Showing 63001 words to 66000 words out of 132567 words

Chapter 22 - BRR. IBRAHIM KHALIL Complete HAUSA NOVEL

02 Jul 2024

8344

yazo yaɗauke ta, ko kaɗan bata son bin abokan Angon sabida yanda wani yamaƙale mata ɗazu da suka zo daga ta buge sa bata sani ba, ita ta ma rasa uban wa yace musu ita ɗin Sister ɗin Amarya ce, yanzu da suka shigo parlour'n sai faman kiran ta suke yi, komi akayi sai suce "ina Sister ɗin Amarya tazo tayi musu sheda" daga ƙarshe ma tashi tayi tashiga ciki tazauna kusa da Saleema dake zaune saman gado

Har Drever yazo basu tafi ba, sannan ne ma suka soma haraman tafiya, anan ne fa Saleema tariƙe Halwa tana kuka wai baza ta tafi ba, in banda dariya babu abinda su Dija suke mata sai faman tsokanarta suke yi, daƙyar dai tasaki Halwa suka tafi suka barta ita kaɗai kamar Mayya.






.




_Nace ko ina Mijin Oho?_🤔😅
[11/7/2020, 3:02 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️


*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_


*بسم الله الرحمن الرحيم*




*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈


*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```


.

*CHAPTER 43*


Ƙarfe 10:30pm. Su Khalil da Brr. Tahir tare da Sameer suka shigo gidan, daƙyar ma Khalil yayarda suka biyo shi don da yace "baya son rakiyan". Shi da kan sa yashiga har ɗakin ta yace "tafito parlour" daga haka yajuya yafita, ita kuma tamiƙe jiki a sanyaye tagyara mayafinta tafito, ahankali taƙarisa tazauna aƙasa tana gaishe su, cike da fara'a suka amsa sannan ne Sameer yasoma musu wa'azi cikin raha, daga ƙarshe suka yi musu fatan alkhairi tare da sanya alkhairi a auren nasu

Har bakin Gate Khalil yaraka su da zasu tafi, yadawo yatarda Saleema tana nan zaune inda take, be ce komi ba yanufi ɗakin sa, yana shiga yasoma cire babban rigan dake jikin sa bayan ya cire Hulan kansa, agogon hannun sa yacire tare da cire links ɗin rigan sa yazube su yanufi parlour

Har yanzu tana nan zaune inda take, zama yayi kan kujera yana kallon ta, sai kuma yaɗauke kai yana kallon ledan da suka shigo dashi, miƙewa yayi yanufi kichen sai gashi ya dawo da plate a hannu tare da wuƙa, zama yayi a ƙasa kamar yanda itama take zaune a ƙasan, yajawo ledan yabuɗe yaciro Kazan ciki yasoma yanka wa cikin plate ɗin don yayi daɗin ci, bayan ya gama duk yajera mata a gabanta da su Holandia sannan yakalle ta yace

"buɗe fuskar ki kici".

Ahankali tayaye gyalen daga kanta taɗago tana kallon sa sai kuma takalli abinda ke gabanta, cike da tsananin kunya tanoƙe ko motsi ta kasa yi, ganin haka yaja baya yana ɗaukan wayan sa yasoma latsawa yana cewa

"Ki ɗauka kici nace".

Wannan karon batayi musu ba ganin ya matsa can baya kuma hankalin sa baya kanta, hakan yasa tasoma ɗauka tana ci duk da dama tana jin yunwa amma baza ta iya buɗe ciki taci ba, kaɗan taci tacire hannun ta cikin sanyin murya tace

"Na gama".

Ɗago kai yayi yakalli plate ɗin sannan yasake maida kansa kan waya yace "ki ƙara".

Hannu tasaka taci gaba taci, bata daɗe ba tasake tsame hannun ta, wannan karon da yaɗago kai miƙewa yayi yaɗau komi yanufi kichen dashi, yana dawowa yace tataso su je ɗaki, miƙewa tayi tabi bayan sa, suna shiga yanuna mata Toilet tashiga tawanke hannu da bakinta tafito, yasake nuna mata kan gadon.. ta ko haye can lungu taƙudundune da gyalen ta


Shi kuwa Toilet yashiga yayi wanka yafito yashirya cikin kaya sannan yahayo kan gadon yakwanta, shiru sukayi ko wanne yana jin numfashin juna, can kamar amafarki tatsinkayi muryan sa

"Ya jikin naki?"

