya hanya, akan ki na bar aiki na nazo garin nan, duk baki gani ba, amma wasu daban da suka wulakanta mahaifinki kin saurare su har kina dafa musu shayi, sai ki sanar dani nasan matsayata."
"Me yasa kake irin wannan maganar?"
"Kin fi kowa sani, kinsan komai tunda ke ai ba yarinya bace ba."
"Me yake faruwa ne anan?" Daadah da tazo wucewa ta dan jiyo su ta karaso da sauri
"Ya tare hanyar wai ba zan wuce ba, ni bansan me nayi ba."
"Daadah shayi ne ta dafawa bakin chan, shine nace ta bani na kai musu da kai na ba sai taje ba."
"Me yasa ba zan je ba? Me yasa zai hanani zuwa?"
"Saboda gaba nake dake."
Yace cikin bacin rai da kishi dan gaba daya ya kasa controling kishin sa, dan ya dan saurari wasu maganganun da yaji Aryan din yanayi, abinda ya tunzura shi kenan ya biyo ta.
"Bashi ya mika musu toh ke Raihana, bashi kiyi hakuri."
Akan deep freezer din kitchen din ta dire masa, ta fice daga kitchen din da sauri. Bin ta Daadah tayi shima ya fice daga kitchen din ba tare da ya dauki kayan ba, ya nufi falon da Aryan din yake ciki.
_*RQ*_
Page 40
***Babu sallama ba komai ya fada ciki,fuskar sa a tamke. Dagowa Aryan yayi jin an shigo ganin wanda ya shigo yasa shi cigaba da abinda yake ba tare da ya bada wani attention din sa ba, tunda shi sam guy din be masa ba dama tun farko.
"Malam magana nazo muyi." Yace ganin Aryan din ya share shi
"Pardon?" Ya fada yana tsayawa da danna wayar da yake yi ya kalle shi a kaikaice
"Naji duk abinda kace da duk take taken ka ma, Raihana tawa ce ni zan aureta, tunda gida be koshi ba, ba za'a bawa dawa ba."
Kamar be ji abinda yace ba, dan idan ya motsa sanadin maganar Muhd din toh wajen nan ya motsa. wani kululun abu ne ya tsayawa Muhd din na wulakancin Aryan din,.
"Lallai ma, Malam magana fa nake maka."
"Oh haba? Ban ji abinda kace ba ko zaka iya maimaitawa."
"In maimaita?"
"Yes please, ina jinka." Ya zare airdrop din kunnen sa ya juyo yana bashi attention dinsa
"Wasa kake wallahi,na maimaita kamar bani da abun yi? Na tabbatar kaji abinda nace kawai dai ka nuna..."
"Hello baku kusa ba?" Ya d'aga wayar sa kamar ba magana Muhd din yake masa ba,
"Ok, ni zan wuce ma hadu a chan."
"No sai mu dawo ko bayan magriba ne, ko ka dawo kai kadai."
"Ok." Ya katse wayar yana mikewa, ya dan kalli gefen da Muhd din yake a tsaye yace
"Sai anjima Malam, ka dan shiga da kayan ciki."
Ya fice ya barshi da tarin bakin ciki, tunda yake ba'a taba ci masa mutunci irin yadda Aryan din yayi masa ba. Rasa me ma zai yi yayi, ya dinga zagaye a dakin yana jin kamar ya bishi ya shako shi ko dai yayi masa wani abun da zai ji haushi sosai. Kafa yasa ya daki kujerar dake kusa dashi ya juya ya koma cikin gidan.
Kuka Raihana ta fashewa da Dadah, kukan bakin cikin abinda yayi mata. Iyakar kureta yayi ya kaita karshe. Ba haka ake ba, bata taba jin inda ake soyayya dole ba, tunda ta nuna masa bata so me yasa ba zai hakura ba, har zai wani zo ya sakata a gaba kamar wani ubanta. Hakan da yayi ya kara mata tsana da haushin shi a zuciyar ta.
"Kiyi shiru haka na, kinsan zuciyar yan maza da kishi, kishi ne yake dawainiya dashi."
"Toh fisabillillah amma ya dace ya saka ni a gaba yana titsiye ni? Naga ai ba'a dole ko?"