Cike da jindaɗi ta'amsa masa ganin yanda yadamu da ita sosai, daga haka basu sake yin magana ba har sanda Khalil yaji numfashin ta na fita da ƙarfi hakan yagane tayi barci, juyowa yayi setting ta duk da baya kallon fuskarta hakan be hana yaƙure ta da idanuwansa ba, shiru yayi yana tunani yana bin ta da kallo, abinda be taɓa faruwa dashi ba yau sai gashi zai kwana da mace

Ya daɗe ahaka yana ta saƙe-saƙe kafin yasauke ajiyan zuciya yamiƙe yakashe fitila yadawo yakwanta, addu'a yayi yarufe idanun sa, lokaci ƙanƙani barci yaɗauke sa kasancewar baya samun hutu.



Washe gari shi yasoma tashi bayan da suka koma barcin asuba, wanka yayi yashirya yasaka Milk colour ɗin Gezna da yayi masa kyau matuƙa gaya, duk da bashi da aiki ya ɗauki hutu amma Shari'an da yake yi be rigada ya ƙarƙare ba, akwai sauran aiyukan da yake yi a Court, yana cikin saka Wrest watch yaji Nocking ƙofa, fita yayi yaje yaduba yaga drever'n gidan su ne Mom ta aiko sa da breakfast, amsa yayi kawai yaje ya'ajiye a dainning table yakoma ciki, sai da yayi rubutu a ɗan Pepper ya'ajiye mata saitin kanta sannan yaɗau abubuwan da zai ɗauka yafita.


Babu jimawa da fitan sa tafarka, ahankali tabuɗe idanuwan ta yayinda ƙamshin turaren sa suka cika ƙofofin hancin ta, sake lumshe idanun tayi tana murmushi cike da jin daɗi, sai da tajima ahaka bataji motsin sa ba sannan ne tayaye gyalen fuskarta, da takardan da ya'ajiye mata tasoma cin karo, take gaban ta yafaɗi babu shiri tayi saurin kai hannu taɗauka tana jujjuya shi, sai kuma tamiƙe zaune idanun ta har yanzu akan takardan, buɗewa tayi sai taci karo da




.



_"Aslm alaikum Ni na fita zuwa wani waje bazan jima ba zan dawo, and akwai breakfast a dainning Mom ta kawo..."_

_Mijin ki✍️_




Batasan sanda murmushi yasuɓuce mata ba, kalman Mijinki shi ke ta mata yawo a ƙwaƙwalwa, gaskiya Brr. Daban ne da sauran Mazaje, duk da kuwa ta tabbatar ba son ta yake yi ba amma kuma kulawan sa agare ta da tausayin ta ya wuce tunanin me tunani, yana da halin ƙwarai sosai, memakon yanuna mata tsangwama a'a sai yana sauke haƙƙinta akansa, wannan shi ake kira adalin namiji, tayi imani koda baya son ta zata zauna dashi ahaka domin tasan shine ɗorewar farin cikin ta na har abada


"Allah yabarmu tare".


Tafaɗa a maƙoshi tana sake faɗaɗa fara'an ta


Miƙewa tayi tasauko kan gadon tanufi ɗakin ta, Toilet tashige tawanke bakin ta tafito parlour tanufi dainning, tana jin yunwa sosai don haka baza ta iya jira har sai tagama abinda take yi ba gudun lafiyan ta, zama tayi tahaɗa tea me kauri tasha tare da ƙwai da Arish, bayan ta gama tatashi tashige ɗaki taɗauko Maganin ta cikin kayan ta taɗiba tafito tasami ruwa tasha dashi, sai kuma takoma ɗakin Khalil ɗin tasoma gyarawa musamman kan gadon da sukayi amfani dashi, duk da ita ba ma'abociya aiki bane komi yin musu ake yi, ba'a barin ta tayi komi amma aɗan kwanakin da zatayi aure sai da duk takoya abinda zai bata wahala, don bata son me aiki cikin gidan ta tana da kishi sosai


Bayan ta gama takoma ɗakin ta tayi wanka tashirya cikin farar shadda wanda tare akayi musu da Khalil ɗin, shi kuma yarigada ya saka nashi jiya, ta fito ɗas Amaryan ta sai zabga ƙamshi take yi, kallo ɗaya idan kayi mata zakaga ƙyallin amarci atattare da ita (aure ba wasa ba🤫)

Parlour takoma tazauna a lumsassun kujerun ta masu tsantsan kyau da burgewa, wayanta dake hannun ta talatsa takira Ummi, ringing biyu taɗauka

"Ummina I miss You so much". Tafaɗa cike da zumuɗi


Daga can Ummi murmushi tayi na jindaɗi tace "me too My dear, har kin tashi?"