"Ba'a yi, kiyi masa uzuri da ciwo kana son mutum yana shareka sai kaga wani yazo an kula shi, ko waye kuma dole yaji haushi, kawai kowa da yadda yake nuna fushin shi ne akan kishi, ni tausayi ma yake ban, son masu wani akwai wahala wallahi, be yi sa'a ba sam."
"Baki ga yadda yake min fada ba Dadah?"
"Na gani, menene toh? Hakuri zakiyi."
Wasu hawayen ne suka sake biyo fuskar ta, har ga Allah taso kaiwa Aryan tea din nan, duk da tana jin nauyi da kunyar sa, tasan a yadda Muhd din yake cikin fushi da k'yar idan ba zuwa zai ya gaggaya masa magana, tasan kuma fushin Aryan zai yi yin zuciya ya tafi ma gaba daya. Dalilin kukan ta kenan, da k'yar Dadah bata baki tayi shiru sannan taje ta wanko fuskarta ta dawo dakin ta bud'e bedside drawer dinta ta ciro wayarta ta kunna ta, fita Dadan tayi ta ja mata kofar. Wani tunani ne yazo mata ta tashi ta fita, ta shiga kitchen din sai taga kayan tea din a ajiye akan freezer din, babu alamun an taba su daga yadda ta ajiye su. Falon chan ta nufa tayi sallama jin shiru baa amsa ba yasa ta tura kofar ta shiga, baya nan da dukkan alamu ma tafiya tayi, da sauri ta juya ta koma cikin gidan tana kwalawa Dadah kira. Dakin ta, ta shiga ta samu Hamma Muhd din a zaune idonsa ya yi ja sosai suna magana da Dadah, juyawa tayi da sauri ta koma dakin ta, ta shiga number sa tayi dialing. Alwala zai yi yana nannade hannun rigar sa kenan wayar sa tayi kara, daga in da yake tsaye ya leka wayar yaga me kiran. Ganin itace ya sakashi tsayawa da abinda yake yi, ya mika hannu ya dauki wayar sannan ya zauna a gefen gadon ya d'aga.
"Hello."
"Hi, ka tafi?"
"Yes,na tafi. Baki kawo min tea din ba."
"Nazo naga baka nan."
"Kinyi latti, amma zan dawo anjima. Ki ajiye min idan nazo sai ki bani nasha."
"Ok." Tace tana sauke ajiyar zuciya jin muryar sa tar alamun babu abinda ya faru tsakanin sa da Muhd, amma kuma me yasa ya tafi haka kawai ba sallama?
"Don't think hard, wani abu ne urgent ya taso min Shiyasa ana tafi."
Yace jin tayi shiru yasan kuma dole tunanin da take kenan, idan ba haka ba ma yasan da wuya ta kirashi.
"Sai anjima tom, sai ka dawo."
"Ok see you then." Ya ajiye wayar, dan sosa kansa yayi yana son figuring abun baki daya, dama tun farkon ganin muhd yasan son raihana yake, ya kuma sak¨¨ tabbatarwa yau, sai dai be sani ba, mutual relationship ne ko one side? Sannan menene stage din da suke kai, baya son yayi abu da ka Shiyasa be biye masa ba duk da yayi masifar mata masa rai amma ya danne dan ba a irin sa yake bata energy da yawon bakin sa ba, ko Adam sai yayi masa abu sau nawa amma sai yaga damar kallon sa ma, ko ya bashi amsar da zata dade tana sosa masa rai.
"I need to find out ko ma menene."
Tafiyar da Aryan yayi yasa Kamal ma yace zai wuce kawai zasu dawo idan Abbyn ya dawo da magriba, sauke shi Lamido yayi a kofar hotel din sannan ya juya ya tafi gida. Knocking yayi a kofar Aryan yazo ya bude dan yasan shine , matsa masa yayi ya shiga yana kallon shi daga shi sai gajeran wando babu ko riga a jikin sa, shiryawa yake Kamal din ya dawo Shiyasa.
"Fita zakayi ne?" Yace yana kare masa kallo
"A ah, ruwa na dan watsa kaji garin zafi da na dawo alamun zaa iya yin ruwa."
"Eh akwai hadari da alama."
"Kun dade, ina kuka yi ne?"
"Aikin mu ne, baa ji."
"Oh okh."