"Eh Ummi kuna lafiya? Ya Daddy da Halwa?"

Cikin dariya Ummi ta'amsa mata tana cewa "ai ga Halwan ma anan".


"To Ummi bata mu gaisa".


Miƙa mata wayan tayi suka gaisa cike da kewan juna sannan tamaida ma Ummi nan ma sukaci gaba da hira, daga baya kuma tabuƙaci akawo mata Husna, Ummi tayi ta rarrashinta akan tabari zuwa nan da sati biyu amma sam Saleema taƙi yarda ita lallai sai an kawo mata Husna yau


"Haba ɗiyata ki kwantar da hankalin ki, ki bari zuwa gobe insha Allahu zan sa akawo miki ita, kinga yau su Gwaggon ki zasu zo zasu kai ki gidan iyayen mijin naki to wa zaki bar ma wa? Ki bari gobe sai akawo miki ita kinji".


"To Ummi amma kar yawuce gobe". Tafaɗa a shagwaɓe".


Daga nan sallama sukayi, tana nan zaune tana tunanin mijin nata sai murmushi take yi, sai da tagaji don kanta ga barci da tasoma ji hakan yasaka takwanta a 3sitter tana rufe idanun ta, babu jimawa barci yaɗauke ta


Can tasoma jin hayaniyan baƙinta tare da bugun ƙofa, babu shiri tatashi tana riƙe kanta dake faman sara mata, daƙyar take tafiya sabida yanda take jin wani zazzaɓi-zazzaɓi na son kawo mata cafka, tana buɗe ƙofan suka shigo nan tatare su da fara'a, duk ƴan uwan Abbanta ne dana Ummin ta su wajen biyar


Su suka sakata tashirya cikin wata Farar atamfa anyi mata Flower da kalan ja da baƙi, sosai atamfan tayi mata mugun kyau kasancewar ta fara, ga ɗinkin da yaɗauki jikin ta sosai na riga da zani, Hijab tasaka fari da takalmi ,sannan suka fito sukayo waje, a motoci biyu suka bar gidan.




*****
Tarba me kyau Mom tayi musu cike da farin ciki sai nan nan take da Saleema, hakan sosai yafaranta ran Ƴan uwanta har basuyi fargaban danƙa mata amanar ƴar su ba, ita kuma Mom ta'amshe ta hannu bibbiyu


Basu jima ba sukace zasu tafi duk da Mom tayi musu tayin abinci amma sukaƙi ci illa ruwa da suka sha, haka suka tafi suka bar Saleema anan, sauran dangin Mom da basu rigada sun tafi ba sai shigowa ɗakin Mom suke yi suna ganin amarya, bayan sun tafi yarage daga Mom sai Saleeman, duk da Saleema tasaba da Mom abaya hakan be sa taƙi nuna kunyan ta ba, Mom kuwa sai janta da hira take yi cike da ƙaunar ta, daga ƙarshe dai da taga taƙi sakin jiki da ita sai tatashi tana cewa


"Tunda kinƙi sakin jiki dani bari in Kira miki Nazeefa tataya ki hira tunda Ni fita zanyi".

Saleema dai batace komi ba har Mom ɗin tafice.




Nazeefa tana kwance akan gadon ta duk abin duniya yabi ya ishe ta, tun sanda aka soma hayaniyan zuwan Amarya tana jin su amma takasa fita, sosai take jin baƙin ciki da kishi aranta sai dai tadage tana ta ƙoƙarin hana kanta kuka, shigowar Mom cikin ɗakin yasa tatashi tana ma Mom ɗin sannu


"Yauwa Nazeefa bakije kinga Amarya ba ga ta can an kawo ta?".


Murmushi Nazeefa tayi tasauke kai ƙasa tace "Mom banji bane barci ya soma ɗauka na".


"To tashi kije wajen ta tana nan aɗaki sai ki tayata zama ko".

Batayi musu ba tatashi sai dai bada son ranta ba tafito tanufi ɗakin Mom ɗin, ita kuma Mom tanufi wajen Dangin ta


Sallama tayi tatura ƙofan tashiga, Saleema dake zaune saman gado ta'amsa mata tana ɗan jan Hijabin ta baya da tarufe idanun ta dashi, kallon kallo sukai ma juna ko wacce da tunanin dake ranta


Ita Nazeefa tana kallon Amaryan Yayan nata ne cike da jin haushi duk da kuwa ta burge ta don kyakkyawa ce sosai wacce kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa ba ƙaramar ƴar jindaɗi da hutu bane, coz ko kaɗan ma batayi yanayi da ƴar talakawa ba


Ita kuma Saleema tana mata kallon rashin sani ne don tasan dai ba ƴar gidan bace, sai dai ko ƴar uwan shi ne duk da babu wani kama da sukayi


Zama tayi akan kujeran dake ɗakin tana ci gaba da kallon Saleeman sannan taƙaƙalo murmushi tace "sannu Amaryan mu, kinzo lafiya?"


Murmushi itama Saleema tayi ta'amsa mata cike da sakin fuska kasancewar ta me yawan fara'a ga kowa


Daga haka shiru ne yabiyo baya dan Nazeefa batasan me zatace mata ba saboda ita ba me yawan surutu bane, itama kuma Saleeman bata sake furta komi ba tayi shiru tana sad da kanta ƙasa, ahaka har Mom tashigo da wasu baƙi tatarar dasu haka, baƙin sun zo ganin Amarya ne, haka Saleema tagaishe su cike da kunya su kuma suna ta yaba mata suna sanya alkhairi, hakan ba ƙaramin sake ƙular da Nazeefa yayi ba har takasa jurewa tatashi tasulale ɗaki batare da sanin Mom ba


koda Mom suka tashi fita bata kula ba haka suka fita ɗakin aka bar Saleema ita kaɗai tana ta zaune, daga ƙarshe kwanciya tayi sabida yanda take jin zazzaɓin jikin ta yana ƙara yawa, lokaci ƙanƙani ciwo yarufe ta ga sanyi da take ji sosai, haka ta ƙudundune jikinta sai faman maƙyarƙyata take yi


Ahaka Mom tashigo taganta, hankalin ta idan yayi dubu ya tashi nan tasoma neman wayan ta, sai tatuna tabar wayan a palrour, fita tayi dasauri babu jimawa sai gata ta dawo tare da wasu mata su biyu, su ma duk hankalin su ya tashi ganin yanda jikin Saleeman yai zafi zauuu



Mom Kiran Khalil tayi tabashi umarnin yai maza-maza yazo matar sa tana gidan ta babu lafiya.
[11/7/2020, 3:33 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️


*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_


*بسم الله الرحمن الرحيم*




*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈


*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```


.

*CHAPTER 44*


Lokacin da Khalil yazo har su Mom sun fito da ita parlour, babu ɓata lokaci yariƙe ta suka fito waje inda motan sa yake, Mom tace mishi "yakai ta asibiti" amma ita Saleeman tace "tana da maganin ta a agida" don haka gida kawai yanufa


Suna zuwa yayi parcking yafito yabuɗe mata motan yariƙo ta tafito, duk da a halin ciwo take amma sosai taji daɗin kusancin sa gare ta, har wani sanyi take ji aranta tana jin kamar ciwon na son tafiya


Tana jingine da jikin sa har suka isa parlour yataimaka mata tazauna sannan yakalle ta cike da tausayi yace


"Ina kika ajiye maganin in ɗauko miki?"


Cikin muryan marasa lafiya tace "yana cikin trolly na Wanda nazo dashi daga gida".