"Me yasa ka dawo wai? Nayi mamaki da kace zaka dawo."
"Aikin mu ne, baa ji." Ya kwaikwayi same amsar da Kamal din ya bashi ya fada.
"Haha, kana da matsala. Please fada min menene?"
"Gayen nan ne, wanda ka kira shi da muka karasa gidan, yazo yana faffada min maganganu, ban ma dai saurare shi ba, ganin zai bata min rai ya tunzura ni yasa na taho kawai."
"Muhd, munyi maganar sa da Lamido. Cousin dinsu ne kuma saboda raihana yazo gidan takanas daga kano. Infact har Abby ma yasan da maganar kuma yana supporting dinsa sosai da hydar ma."
"I know, dole kayi mentioning hydar a karshe. It's like kamar yafi kowa daukar zafi akai, da ni ma yake fushin naga alama."
"Eh gaskia. Shima irin ka ne da Zafin zuciya sannan abinda ya faru a office da kana ma raihana fada da Ya gani ya sake lalata komai."
"Yes na tuna, har yana cewa sai nayi nadamar abinda nayi mata. Amma ai na bata hakuri ta hakura ma. Shi menene Nasa?"
"Gani yake baka dace da ita ba ko? Kamar zaka wahalar musu da kanwa."
"Hmm. Zan bashi mamaki. Shi zan fara kira nace yazo ya rakamu asibiti idan nayi ma kanwar tasa ciki."
"Hahaha! Kai ko? Baka fa da m wallahi aryan."
"Toh Allah ya zafafa da yawa. Ni kuma da gaske nake ba wasa nake ba, yadda mukayi ta rigima a kanta da yarinta shi yake so mu dora, ya manta ko da din nike winning, cox ni take zaba akanshi."
"Match made in heaven kenan."
"I'm serious, ni da shi ne."
"Ba kara? Soon to be in-law dinka ne fa."
"Lamido ba? Da sadeeq amma hydar sam. Su karata shi da dan iskan yaron chan da Ya gama gaggaya min magana."
"Yanzu dai haushin Muhd takwaran ka, zaka huce shi akan hydar."
"Duk su karata."
"Yanzu duk ba wannan ba, yadda zaa shawo kan Abby ya amince kawai ake nema, Lamido yace kafin mu koma anjima zai fara masa maganar, idan yaso sai muje masa muma da maganar."
"Ok. Go ahead dinsa kawai nake nema. Shi yasa nake bin komai a sannu saboda hakan shine daidai."
"In sha Allahu komai zai zama normal. Ka fara babbar magana ai dole ayi abinda Ya dace."
"Kar ayi ma." Yace yana murmushi. Shi kansa maganar tashi ta bashi dariya.
*****Fada sosai Abby yake wa Lamido, ta in da yake shiga bata nan yake fita ba. Tun da ya same shi da maganar zuwan nasu da kuma maganar raihana ya saka masa full stop dan baya son zancen ma. Da kyar aka samu yayi shiru da fadan ya zauna yana huci.
"Kira min ita maza, idan bata da hankali ni Ina dashi. Idan kuma zaku nuna min iyakata ne toh."
"Ba haka bane Abby. Suna son junan su ne wallahi, mu kuma farin cikin ta muke nema."
"Kana nufin na dauke ta na kaita gidan nan? Kana da hankali kuwa Lamido? Ko dai girman ne kawai na hankali!?"
"A ah, Allah ya huci zuciyar ka. Kayi hakuri."
"Sa waya ka kirata tazo maza ta same ni, akan wannan maganar zan yi mummunan sabawa kowa wallahi, har kai din kuwa."
"Ayi hakuri Abby. Kanwata Kizo Abby na son ganin ki."
"Tunda ita shashasha ce bata da hankali. Mutumin da ya wulakanta ku, Ya kore ku daga gida Ya kwace muku komai , shine dan rashin hankali zaka dauki kanwar ka, ka kaita gidan tayi rayuwar aure. Lallai kuwa sannun ka."
Shigowa tayi kamar Munafuka ta zauna daga bakin kofar ta gaida abbyn ya amsa a ciki ciki sannan yace
"So nake ki fitar da miji, idan kuma babu kowa ni zan zaba miki mijin. Sati daya kuma yayi