Gyaɗa kai kawai yayi yanufi ɗakin nata, yana shiga yasoma wurwurga idanu, can yahangi akwatunan da yayi mata guda shida, sai yamaida idanun sa kan wani babba kalan sa daban, yana da tabbacin shine wanda take nufi


Wajen yanufa yabuɗe, duk abubuwan amfanin ta ne da tazo dashi daga gida, yana soma bincika wa yaga ledan maganin, ɗauka yayi yanufi parlour'n


Zama yayi gefen ta yabuɗe tare da nuna mata alamun tayi masa bayani, nuna masa waɗanda zata sha ɗin tayi yaciro yamiƙa mata sannan yatashi yaje yaɗauko ruwa a Fridge yabata


Har tagama sha yana ta kallon ta kamar wanda zai haɗiye ta, hakan yasa taji kunya tana sad da kanta ƙasa, be san sanda yasaki guntun murmushi ba yamiƙe tsaye yanufi kichen ita kuma tabi bayan sa da kallo cike da tsananin ƙaunarsa a ranta


Be wani jima ba yadawo riƙe da Cup a hannun sa, miƙa mata yayi yana tsaye a kanta, ita kuma tasaka hannu ta'amsa tana kallon abinda ke ciki, Tea ne yahaɗo mata, be ce mata komi ba sai dai kallon ta da yake yi har tashanye tatashi da ninyan kai Cup ɗin


"No kawo cup ɗin, je ki kwanta idan an kira sallah zan tashe ki".


Babu musu tanufi ɗakin ta tashige, shi kuma bayan ya kai Cup ɗin kichen yadawo yanufi ɗakin sa, ɗakin karatun sa yashige (Library) yasoma binciken abinda yakawo sa, har aka kira sallan azahar yatashi yagabatar yakoma yaci gaba da aikin sa, yana tune da Saleema sai dai yaƙi tashin ta ne saboda bata daɗe ba aka kira sallan, don haka yabari zuwa sallan Asar yatashe ta


Sai da aka kira sallah yafito yashiga Toilet yaɗauro alwala, fitowa yayi yana warware hannun rigan sa da yanannaɗe wajen yin alwalan, yafito daga ɗakin nasa yashiga ɗakin Saleema, yana shiga ya'isa bakin gadon yatsaya yana kallon ta, barcin ta take yi cikin kwanciyan hankali, sai dai yanda take fitar da numfashi da ƙarfi hakan zai sa kagane ba lafiya ba


Ya daɗe atsaye a wajen yana kallon ta cike da tsananin tausayin ta, yasan da cewa tana fama da ciwo tunda lokacin gab da za'ayi auren su Abbanta yakira sa musamman don su tattauna matsalan Saleeman, anan yake faɗa masa komi kuma yaɗaura da roƙon sa akan don Allah yariƙe masa ƴa bisa amana


Ajiyan zuciya yasauke kana yasaka zara-zaran hannun sa me yalwataccen gashi a kwance yasoma tadata, pilon yake ɗan ja ahankali yanda zata iya tashi, kasancewar bata da nauyin barci hakan yasa yana soma taɓa wa tabuɗe idanunta da sukayi ja alamun barcin yayi nisa sosai, suna haɗa idanu tayi saurin yunƙurin tashi amma yanda jikinta be da ƙarfi dole takoma takwanta tana sake rufe idanunta


"Ya jikin naki?" Yafaɗa ahankali cike da kulawa kuma har alokacin idanun sa na yawo a jikinta


Bata buɗe idanun ta ba tace "da sauƙi".


Gyaɗa kansa yayi kafin yace "ki tashi kiyi sallah".


Daga haka yajuya yafita batare da yajira me zatace ba


Sai da tatabbatar ya fita kafin tabuɗe idanun nata cike da kasala tatashi zaune tana riƙe kanta, babu ƙarfi ko kaɗan ajikin ta ga kuma kanta dake faman ciwo baya ga haka babu komi yanzu dake damun ta, waigawa tayi taɗauki wayan ta dake kan drowan Gadon taduba lokaci, zaro ido tayi tana kallon wayan cike da mamaki, batayi tunanin har tayi barci me nisa haka ba tunda har gashi ƙarfe 04:07pm.


Ajiye wayan tayi tazuro ƙafafuwan ta ƙasa tasauko, Toilet tanufa taɗauro alwala tafito tasanya Hijab ta tada sallah, azahar da la'asar tayi sannan tacire Hijabin ta'ajiye, wanka tashiga tayi don tasami ƙarfin jikin ta, tana fitowa tashirya cikin jan atamfa me ratsin baƙi da fari, ɗinkin riga da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login